Ticker

6/recent/ticker-posts

Tarihin Marigayi Alhaji Abubakar Muhammadu Kassu Zurmi

Asalinsa Bagobiri ne domin Kakansa(wanda ya haifi Mahaifinsa) da ake kira Gandau ne ya taso daga Kurawa ta Sabon Birnin Gobir ya dawo garin Dunfawa dake Masarautar Moriki ta Jihar Zamfara ta yau.

Gandau wanda ya na fawa ya na kuma Kiɗa ne ya haifi Muhammadu /Ahmadu Ganga a Dunfawa. Muhammadu Ganga ne ya tashi daga Dunfawa ya koma Magarya dake cikin Masarautar Zurmi inda ya haifi Kassu a shekarar 1910. Sunan Mahaifiyarsa Maimuna /Kande, shi ne ɗansu na farko sun kuma haifi Balarabe da Nasara duk kuwa da yake sun riga Kassu (yayansu/wansu) rasuwa.

Sunansa na yanka shi ne Abubakar ana kuma yi masa kinaya da Mai Kasuwa ko Kassu saboda an haife shi a ranar Lahadi ne, wato ranar da Kasuwar wani gari dake kusa da garinsu  da ake kira Dauran ke ci.

Ya girma a garin Kadawa inda suka koma daga baya shi da mahaifinsu da sauran iyalin daga baya kuma Mahaifin nasa ya baro shi a Kadawa ya sake dawowa Magarya. A Kadawa ne Kassu ya ci gaba da rayuwa har ya zuwa wafatinsa sanadiyar jinyar da ya yi fama da ita a shekarar 1983 yana da shekaru 73 a duniya, ya bar matan aure 4 da 'ya'ya 12, 6 Maza, 6 Mata. Wasu daga cikinsu sun rasu, waɗanda ke raye a halin yanzu sune Mal. Namakka da Mal. Rabi'u (wanda Makaho ne) da kuma Mal. Aliyu dake wa'azi a Masallacin Jumu'a na garin Kadawa kafin Limamin Masallacin ya iso.

Ya yi karatun allo amma bai yi na zamani ba. Ya soma Kiɗa da waƙa tun yana da kimanin shekaru 15 a duniya. Kiɗan noma ne ya fara dashi da Ganga kafin daga baya ya fara Kiɗan Farauta da Tauri da na Ɓarayi.

Wanda ya fara yiwa Kiɗan noma shi ne Ƙwazo ɗan Sani, Sarki Bahago ne ya fara yiwa Kiɗan farauta, Garugaru ne Ɗan Tauri na farko da ya fara yiwa Kiɗan Tauri yayin da ban samu Ɓarawon da ya fara yiwa Waƙa ta farko ba.

Bayan Kiɗa da waƙa Kassu Zurmi ya na yin noma da kiyo domin rufawa kansa asiri. Tsakanin Manoma da Mafarauta da Yan Tauri da Ɓarayi da wasu ɗaiɗaikun mutane Kassu Zurmi ya waƙe fiye da mutane 800 duk kuwa da yake ba duka bane za a samu Waƙoƙinsa naɗe a fayafayi ba.

Sanadiyar wani ɗan Tauri da aka yi a Funtua ta Jihar Katsina mai suna Alhaji Isah ne ya sadu da Alhaji Dr. Mamman Shata Katsina har ma ƙauna da soyayya ta ƙullu a tsakaninsu inda Alhaji Dr. Mamman Shata Katsina ya biya masa kujera ya tafi Kasar Saudiya ya yi aikin Hajji a shekarar 1973.

Duk da yake wasu jama'a ciki kuwa har da masana ilimin zamani da manazarta suna yi masa wani kallo na mutumen da bai kamata a karrama da irin wannan taro ba, sai ina ganin wannan ra'ayi nasu ya ci karo da na wasu jama'ar, musamman waɗanda suka yi dandazo a wannan Taro da aka yi a Jami'ar Jihar Sakkwato daga 18 zuwa 21 ga watan Afrilun 2025  ko dai domin gabatar da Muƙalunsu ko domin sauraren abubuwan da suka wakana.

Ana kiransa da Kassu Zurmi a maimakon Kassu Magarya ko Kassu Kadawa domin Zurmi ce hedikwatar Masarautar dake kula da Magarya da Kadawa. Ya gaji/gadi Kiɗa ne daga Mahaifinsa Muhammadu Ganga/Ahmadu wanda shi ma ya gada ne daga Mahaifinsa Gandau.

Da wannan nike fatar Maigirma Alhaji Dikko Bala Ƙofar Sauri, Katsina ya samu wani ɗan bayani daga cikin bayanan da yake nema akan Marigayi Alhaji Abubakar Muhammadu /Ahmadu Kassu Zurmi. Allah ya jiƙan magabatanmu ya sa mu wanye lafiya mu cika da kyau da imani, amin.

Daga alƙalamin:

Alh. Ibrahim Muhammad Ɗanmadamin Birnin Magaji, Jihar Zamfara, Nijeriya.
Alhamis, 24/04/2025.

Kassu Zurmi

Post a Comment

0 Comments