Citation: Shehu, M and Aliyu, L. (2024). Tanadin Tatsuniyoyin Hausa wajen Tabbatar da Zaman Lafiya. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 188-197. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.022.
TANADIN
TATSUNIYOYIN HAUSA WAJEN TABBATAR DA ZAMAN LAFIYA
Musa Shehu
Department of
Nigerian Languages
Usmanu Danfodiyo
University, Sokoto
Lauwali Aliyu
Department of
Hausa
Adamu Augie
College of Education, Argungu
Tsakure:
Hausawa na cewa “zaman lafiya mai
daɗi”. Tatsuniya tana
daga cikin fannonin adabi da suka game duniya baki ɗaya, saboda a kowane harshe da ke cikin faɗin duniya komai ƙanƙantarsa
da rashin yawan masu amfani da shi ana samun tatsuniya a cikinsa. (Dorson 1972
a cikin Koko 2009). Manufar wannan takarda ita ce fito da wasu tatsuniyoyin
Hausa a yi fashin baƙinsu dangane da saƙon zaman lafiya da suke ɗauke da shi. Saboda haka,
takardar ta fito da wasu ginshiƙan samar da zaman lafiya da ke cikin wasu tatsuniyoyin waɗanda suka haɗa da riƙon
amana da adalci da haƙuri da alkawali da yafiya da kuma haɗin kai don a gudu tare a tsira tare.
Fitilun Kalmomi:
Gudunmuwa, Zaman Lafiya, Tatsuniya
Gabatarwa
Tatsuniya
na daga cikin manyan sassan adabin bakan Hausawa wanda suke taƙama da su tun zamanin zamunna. Tatsuniya ta kasance
makaranta ta farko ta koyar da Hausawa tarbiyya tagari da kyakkyawar
zamantakewar rayuwar duniya. Muhimmancin tatsuniya a rayuwar Hausawa abu ne da
ya fi ƙarfin a bayyana, sai dai a faɗi
albarkacin baki a shafa fatiha a watse. Tatsuniya tana ilmantarwa wajen shiryar
da yara yanayin zaman duniya da halin rayuwa da iya zamantakewa da sanin
tarihin wasu abubuwa da rayar da halayen al’umma daga kaka zuwa tattaɓa
kunne. Haka ma, tana iya kasancewa hanyar sadar da ilimi, ma’adinin al’adu, haɓaka
al’adu, matakan tsaro, madubin rayuwa, nishaɗi,
iya siyasa, haɓaka harshe da raya shi, cusa tarbiyya ga yara da
sauransu. Dangane da sha’anin zaman lafiya da sasantawa kuwa, tatsuniya ta yi
rawar gani wajen daidaita akalar rayuwar Hausawa, domin kuwa akwai tatsuniyoyi
masu tarin yawa waɗanda ke nuni da yadda ake zama lafiya da sasantawa idan
wata matsala ta kunno kai.
Tatsuniya
na daga cikin fannonin adabi da suka game duniya baki ɗaya,
saboda a kowane harshe da ke cikin faɗin duniya
komai ƙanƙantarsa da rashin yawan masu amfani da shi ana samun
tatsuniya a cikinsa. (Dorson 1972 a cikin Koko 2009). Wannan kuwa bai rasa
nasaba da cewa, kowace al’umma ta duniya tana da nata hanyar da take aiwatar da
ilimin hikimominta waɗanda suka haɗa da ƙere-ƙere da magungunan gargajiya da sauransu. Ta ƙara da cewa, bincike ya nuna ba Hausawa kaɗai
ke yin tatsuniya ba, al’ummun duniya na kusa da na nesa suna aiwatar da ita.
Haka ma, ba abin mamaki ba ne a ce labarun da ke cikin tatsuniya suna yaɗuwa
ne daga wannan al’umma zuwa waccan, amma kuma tushensu daga wata ƙasa ce ta daban wadda idan tatsuniyar ta zo ga al’umma
sai su gyara ta ta yadda za ta dace da al’adunsu, sai ta zama tasu.
Ma’anar
Tatsuniya
Masana da manazarta sun faɗi
albarkacin bakinsu gwargwadon fahimtarsu. Yahaya (1971) yana cewa: “Tatsuniya
wani ƙagaggen labari ne da al’adar Hausawa ta tanada domin
nishaɗantarwa da kuma cusa tarbiyya ga ‘ya’yan Hausawa.” Calvin
(1984) a cikin Salihu (2009) “Tatsuniya abu ce a tsarin al’adun Hausawa inda
tsohuwa ce kan tara jikokinta ko yaran gida da dare ta riƙa yi musu
tatsuniya.” Shi kuma Zaruk (1987) cewa ya yi: “Tatsuniya ƙagaggen
labari ne da aka shirya game da gizo ko waninsa da ya ƙunshi wani
darasi ko ya cimma wata manufa ta musamman cikin hikima”. Ita kuwa Hadiza
(2009) tana da ra’ayin cewa: “Tatsuniya wasu labarai ne da mutane ke ƙirƙirowa cikin azanci don su tarbiyyantar
da ‘ya’yansu da kuma cimma wasu buƙatoci dangane da al’umma.” A tunanina kuwa, tatsuniya
wani ƙirƙirarren labari ne da ake yi wa yara don
karantar da su rayuwar duniya mai alfanu, da kauce wa marasa alfanu.
Dabarun
Tabbatar da Zaman Lafiya a Tatsuniyoyin Hausa
Koko (2009) ta kawo jerin jigogi fiye da ashirin, wanda
suka haɗa da girmama manya da mutunta su, da adalci da jaruntaka
da tausayi da tawakkali da amana da haƙuri da
juriya da zamantakewa da soyayya da tarihi da dabarun fitar da kai da kwaɗayi da
illolinsa da sakamakon zamba da yaudara da wa’azi da ilimi da tsoratarwa da
sana’o’in gargajiya da sakamakon cin amana da sakamakon mugunta da zalunci da
sauransu. Idan aka yi nazarin waɗannan jigogi da ƙwaƙwalwar hankali da idanun basira za a ga cewa, wasu da
dama daga cikin jigogin da aka ambata, matakai ne na wanzar da zaman lafiya
musamman jigogi irin su amana da adalci da haƙuri da
sana’o’i, da kuma tsare dokokin al’umma. A kan haka, za a kalli yadda wasu
tatsuniyoyin Hausa ke koyar da zaman
lafiya da kuma sasanta rikice-rikice idan sun kunno kai. Daga cikin dabarun
samar da zaman lafiya da za a iya tsinta a tatsuniyoyin na Hausa sun haɗa da.
Riƙon Amana
Kamar yadda aka bayyana a baya, riƙon amana
na daga cikin ginshiƙan wanzar da zaman lafiyar al’umma,
kamar yadda rashinsa a tsakanin al’umma ke haifar da rikice-rikice da
tashe-tashen hankula masu hana zaman lafiya. Idan aka dubi yanayin da ake ciki
na rashin zaman lafiya a ƙasar nan a yau, za a ga yana da nasaba
da rashin amanar shugabanni da ɗaiɗaikun mutane. An danƙa wa
shugabanni dukiyar talakawa domin kyautata rayuwarsu, da samar musu abubuwan
more rayuwa, amma sun danne, sun bar su cikin talauci, babu aikin yi, ba a kula
da lafiyarsu, an kasa samar musu hanyoyin sufuri masu kyau, ga rashin wutar
lantarki da ruwa masu tsafta, ga su nan dai. Irin Wannan yanayi da aka jefa
talakawa ya taimaka wajen wanzuwar ayyukan ta’addanci da ya hana al’ummarmu
zaman lafiya a yau.
Za a iya kallon rawar da riƙon amana
ya taka wajen wanzar da zaman lafiya a tatsuniyar “Abotar Zaki da Mutum” da aka
kawo cikin littafin Taskar Tatsuniyoyi na Bukar
Usman, wadda aka nuna an yi abota tsakanin ɗan zaki da
ɗan mutum,
kuma ɗan zaki ya riƙe amana ya
ƙi gaya wa uwarsa cewa akwai ɗan Adam
tare da su, domin yin hakan tamkar cin amana ne da zai iya haddasa rashin zaman
lafiya a rayuwarsu. Ga yadda tatsuniyar take:
Tatsuniyar Abotar Zaki Da Mutum
Wani maharbi ne ne kullum yakan tafi daji
yawon harbi, idan ya harbo naman daji sai ya kawo gida. Ana nan, sai wata rana
ya tafi daji yawon farauta bai samo komai ba har kusan faɗuwar rana,
sai ya ga fara ya kama ya kai gida. Da isowarsa sai matarsa ta yi masa maraba
ta kawo ruwa ya sha, sai ta ɗauki burgamensa tana buɗewa sai fara ta tashi sama ta gudu. Sai maharbi ya ce wa
matarsa, “Kash! Abin da na samo ke nan tun safe, bi ta ki kamo ta duk inda ta
kai, in ba haka ba mu kwana da yunwa.” Matar maharbin nan kuwa tana da ciki ta
kusa haihuwa, sai ta tashi da ƙyar ta bi
fara. Tana cikin bin fara sai naƙuda ya
kama ta, sai ta ga wata ƙatuwar
kuka mai kogo ta shiga gefe ɗaya sai ta haifi ɗa namiji, gefe ɗaya kuma ashe wata zakanya ke ciki ta haihu. Wata rana
zakanya ta fita kiwo, ita ma matar nan ta fita neman abinci, sai ‘ya’yansu (ɗan matar
nan da ɗan zakanya) suka fito bakin kogo shan iska suka ga juna
Allah ya haɗa so tsakaninsu, suka ƙulla abota
cikin aminci ba tare da ɗan zakanya ya tona masa asiri wajen zakanya ba. Ɗan zakanya a kullum yana yi wa ɗan matar
nan kashedi da cewa, “kada ya kuskura uwarsa zakanya ta gan shi saboda za ta
iya kashe shi.” Rannan sai zakanya ta fito ba tare da ɗanta ba,
sai ta ci karo da matar nan sai ta bangaje ta ta faɗi ta mutu,
ta ɗauko ta kawo bakin kogo ta aje sharab! Ko da ɗan zakanya
ya gano cewa gawar uwar abokinsa ce, sai ya ce “ba zan ci wannan naman ba, na
daina cin naman mutum. Ana nan, ranar sai ɗan zakanya ya ce wa uwarsa, “Inna bari in nuna miki na
iya bangazar namun daji ki gani.” Sai uwar ta ce “to gwada mu gani in ka iya.”
Sai ɗan zakanya ya ja da baya ya ba uwarsa karab, sai ta faɗi ta mutu.
Sai ya ja ta ya kai wa abokinsa ya gani. Abokinsa ya tambaye shi yaya aka yi
haka? Sai ɗan zakanya ya ce “Ni na kashe ta, yanzu mun zama daidai,
za mu ci gaba da zaman duniya lafiya lau ba tare da wata fargaba ba, kuma Allah
zai taimake mu da abin da za mu ci mu sha.” ...Haka suka ci gaba da rayuwa har
lokacin da ƙaddara ta sami ɗan zakanya sarkin baka ya harbe shi da kibiya rai ya yi
halisa.
Wannan ya nuna riƙon amana
wani sinadarin wanzar da zaman lafiya ne, domin da tun farko ɗan zaki ya
ci amanar ɗan matar nan ya faɗa wa zakanya halin da ake ciki, da zamansu ya yamutse.
Haka ma, da bai yi adalcin kashe uwarsa zakanya ba, da ba su sami zaman lafiya
mai ɗorewa ba.
Don haka, da shugabanninmu na yau za su riƙi amanar
talakawansu, su rufa musu asiri ta hanyar kyautata rayuwarsu, su samar musu
maslaha a kan matsalolinsu, da ƙasar nan an zauna cikin ƙoshin lafiya, sai ɗan abin da ba a rasa ba. Har wa yau, wasu rikice-rikicen
aure da suke faruwa tsakanin ma’aurata, suna da nasaba da cin amanar
zamantakewa, ko dai ta gefen miji, ko ta gefen mace.
Bugu da ƙari, akwai wata tatsuniyar “Rimi da
‘yar Amana” a cikin littafin Taskar
Tatuniya na Bukar Usman, wadda ke koyar da amfanin riƙon amana a
rayuwar mutane. A tatsuniyar an nuna cewa, wata marainiya ce da ba uwa ba uba,
amma kafin rasuwar iyayenta sai suka danƙa ta amana
ga wani iccen Rimi wanda ya riƙa kula da ita har ta girma kyawonta ya
fito sosai. Wata rana Gizo ya gan ta sai ya sheƙa ya gaya
wa sarki, sai sarki ya turo fadawa don a kai masa ita. Da aka zo kama ta sai ta
maƙale wa Rimi tana neman agajinsa. Daga nan sarki ya sa a
sare itacen Rimin, amma aka kasaa saboda amanar yarinyar da ya riƙe. Ga labarin tatsuniyar kamar yadda aka kawo ta:
Tatsuniyar Rimi da ‘Yar Amana
An yi wani gari mai yawan jama’a da Sarkinsu
mutumin kirki. Akwai wani mutum mazaunin wannan gari shi da matarsa da ‘yarsu ɗaya. Wata
rana ciwon ajali ya kama matar wannan mutum. Kafin ta rasu sai ta kira shi ta
ce: “Maigida, ni fa ina jin ba zan tashi daga ciwon nan ba, amma ga amanar
‘yarmu nan ka kula da ita sosai, kada ka bari wani mugun abu ya same ta. Da
matar ta rasu sai uban yarinyar ya ci gaba da renon ‘yarsa har ta yi wayo. Sai
wata rana shi ma ciwon ajali ya kama shi, sai ya rasa yadda zai yi da ‘yarsa,
kuma ba shi da kowa a garin. To amma akwai wata tsohuwar bishiyar Rimi a ƙofar gidansa, sai ya fito ya ɗauko
yarinyar ya kawo ta gindin Rimin, sai ya dubi Rimin nan ya ce ya ba shi amanar
‘yarsa domin yana jin wa’adinsa ya kusa cika. Daga nan ya koma gida bai sake
fitowa ba har ya rasu. Bayan rasuwarsa da ‘yan kwanaki, duk sanda yarinyar ta
ji yunwa sai ta je wurin Rimin nan ta kama waƙa tana
cewa: “Rimi, Rimi uwata, Rimi ubana ya ba ka amanar Allah, uwata ta ba ka
amanar Allah.” Da ta yi wannan waƙa sai Rimi
ya ba ta abin da take so. Wata rana Gizo ya fita yawo sai ya ga ‘yar budurwa
tana wanki a gindin Rimi, to da ma sunanta Jummai. Da Gizo ya ga kyaunta sai ya
garzaya gidan Sarki ya kwashe labarin yarinyar nan ya gaya masa. Da Sarki ya ji
haka, sai ya tura fadawansa su ɗauko yarinyar. Da suka isa wurin Rimi sai yarinyar ta gan
su ta kuma razana, sai ta je ta rungumi Rimi ta fara waƙa tana neman agajinsa. Sai ya ce mata, yi wankinki, cikin
ɗari da goma, ɗaya ya koma. Da dogarai suka matsa kusa da ita sai duk
suka mutu. Da Sarki ya ji labari sai ya sa a je a sare wannan Rimi. Da aka taru
za a sare, idan aka sara jikin sai ya ƙara
tohowa, har dai masu saran suka gaji suka haƙura. Har
yanzu wannan Rimi da ya riƙe amana
yana can a garin, mutane suna zuwa kallonsa.
Wannan ya nuna cewa, riƙon amana
babban makami ne na zaman lafiya, domin yana kariya ga duk wata musibar da ka
iya yi wa rayuwa barazana ga zaman lafiyarta.
Adalci
Wanzuwar adalci a cikin al’umma yana haifar da zaman
lafiya da ƙaunar juna mai ɗorewa, kamar yadda rashin adalci ke jawo rikici da
haddasa gaba a cikin al’umma. Akwai wata tatsuniya da aka kawo a cikin littafin
Jagoran Nazarin Tatsuniya na Hadiza
Salihu Koko, ta wani yaro mai suna “Daredi” wadda ke nuni da illolin da rashin
adalci ke haifarwa na haddasa fitina da ruɗani, da
kuma yadda za a sasanta domin a zauna lafiya.
Ga dai labarin tatsuniyar kamar yadda yake:
Tatsuniyar Daredi
A wani
gari da ake kira Tunga, an yi wata yarinya mai kyau wadda ba ta son kowa duk
garin sai wani yaro da ake kira Daredi. To su kuwa iyayen yarinyar nan suka yi
tsayin daka suka ce ba su ba shi ita aure. Yarinya ta yi ta yi da su suka ƙiya. Sai rannan wata shawara ta zo mata, sai ta tafi ta
kwashe duk ruwan da ke cikin rijiyoyi da gulaben garin, ta haye saman itace ta
yi zamanta. Da mutanen gari suka matsu babu ruwan sha, sai aka roƙi iyayen yarinyar nan da su je su roƙe ta ta sako ruwa a samu a sha. Sai uwarta ta fara zuwa
tana rera waƙa tana roƙon ta,
amma ta ƙiya. Sai uwar ta faɗi ta mutu. Daga nan sai ubanta ya zo ya roƙe ta, amma ta ƙiya, shi
ma sai ya faɗi ya mutu. Haka dai ‘yan’uwanta suka yi ta zuwa suna roƙon ta tana ƙiyawa, sai
su faɗi su mutu. Kai har dai duk zuriyarsu ta ƙare. Sai mai gari ya zo da kansa yana rera waƙa yana roƙon ta. Sai
nan take ya sa aka biɗo Daredi saboda lokacin da iyayen yarinyar suka hana masa
ita sai ya bar gari don baƙin ciki.
Daga nan sai Daredi ya fara rera waƙa yana roƙonta ta ba shi ruwa ya sha. Sai yarinyar ta sauko daga
saman itaciya ta mayar musu da ruwa kowa ya sha. Sai mai gari ya sa aka ɗaura musu
aure suka yi zamansu.
Wannan tatsuniya tana nuni da illar da rashin adalci ke
haifarwa a rayuwar mutane, da kuma irin rawar da sarakuna za su iya takawa
wajen sasanta rikici domin maido da zaman lafiya a tsakanin al’umma. Haka ma,
tatsuniyar na hannunka mai sanda ga iyayen da ke tilasta wa ‘ya’yansu mata
auren dole, alhali suna da masoya na gaskiya waɗanda aka
tabbatar da ba su da wata illa da za ta hana a ba su aure. Wannan matsala a yau
tana daga cikin rikice-rikicen da ake fama da su a ƙasar Hausa
wadda ta sha haifar da masifu iri daban-daban, har ma da rasa rayukan waɗanda abin
ya shafa da ma waɗanda bai shafa ba. Bugu da ƙari,
rashin adalcin da ake fuskanta a wajen mahunkunta, babu mai gaskiya sai mai
abin hannunsa ko mai uwa a bakin murhu, ko a ware wasu mutane, hukunci bai hawa
kansu sai marasa gata, yana taimakawa wajen ƙara
haddasa wasu rikice-rikice da suke yawan aukuwa.
Akwai wata tatsuniya a cikin Taskar Tatsuniyoyi na Bukar
Usman da ta yi ƙoƙarin
bayyana adalcin shugabanni a matsayin sinadarin wanzar da zaman lafiya. Wasu
tsuntsaye ne biyu, wato “Talipaku da Kurciya” suka haɗa kansu
suna tafiyar da lamurransu lami lafiya. Daga bisani Talipaku ta shirya yaudara ta sace ‘yar
Kurciya ta gudu. Daga ƙarshe rikicin ya kai ga sarkin
tsuntsaye wanda ya sasanta rikicin bisa adalci. Ga cikakken bayanin tatsuniyar:
Tatsuniyar Talipaku da Kurciya
Wata rana tsuntsuwa Talipaku da Kurciya suka
yi sheƙa a bishiya ɗaya. Da lokacin saka ƙwan da
suka ɗauka ya zo, sai suka haɗa ƙwansu a
wuri ɗaya. Bayan sun gama kwanci, sai suka ƙyanƙyashe suka
sami ‘ya’yansu guda biyu. Suna nan a haka, kullum sai su fita neman abincin
‘yan tsakinsu. Kansu ya haɗu komai na tafiya rumui-rumui. To ashe ita Talipaku ba ta
jin daɗi da bakin ‘yarta ya yi tsawo fiye da na ‘yar Kurciya
wadda kyakkyawar gaske ce. Duk lokacin da za su fita neman abincin ‘ya’yansu,
sai a karɓi renon ‘yar Kurciya, amma a bar ‘yar Talipaku a sama
cikin sheƙa. Wata rana Talipaku ta yanke shawarar sace ‘yar Kurciya
ta gudu da ita. Wata rana suna wurin neman abinci, sai Talipaku ta sulale ta je
ta sace ‘yar Kurciya ta gudu da ita. Ko da Kurciya ta dawo gida ta shiga sheƙa, sai ta ga ba ‘yarta, sai ‘yar Talipaku. Sai ta fita ta
kama cigiya. Sai aka ce mata ai an ga Talipaku ta ɗauki ‘yar
Kurciya sun yi sama. Da jin haka sai Kurciya ta koma sheƙarsu ta ɗauki ‘yar Talipaku ta fito ta kama waƙa tana neman Talipaku. Ita kuwa Talipaku tuni har ta isa
garin Sarkin tsuntsaye aka kai ta gidan Sarkin tsuntsaye mai suna Miki. Da ta
je gaban Sarkin sai ya tambaye ta abin da ke tafe da ita. Sai ta ce ta zo ne
ita da ‘yarta a ba su wuri a garin domin su zauna. Da Miki ya ji haka sai ya
ce: “To ai ‘yar da kika zo da ita ba ta yi kama da ke ba, ba ‘yarki ba ce. Ina
kika samo ta?” Ita kuwa Kurciya tuni ta haɗu da wasu mutane a jeji ta tambaye su ko sun ga Talipaku?
Sai suka ce mata yanzu ta tambaye su hanyar gidan Sarkin tsuntsaye. Sai suka
nuna wa Kurciya hanyar, suka ce ta yi sauri ko ta same ta a gidan Sarkin
tsuntsaye. Tana zuwa gidan, sai ta tarar ana tambayar Talipaku inda ta samo
‘yar da ba ita ta haifa ba. Sai ta faɗi ta yi gaisuwa, sai ta yi wa Sarki bayani yadda suka yi
da Talipaku. Sai Sarkin ya sa aka ƙwace ‘yar
Kurciya daga hannun Talipaku a ba Kurciya, ita kuma Talipaku aka ba ta ‘yarta.
Sarkin tsuntsaye ya ja kunnen Talipaku da kada ta sake satar ‘yar wani tsuntsu.
Idan aka sake kawo ƙarar ta,
to za a kashe ta. Sai aka sallame su, Kurciya ta ɗauki
‘yarta ta yi godiya ta tafi. Ita kuma Talipaku ta tafi da ‘yarta.
Wannan tatsuniya na koyar da mu cewa, samun shugaba
nagari mai adalci tsakanin al’ummarsa wani mataki ne na zaman lafiyar al’umma.
Da ƙasarmu za ta sami irin wannan managarcin shugabanci a
yau, ba shakka da rikice-rikicen da ke addabarta sun ƙaranta.
{asarmu a yau ta zama babu mai gaskiya sai mai abin hannunsa, ko mai uwa a
bakin murhu, ko kuma wanda ake ɗasawa da shi. Don haka, da za a kawar da wannan mummunar ɗabi’a, a ɗauki ɗabi’ar
Sarkin tsuntsaye, da kakarmu ta yanke saƙa.
Alƙawali
Ba shakka, alƙawali wani
babban jigo ne da ke taimakawa ga wanzar da zaman lafiya a cikin al’umma.
Rashin cika alkawali abu ne da addini da al’ada suka yi tir da shi, kuma yana
da tasa gudunmuwa wajen haifar da rikici da hana zaman lafiya. Akwai tatsuniyar
wani mahaukaci wai shi Zarumi a cikin
littafin Jagoran Nazarin Tatsuniya na
Hadiza Koko. Zarumi mahaukaci ne mai tarin suma da kwarkwata a cikinta. Wata
rana Zarumi yana son fita neman abinci amma ya rasa mai tsare masa shukarsa
(wake). Sai kwarkwatar da ke cikin sumansa ta ce, ta yi alkawalin tsare masa
wakensa amana har ya dawo gida. Sakamakon haka, danƙon zumunci
ya ƙaru tsakanin Zarumi da kwarkwata, ya kuma yi sanadin
fitar kwarkwatar daga ƙangin suman Zarumi zuwa cikin kwalban
zinari. Ga abin da tatsuniyar ke cewa:
Tatsuniyar Zarumi
An yi wani mahaukaci da ake kira Zarumi.
Zarumi bai zagin kowa balle bugu, sai dai yana da tarin suma mai kwarkwata a
ciki. Wata rana yana kwance cikin bola sai ya ga wani wake ja mai kyau, sai ya ɗauka ya je
gida ya shuka. A hankali wake ya girma ya yi ‘ya’ya sosai. Rannan Zarumi na son
ya fita neman abinci sai ya rasa mai fake masa waken nan. Can daga cikin
sumansa sai ji ana cewa “ni zan tsare maka gidan.” Ko da Zarumi ya duba sai ya
ga ashe kwarkwatar da ke kansa ce ke magana. Sai Zarumi ya ciro ta daga sumansa
ya ce “to na ba ki amanar gidana.” Sai kwarkwata ta ce “na yi alkawalin tsare
maka, Allah ya dawo da kai lafiya.” Bayan fitar Zarumi, Gizo ya shigo bara. Da
ya ji kamar ba kowa gidan sai ya ce, bari in ɗan ɗibi waken nan in je gida in dafa jinɓiri. Ko da
Gizo ya taɓa wake sai kwarkwatar nan ta fara rera waƙa tana ce wa Gizo kar ya taɓa, waken
Zarumi ne. Sai ya tsaya bai ga kowa ba. Ya kuma ƙara taɓawa ya ji
an yi waƙa kuma bai ga kowa ba, sai ya fara rawa. Da Gizo ya ga
haka, sai ya garzaya gidan sarki ya gaya masa ya tafi wani gida bara ya ga wake
mai kyau, ko da ya sa hannu ya ɗiba sai ya ji waken na waƙa mai daɗi. Da
sarki ya ji wannan bayani, sai ya aika fadawansa su je su ɗebo masa
wannan wake. Ko da suka sa hannu su ɗiba sai suka ji ana waƙa sai suka
kama rawa har rana ta faɗi. Ko da sarki ya ga ba su dawo ba sai rana ya ɓaci ya hau
doki da kansa domin ya je ya ga abin da suke yi. Da zuwansa ya kama yi musu faɗa ya sauko
ya sa hannu zai ɗebi wake sai wake ya kama waƙa. Sai sarki ya kama rawa tare da fadawansa da Gizo har
Zarumi ya dawo ya iske gida ya cika da mutane har da sarki. Ko da ya tambaya
aka ce masa wakensa ke waƙa mai daɗi. Sai
Zarumi ya ce, ba wake ke waƙa ba,
kwarkwata ce. Daga nan sarki ya ce yana son ya sayi kwarkwatar, sai ya ba
Zarumi bawa goma da dinari dubu, Zarumi ya ba shi kwarkwatar, ya ce maaa
abincinta shi ne man shanu. Sarki ya yi godiya ya koma gida ya sa kwarkwata
cikin kwalbar zinari da auduga da man shanu ya rufe ya rataye a kan gadonsa.
Duk lokacin da ransa ya ɓaci sai ya zo ya taɓa kwalbar nan sai kwarkwata ta fara yi masa waƙa har sai ransa ya yi sanyi.
Wannan tatsuniya tana karantar da mu cewa, riƙon amana da cika alkawali sinadarai ne na samar da ci
gaba da wanzar da zaman lafiya a rayuwar al’umma, musamman idan aka yi la’akari
da yadda Zarumi ya saka wa kwarkwata da alheri, daƙon zumunci
ya ƙara ƙarfi tsakaninsa da kwarkwata har zuwa
lokacin da suka rabu lami lafiya. .
Yafewa
Yafe wa juna a kan wani saɓani da ya
gudana tsakanin mutane, wani babban mataki ne na wanzar da zaman lafiya
tsakanin mutane. Sau da yawa wasu rikice-rikice suke faruwa a sanadiyyar ɗaukar
fansa musamman a rikice-rikice masu alaƙa da
addini ko ƙabilanci ko siyasa, wanda galibi yakan haddasa gaba mai ɗorewa
tsakanin al’umma. Akwai wata tatsuniyar kishiyoyi biyu da aka kawo a cikin
littafin Taskar Tatsuniyoyi na Bukar
Usman, suna zaman lafiya ba su taɓa ɓata wa juna rai ba. Suna cikin irin wannan zama, sai ɗaya ta
kwanta jinya har Allah ya ɗauki ranta, sai dai kafin ta rasu ta bar wa kishiyarta
amanar ɗiyarta. Bayan rasuwar kishiyar, sai kishiyar ɗaya ta riƙe amanar marainiyar kamar yadda ta riƙe ɗiyarta na cikinta, kafin daga bisani wata tsohuwa ta zo
ta hure mata kunne, sai ta fara azabtar da marainiyar har ta kore ta daga gidan
ta shiga duniya. Da man Hausawa na cewa: “Mahaƙurci
mawadaci.” Wannan kora da aka yi mata sai ya zamo mata alheri, domin a kan haka
ne ta haɗu da ɗan sarki ya aure ta suka ci gaba da rayuwa mai daɗi. To sai
dai kuma, duk da irin cin zarafin da kishiyar uwarta ta yi mata bai sa ta manta
da ita ba, ko kuma ta ƙudurci aniyar ɗaukar
fansa tun da ta samu dama. Amaimakon haka, sai ta shirya tare da mijinta suka tafi suka gan ta, suka yi mata goma na
arziki tare da yafe mata. Ga labarin tatsuniyar kamar yadda take:
Tatsuniyar Kishiyoyi Biyu
An yi wasu kishiyoyi biyu masu zaman lafiya,
ba su taɓa ɓata wa juna rai ba. Sai wata rana ɗaya daga
cikinsu ta kwanta jinya. To da ma kowacensu tana da ‘ya mace, kuma sun yi kama
da juna ainun, yadda ba kowa ne zai iya bambance su ba. Da mai jinyar nan ta ga
alamun ciwon nata ba na tashi ba ne, sai ta kira kishiyarta, ta ba ta amanar
‘yarta. Kishiyar ta karɓa, kuma ta yi alkawali za ta kula da duk yaran biyu kamar
ita ta haife su. Da mai jinyar ta rasu, sai kishiyar ta ci gaba da kula da
yaran har suka girma suka zama ‘yan mata. Rannan sai wata tsohuwa ta ziyarce
su, da ta lura da yanayin matar ta hanyar adalcin da take nunawa a tsakanin
yaran, sai riƙa yi mata faɗa a kan yaya za ta riƙi ‘yar
wata kamar nata. Sannu a hankali har ta fara karkata ga zancen tsohuwa. Daga
nan fa sai ta fara gana wa ‘yar kishiyar nan tata azaba iri-iri, har ya kai in
za su ci abinci sai ta ƙi zuba wa
‘yar kishiyar abincinta a akushi, sai ta zuba mata a ƙasa. Ana nan a haka, sai ta daina ba ta abinci sam-sam,
har ma dai ta kore ta daga gidan, wai ta je can ƙabarin
uwarta ta karɓi abinci. Da yarinya ta ji haka, sai ta yi ta kuka, ta
kama hanya ta tafi bakin ƙabarin
uwarta tana kuka. Wata rana da ta je ƙabarin
uwar tana kuka, sai uwar ta fito ta rarrashe ta, ta ba ta abinci, ta ci ta ƙoshi. Kullum haka nan yarinyar take yi idan aka hana ta
abinci. Nan da nan ta sake yin ƙiba ta yi
kyau, abin gwanin ban sha’awa. Wata rana sai wasu samari suka je tambayar uwar
cewa, ɗaya daga cikinsu yana son ya shiga neman auren
marainiyar. Sai ta ce, sai dai su auri ‘yarta. Da marainiyar nan ta ga haka,
sai ta gudu, ta shiga uwa duniya. Tana cikin tafiya sai ta ga hadari ya haɗu, sai ta
hangi ‘yar bukka sai ta shiga. Bayan ta zauna sai ta ga wani babban kumurci a
gefenta. Macijin nan ya riƙa rikiɗa yana
komawa abubuwa masu ban tsoro, amma bai sa yarinyar ta razana ba. Daga ƙarshe ya rikiɗa ya koma yaro matashi kyakkyawa. Yarinyar ba ta sani ba
ashe macijin nan ɗan Sarki ne yake neman aure, amma sai ya bi wannan hanya
don ya sami mace mai hankali da amana. Nan da nan ya sa aka ɗauke ta a
kan doki aka kai ta gidan Sarki aka ɗaura mata aure da shi aka sha biki. Wata rana sai amarya
ta kwanta ɗaki ita kaɗai tana rusar kuka. Da mijin ya shigo ya tambaye ta abin
da ya faru, sai ta ce tana tunanin gidansu ne da mahaifinta da kuma kishiyar
mahaifiyarta wadda ta riƙe ta. Ta
kwashe labarin gaba ɗaya ta gaya masa. Da ya ji bayaninta, ba tare da ɓata lokaci
ba, sai ya ce ta shirya su je su kai musu ziyara. Da suka isa garin, sai suka
zarce gidan iyayenta suka shiga gidan. Da ‘yar’uwarta ta gan ta sai ta rungume
ta, amma kishiyar uwarta da ƙyar ta
gane ta saboda tsagun fuska da ta yi mata. Bayan amarya ta huta, sai ta kwashe
labari tun daga fitarta gida zuwa lokacin da ta auri ɗan Sarki.
Da ta gama ganin dangi ta yi wa kowa alheri, sai ita da mijinta suka yi musu
sallama suka kama hanyar garinsu...
Wannan yana koyar da mu yafiya a lokacin da aka zalunce
ka bisa kuskure ko da gangan, saboda yin
hakan zai dawo da zaman lafiya da ƙaunar juna mai ɗorewa.
Haka ma, tatsuniyar na nuni da yin taka-tsan-tsan da wasu mutane da ka iya kawo
tashin-tashina a cikin al’umma.
Har wa yau, akwai tatsuniyar wasu abokai biyu, “Nasiru da
Nisiru” a cikin Taskar Tatsuniyoyi na Bukar
Usman, wadda ke ɗauke da jigon yafiya a matsayin hanyar zaman lafiya da
sasantawa. Tatsuniyar ta nuna cewa, mahaifiyar Nasiru suna zaune lafiya da
kishiyarta ba a taɓa raba su ba.
Rasuwar uwar Nasiru ke da wuya
sai kishiyarta ta shiga azabtar da Nasiru da ma ƙoƙarin halaka shi, sai dai ɗan
kishiyar uwar Nasiru mai suna Aliyu yana son Nasiru sosai. Wannan ya tilasta
Nasiru barin gari tare da abokinsa Nisiru, suka koma wani gari da zama, inda
aka nuna Allah ya azirta su sosai. Bayan sun yi arziki, sai suka yanke shawarar
zuwa ganin gida, suka tarar da kishiyar uwar Nasiru cikin mawuyacin hali na
talauci da tsufa. Nan take Nasiru ya ba ta dukiya mai tarin yawa, ya kuma kawo
jari mai kauri ya ba ɗanta Aliyu. Tun daga wannan lokaci duk sa’ad da uwar Aliyu ta zauna sai ta shiga
tunanin ƙetar da ta shirya wa Nasiru da kuma irin alherin da ya
saka mata da shi, sai ta yi da-na-sani ta roƙi
gafararsa, ya yafe mata. Ga labarin tatsuniyar kamar yadda take:
Tatsuniyar Nasiru da Nisiru
A can ƙasar Mazarƙwaila, an yi wani yaro ɗan Sarkin Zaƙi mai suna
Nasiru. Yana da wani aboki wai shi Nisiru. A na nan sai mahaifiyar Nasiru ta
rasu. Rasuwarta ke da wuya sai kishiyarta ta shiga ba Nasiru wuya. To amma ɗan
kishiyar uwar mai suna Aliyu yana son Nasiru sosai, ba ya nuna masa ƙiyayya ko kaɗan. Wata rana sai Aliyu ya ce wa Nasiru da abokinsa: “Yau
zan raka ku shan zuma.” Lokacin da Nasiru da Aliyu suka ji wannan maganar, ashe
wata mata magulmaciya ta ji su, sai ta je ta ce wa uwar Aliyu: “Kin ga Nasiru
da abokinsa Nisiru za su ja ɗanki daji su halaka shi.” Uwar nan na jin haka, sai ta
nemi shawarar ‘yar zugar nan, sai ta ce: “Akwai wani boka wanda za mu je ya ba
mu maganin da za mu kashe Nasiru kawai mu huta.” Uwar Aliyu na jin wannan
gurguwar shawarar, sai ta ce: “To Shi ke nan mu je.” Da zuwansu wurin boka sai
ya ba su magani ya ce su zuba a nono su ba Nasiru ya sha. Ya ce idan ya sha,
nan take zai mutu. Da ta ba Nasiru sai ya koma can waje ya ba ɗan akuya
ya sha, nan take ya faɗi ya mutu. Daga nan sai Nasiru ya faɗi yana
shure-shure kamar da gaske. Da kishiyar nan ta ga haka, sai ta shiga murna, ta ɗauki
Nasiru ta kai shi bayan gari ta jefar. Bayan ta wuce sai Nasiru ya tashi ya
nemi abokinsa Nisiru suka yanke shawarar barin garin don gudun mugun halin uwan
Aliyu. Daga nan suka koma wani gari mai babbar kasuwa da karkara mai dausayi,
ga filayen noma nan sai an zaɓa. Da yake su duka muzakkarai ne, sai suka shiga neman
abin kansu. Kafin shekara ta dawo kowanensu ya mallaki dukiyar da an jima ba a
ga masu kamarta ba. Wata rana bayan shekara biya, Nasiru da abokinsa suka yanke
shawarar zuwa ganin gida. Nan da nan kuwa suka yi laftun dukiya suka ɗora wa raƙuma, suka tafi da ita garinsu. Nasiru ya tarar da uwar
Aliyu tana cikin mummunar talauci, sai ta yi da-na-sani ta roƙi gafararsa, ya yafe mata, ga tsufa ya kama ta, ƙanensa Aliyu kuwa ba ya komai sai baranta a gidan wani
tajiri. Nan take Nasiru ya ba ta dukiya mai tarin yawa. Ta shiga cin daɗi, ba da
daɗewa ba ta murmure. Ya kawo jari mai kauri ya ba ƙanensa Aliyu. Shi da abokinsa kuma suka shirya suka koma
wurin sana’arsu. Ta roƙi
gafararsa, ya yafe mata.
Wannan yana koyar da mu sha’anin sasantawa domin zaman
lafiya, domin a maimakon Nasiru ya ƙuduri
aniyar ɗaukar fansar azabar da kishiyar uwarsa ta yi masa a
lokacin da ya sami damar yin hakan, sai ya yafe mata, ya kuma ba ta kyauta. Yin
hakan shi zai kawar da duk wani zogin zuci da tashin-tashina, da samun zaman
lafiya mai ɗorewa tsakaninsu. Haka ya kamata mutane su kasance masu
yafe wa junansu ga duk wani saɓani da ya auku tsakaninsu, ba mutum ya ƙudurci ramawa ko ɗaukar fansa idan ya samu dama ba.
Bugu da ƙari, akwai tatsuniyar “Yelwa da Tsohuwa
da Sarki” da ke cikin littafin Taskar
Tatsuniyoyi na Bukar Usman, wadda ke bayyana yafiya a matsayin matakin
wanzar da zaman lafiya da sasantawa. Tatsuniyar ta nuna cewa, akwai wata
yarinya mai suna Yelwa tana da ƙawaye da yawa. Wata rana Sarkin garinsu
ya umurci ‘yan matan garin da su tafi kogi su kamo kifi kowa ya yi masa miya,
kuma duk wadda miyarta ta fi daɗi ita zai aura. Da ma sauran ‘yan matan sun tsani Yelwa,
da suka tafi kogi sai suka jefa ta ruwa suka kama nasu kifi suka koma gida.
Tana cikin wannan yanayi sai Allah ya kawo wata Tsohuwa sai ta tsamo ta. A taƙaice dai Tsohuwar nan ta ba Yelwa kifi ta je ta dafa ta
kai wa Sarki, sai ga shi miyarta ta fi ta sauran ‘yan matan nan daɗi, sai Sarki ya aure ta, duk da cewa ba ta da iyaye duk
sun rasu. Daga nan ƙawayen nan nata suka ji kunyar abin da
suka yi mata suka nemi gafararta, Yelwa kuma ta yafe musu. Ga cikakken labarin
tatsuniyar kamar yadda take:
Tatsuniyar Yelwa da Tsohuwa da Sarki
An yi wata yarinya mai suna Yelwa, mai ƙawaye da yawa. Wata rana Sarkin garinsu ya umurci ‘yan
matan nan su je rafi su kamo kifi bisa sharaɗin cewa duk wadda ta kamo ta yi masa miya mai daɗi, ita zai
aura. Da ma sauran ‘yan matan sun tsani Yelwa, saboda haka, bayan sun kamo kifi
sai suka haɗa baki suka jefa ta cikin kogin ta nutse. Sai ta yi sa’a
wata tsohuwa ta zo ta tsamo ta. Wannan tsohuwa kuwa tana da baiwa, sai Yelwa ta
kwashe labarin duk abin da ya faru ta gaya mata. Tsohuwar nan ta ji tausayin
Yelwa, nan da nan ta kama wani ƙaramin
kifi ta ba ta, kuma ta ba ta wata ‘yar tukunya ta ce mata ta sa wannan kifi a
cikin tukunyar ta rufe ta kiwata shi. Washe gari da Yelwa ta buɗe tukunyar
sai ta ga wani babban kifi a ciki. Ta yi mamakin yadda kifin ya girma haka. Ta
kama kifin ta dafa, ta ɗauka ta nufi fada. Kafin ta je an soma biki har an rufe ƙofa. Ta roƙi dogarai
suka buɗe mata ta shiga. Kafin zuwanta Sarki ya riga ya ɗanɗana dukkan
miyan da ‘yan matan suka kai, amma babu wadda ya gamsu da ita. Saboda haka, da
Yelwa ta kai tata miyar, Sarki bai so ya ɗanɗana ta ba, sai da tsohuwar nan ta matsa kusa da shi ta raɗa masa
cewa ya taɓa. Sarki ya taɓa ya ji miyar Yelwa zaƙi cakwai,
abin ba dama. Ba da ɓata lokaci ba, washe gari Sarki ya bayyana mata buƙatarsa ta autenta. Ya ce in ta yarda ta je ta shaida wa
iyayenta a ɗaura musu aure nan da kwana biyu. Yelwa ta tafi tana kuka
saboda baƙin cikin maraici, domin tuni mahaifanta suka rasu. Ta
fara batun zuci tana cewa: “Kaito, yaya zan yi da raina yanzu, ga ni ba ni da
iyaye.” Can sai ga tsohuwar nan ta bayyana, ta ce mata ta daina kuka, kar ta
damu, komai zai yi kyau. Ta umurce ta da ta je ta samo ƙwari biyu ta kawo mata. Da ta kawo sai tsohuwar ta mai da
su mutane, mace da namiji, wato sun zama iyayen Yelwa ke nan. Daga nan suka
tasam ma fada, aka ɗaura aure. Nan fa sai ƙawayen
Yelwa suka ji kunya, suke nemi gafararta. Yelwa ta yafe musu saboda halinta na
haƙuri. Ita da ƙawayen
suka zauna lafiya har kowacensu ta yi nata auren.
Ashe ke nan, duk lokacin da aka cuce ka kada ka ƙudurci aniyar ramawa, yin yafiya shi ne mafi alheri da
kawo zaman lafiya. Haka ne kuma zai sa wanda ya cuce ka yin da-na-sani da jin
kunya, don haka ba zai ƙara cutar da kowa ba. Haka ma, Allah
kan musanya ma wanda aka cuta ya yi haƙuri da
mafificin alherinsa, kamar dai yadda ya faru ga Yelwa a cikin wannan tatsuniya.
Haƙuri
Hausawa na cewa: “Haƙuri
maganin zaman duniya”, kuma “Mai haƙuri
mawadaci”. Haƙuri na daga cikin abubuwan da ke kawo
zaman lafiya da sasantawa a rayuwar al’umma, kamar yadda rashinsa ke haifar da
tashin-tashina da rikice-rikice masu cin zarafin rayuwa. Rikice- rikicen addini
da ƙabilani da rikicin aure da siyasa waɗanda suke
addabarmu a yau, duk suna faruwa ne a dalilin rashin kai zuciya nesa, wato
rashin haƙuri. A kan haka, Hausawa sun samar da wasu tatsuniyoyi
masu koyar da haƙuri domin a yi koyi da karantarwarsu
don kyautata rayuwar duniya da ma ta
gobe ƙiyama. Akwai wata tatsuniyar “Tasalla mai kifi” da aka
kawo a cikin Taskar Tatsuniyoyi na
Bukar Usman, wadda ta kasance mai haƙuri da
yafiya bayan an zalunce ta. Tatsuniyar dai ta bayyana cewa, akwai wata mace mai
suna Tasalla wadda ke kiwon kifi har suka saba da juna, sukan yi wasa tare a
wasu lokuta. Wata rana Tasalla ta yi tafiya, sai mutanen ƙauyen suka
kama kifin suka cinye. Bayan da Tasalla ta dawo ta nemi kifinta ƙasa da sama ba ta gani ba. Da ta yi cigiya ba ta sami
bayanin komai ga kowa ba. Daga nan sai ta yi wani siddabaru wanda ya ƙarar da ruwan ƙuyen baki ɗaya aka
rasa na sha balle na abinci. Wannan ya sa mutanen ƙauyen da
Sarki da mahaifiyarta suka yi ta ba ta haƙuri, sai
ta haƙura ta kuma warware siddabarun da ta yi, sai ruwa ya samu
kowa ya wadata. Ga cikakken bayanin tatsuniyar kamar haka:
Tatsuniyar Tasalla Mai Kifi
Tasalla mace ce wadda ke zaune a wani ƙauye mai suna Saladuna. Tana kiwon wani kifi babba har
sun saba da juna. Tasalla tana ciyar da kifin a kullum gwargwadon ƙarfinta. Saboda sabon da suka yi da juna, har yakan riƙa yin tsalle cikin wasa da ita. Wata rana Tasalla ta yi
tafiya, sai mutanen ƙauyen suka
kama kifin nan suka cinye. Da Tasalla ta dawo ta nemi kifinta ko sama ko ƙasa, ya ɓace. Ta yi tambaya da cigiya ko ta ji wani abu game da da
kifin, amma ba ta sami bayani daga bakin kowa ba. Nan take ta shiga kukan
takaici. Wannan ya sa ta yi wani siddabaru da ya ƙarar da ruwan garin, kowa ya rasa ko ruwan wanke ido,
balle na wanka da girki. To amma akwai wani mutum ɗaya da
Tasalla ke jin nauyi, kuma tana matuƙar ƙaunarsa. Sai aka turo mata shi domin ya roƙe ta ko za ta warware siddabarn da ta yi suka rasa ruwan
sha. Sai ya zo yana rera waƙa yana roƙonta amma ba ta mince ba saboda ta yi fushi. Sarkin garin
da fadawansa suka ɗunguma suka je roƙonta, amma
ta ƙi saurarensu. Sai can uwarta ta zo ita kaɗai ta roƙe ta ruwan sha. Saboda ƙaunar da
take yi wa uwar, sai ta daina fushin da take yi. Nan take ta warware
siddabarun, ruwa ya samu kowa ya wadata da shi. Daga bisani mutanen garin suka
zo suna ba Tasalla haƙuri, kuma
suka amince lallai sun yi mata laifi da suka cinye mata kifi. Sai ta yi haƙuri, ta bar ma Allah. Sai kuma mutanen garin suka ɗauki alƙawari za su nemo mata wani kifin. Bayan watanni suka samo
mata wani kifin. Sabon kifin yana da ruwan zinari, kamar dai wanda aka cinye.
Wannan ya sa zaman lafiya tsakaninta da su ya tabbata. Kifin ya girma, kuma ya
dinga hayayyafa. Daga ƙarshe dai
har kifin ya zama ya wadaci mutanen garin.
Wannan tatsuniya ta nuna cewa, haƙuri da
yafewa na kawo zaman lafiya da sasantawa a tsakanin al’umma, kamar yadda
rashinsu ke haddasa gaba da rikici a rayuwa.
Haɗin Kai
Ko shakka babu, haɗin kan al’umma wuri ɗaya yana
haifar da ci gabanta da kawo zaman
lafiya mai ɗorewa, domin babu abin da rarrabuwar kawunan al’umma ke
haifarwa face koma baya. A duk lokacin da mutane suka haɗa kai suka zama tsintsiya maɗaurinki ɗaya, ƙarya ne ‘yan hana ruwa gudu da masu haɗawa su
gudu, su sami kafar haddasa husuma a cikinku. A ƙoƙarin Hausawa na yayata zaman lafiya ta hanyar haɗa ƙarfi da ƙarfe, sun samar da wasu tatsuniyoyi da
ke bayyana amfanin haɗin kan al’umma wuri ɗaya domin
a gudu tare, a tsira tare. Akwai wata tatsuniyar “Kurege mai wayo” da ke cikin
littafin Taskar Tatsuniya na Bukar
Usman, an bayyana cewa, an yi wani lokacin yunwa babu abinci. Sai Kura da
Maciji da Alade da Kurege suka haɗa kai domin su yi noma tare su fita cikin bala’in da ke
damun su. Hakan kuwa aka yi, inda aka raba wa kowa aikin da zai yi, hakan ya sa
suka sami nasarar da suke buƙata na samun abinci suka fita daga ƙangin yunwa. Ga labarin tatsuniyar kamar yadda take:
Tatsuniyar Kurege Mai Wayo
Akwai wani lokaci da aka yi yunwa, ba
abinci. Wuya ta sa Kura da Maciji da Alade da Kurege suka haɗa kai
domin su yi noma tare. Sai suka zaɓi wani fili a dajin da suke, suka gyara, ya zama gonarsu.
Jim kaɗan kafin damana ta faɗi, sai Maciji ya ce shi zai yi sassabe. Alade ya ce: “Ni
zan yi muna huɗa.” Kura ta ce: “Ni zan nome muna gonar. Kurege kuwa sai
ya ce: “Ni kuma zan nemo muna irin shukawa.”A daidai lokacin da ya dace, sai
Maciji ya tuge bishiyoyin gonar ya ƙone. Alade
ya yi musu huɗa. Kura ta nome. Kurege ya tafi neman irin shuka a
kasuwa, sai ya ga wata mata ta tara dawa da masara da gyaɗa da wake.
Nan ya yi mata wayo ya samo iri aka zo aka shuka aka sami amfani...
Wannan ya nuna muna cewa, haɗin kai
wani mataki ne na kawar da duk wata matsala da ta taso a tsakanin al’umma. Dubi
yadda rikice-rikice suka dabaibaye addinin Musulunci a faɗin duniya
musamman tsakanin mabiya Sunna da mabiya Shi’a. Wannan yana faruwa ne sakamakon
rarrabuwar kawunan mabiya addinin. Da za su haɗa kai su
zauna su sasanta a fahimci juna, da an kawo ƙarshen
rikicin da ya share zamunna ana fama da shi.
Kammalawa
Bisa ga misalan tatsuniyoyin da suka gabata, za a aminta
da cewa, tatsuniya ta kasance wata taska ta adana tarsashin rayuwar Hausawa
musamman a kan zaman lafiya da sasantawa wanda shi ne jigon ci gaban rayuwar
kowace al’umma a duniya. Matsalar da ake fuskanta a yau na rashin zaman lafiya
yana da alaƙa da watsi da tanadin al’adunmu na gargajiya da koyarwar
magabata. Ba shakka, da za a waiwayi baya a sake yi tanadin al’adunmu karatun
ta natsau, lallai za a samu sauƙi na mawuyacin halin da ake ciki.
Manazarta
Bunza, A.M. (2015)
“Zama Lafiya Ya
Fi Zama Ɗan
Sarki: Shirin Tunkarar Zaɓen 2015 a Nijeriya” Takardar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani kan kyautata zama lafiya a zaɓen da za a gudanar a shekarar 2015 wanda ƙungiyar Orphans and Huffaz Educational Foudation Birnin
Kebbi ya shirya.
Bunza, A.M. (2015)
“Zaman Lafiya da Tsaro a Daular Musulunci ta Sakkwato: Abin Koyi ga Shugabannin
Zamaninmu”. Takardar da aka gabatar a taron yini ɗaya da Centre for Intellectual Services on Sokoto
Caliphate ta shirya na faɗakarwa a kan muhimmancin tsaro da zaman lafiya.
Bunza, A.M.
(2015) “Labarin Zuciya a Tambayi
Fuska: Saƙon Dariya Ga Sasanta Tsaro
a Farfajiyar Karatun Hausa”. Takardar da
aka gabatar a Makarantar Harsuna, Sashen Hausa na Kwalejin
Ilimi ta Adamu Augie, Argungu.
Ezirim, G.E.
(2009) “The Role of Civil
Society in Conflict Management” in Peace Studies and Conflict Resolution
in Nigeria: A Reader,
Edited by Ikejiani-Clark M.
Ibadan: Spectrum Books Limited.
Francis, D.J. (2006) “Peace and Conflict Studies: An
African Overview of Basic Concepts” in Introduction to
Peace and Conflict
Studies in West Africa, Edited by Shedrack Gaya Best. Ibadan:
Spectrum Books Limited.
Koko, H.S. (2009) Tatsuniyoyin
Hausa a Rubuce. Sokoto: Makarantar Hausa Publishers.
Usman, B.
(2012) Taskar Tatsuniya: Littafi na Ɗaya zuwa na Goma sha Huɗu. Kano:
Gidan Dabino Publishers.
Sani, S. (2007) The
Killing Fields: Religious Violence in Northern Nigeria. Ibadan: Spectrum Books
limited, Spectrum House.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.