𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam Shin Wankan Juma'a Yanakan Mai Zuwa Juma'a Ne Ko Har da Wanda Yake Gida?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumusalam warahmatallahi wabarakatuh
Wankan juma'a mustahabbine ba wajibi bane abisa
maganar jamhur ɗin malamai. Wasu
suntafi akan wajabcinsa.
Wankan juma'a Sunnah ne akan wanda zaije Sallar
juma'a mace ne ko namiji, duk da cewa maza aka nemi suhalarceta a cikin faɗin Allah maɗaukakin Sarki:
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا إِذَا نُودِيَ لِلصَّلَاةِ مِنْ
يَوْمِ الْجُمُعَةِ فَاسْعَوْا إِلَىٰ ذِكْرِ اللَّهِ وَذَرُوا الْبَيْعَ ۚ ذَٰلِكُمْ
خَيْرٌ لَكُمْ إِنْ كُنْتُمْ تَعْلَمُونَ
Yã kũ waɗanda suka yi
ĩmãni ! Idan anyi kirã zuwã ga Sallah a rãnar Jumu´a, sai ku yi aiki zuwa ga
ambaton Allah, kuma ku bar ciniki. Wancan ɗinku ne mafi alheri a gare ku idan kun kasance kunã sani.
Saidai idan mace ma zata juma'ar an shar'nta mata
wanka saboda juma'ar dakuma ladabtuwa da ladabin juma'a ɗin.
Hakika ibnu hibban yayi babi a cikin Sahihin
littafinsa ya ce ( Babinda zai magana akan mustahabbancin wankan juma'a ga mata
idan sunasan halartar juma'ar)
Sanna yakoro hadisin Usman Bin waqid Umry daka
nafi'u daka Ibnu Umar ya ce: Manzan Allah Sallallahu Alaihi wasallam ya ce: (
Wanda zashi sallar juma'a cikin maza ko mata to yayi wanka)
Hadisin Bukhari da muslm sun ruwaitoshi banda
karin ( Cikin maza da mata) wannan karin Ibnu kuzaima da ibnu hibban da baihaqi
a cikin sunan sun ruwaitota, Malamai sun yi Saɓāni akan ingancinta.
Nawawi Allah yajikansa darahama yaingantata a cikin
maj-mu'u ( 4/405) da ibnu mulqim a cikin Badarul Muneer ( 4/649)
Alhafiz ibnu hajar Allah yajikansa da rahama a
cikin fat-hul bari ( 2/358) ya ce: Maruwaita hadisin amintattune, saidai bazzar
ya ce: Ina tsoran kada yakasance Usman bin waqid wahami yayi.
Abunda Ibnu bazzar yaji tsoro na wahamin usmanu
bin waqid abu daudama yatafi akansa Allah yajikansa da rahama.
Abu Ubaidal Ujuri ya ce: Natambayi Abu Dauda akan
usman bin waqid ya ce: Za'ifine,
Sai na ce da Abu dauda Abbas bin Muhammad
yaruwaito daka yahya bin Ma'een cewa amintaccene shi? ya ce: Za'ifine yaruwaici
hadisi Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya ce ( Wanda zashi sallar juma'a
cikin maza ko mata yayi wanka) Bamusan wani daya fadi hakan ba sai shi
Tahzeebul kamaal ( 19/505)
Shaik Albani ya raunana wannan hanyar yakuma nuna
fandararriya ce duba sil-sila za'ifah ( 8/430)
Daka cikin Abunda yake karfafa cewa mata zasuyi
wankan juma'a inzasuje sallar shine abunda ibnu Abu shaiba ya ruwaito a cikin
Musannaf dinsa daka Ubaidata bintu na'il ta ce: Naji ibnu Umar da ibnata sa'ad
bin Abu waqqas suna cewa: ( wacce zataje masallaci a cikinku ta yi wanka)
dawuus yaruwaito irin wannan hadisin, daka shaqeeq yakasance yana Umartar
iyalinsa maza da mata suyi wankan ranar juma'a duba Al-Musannaf ( 2/9)
Wankan juma'a ma'narsa shine tsafta da gusar
dawari mara daɗi daka jikin mutum
saboda haka aka umarci mace idan zataje ta yi wanka.
Imamun Nawawi Rahimahullahu ya ce: Wankan juma'a
bawaji bane wajinbinda idan kabarshi ka yi saɓo sunnah ne ga maza da mata, duba Al-maj-mu'u ( 4/405)
Dan haka wankan juma'a bayakan wanda yake gida
saiga wanda zashi sallar juma'a, Sunnah ne ahakkin mace dana miji.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.