Ticker

6/recent/ticker-posts

Shin Dole Sai Na San Wanda Ya Koya Min Sallah

TAMBAYA (202)

Assalamu'alaikum malam barka da safiya

Tambayana a kan sallah ne malam wai an ce dole kowani musulmi ya san malamin da ya koya mai sallah?

Ni kuma wallahi bawan da ya koya mun na taso Na ga ana yi ne malam Dan Allah a koya mun 🙏🏼???

AMSA

In dai har ya zama dole a dinga bawa gangar jiki abinci da ruwa don ta tayu to ya zama dole mutum ya koyi yanda ake bautawa Allaah Azzawajallah don wannan Ibadar ita ce abinci da abin shan Ruhin kowanne dan Adam kafiri da musulmi, wanda daman babban dalilin da ya sa Allaah ya haliccemu shi ne don mu bauta masa

Kamar yanda ya jaddada haka a cikin ayoyi da yawa daga Qur'ani:

( وَأَنِ اعْبُدُونِي ۚ هَٰذَا صِرَاطٌ مُّسْتَقِيمٌ )

يس (61) Yaseen

"Kuma ku bauta Mini. Wannan ita ce hanya madaidaciya."

Kuma daman duk wanda bai bautawa Allaah ba to kuwa zai bautawa son zuciyarsa, daganan wuta tazamo makomar:

( وَقَالَ رَبُّكُمُ ادْعُونِي أَسْتَجِبْ لَكُمْ ۚ إِنَّ الَّذِينَ يَسْتَكْبِرُونَ عَنْ عِبَادَتِي سَيَدْخُلُونَ جَهَنَّمَ دَاخِرِينَ )

غافر (60) Ghafir

Kuma Ubangijinku ya ce: "Ku kira Ni in karɓa muku. Lalle waɗannan da ke kangara daga barin bauta Mini, za su shiga Jahannama suna ƙasƙantattu."

Tunda dai har bai halicci mutum da Aljan ba sai domin su bauta masa:

( وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإِنسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ )

الذاريات (56) Adh-Dhaariyat

Kuma Ban halitta aljannu da mutane ba sai dõmin su bauta Mini

Kenan ta yaya zamu bauta masa

Ta yanda ManzonSa ya koyar damu

Sai mu tuno da hadisin dake cikin Sahihayn (Bukhari da Muslim riwayar Abu Hurairah (Radiyallahu anhu) Wanda Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya ce: "Sallu kama ra'ayat muni usalli", bi ma'ana: "Kuyi Sallah kamar yanda kuka ga Ina yi"

Wannan fa Umarni ne bawai shawara ba

Kenan cikin biyu dole zamu fada daya:

Ko dai muna Sallar mu ne irin yanda Annabin ya koyar da Sahabbansa ta hanyar karanta littattafai irinsu: "SIFATU SAKATIN NABY MINAT TAKBIRI ILAT TASLIM KA'ANNAKA TARAHA" (Siffar yanda Annabi ya koyar da Sallah tun daga Takbir har zuwa Sallama Kamar kana kallon Sallar)

Ko Kuma na biyu, mun ta so ne mun ga ana Sallar a al'adance muma muja ara muka yafa. Wanda dole a nan za a Kura kurai kam

In dai har wancan Sahabin zai maimaita Sallah sau 3 a Masjidin Nabawy Kuma Ma'aiki Sallallahu alaihi wasallam ya ce masa ko ma ka sake Sallah domin kuwa baka da sallah

To Ina Kuma ga mu yan karshen Zamani Wanda tazararmu da wancan lokacin ta zarce shekaru 1,400

Ka ga kenan akwai aiki jajawur a gabanmu

Akwai wani Sahabin da baya yin Cikakkiyar Ruku'u da cikakkiyar Sujjada, haka Ma'aiki ya ce wallahi da zai mutu yana hakan to da sai dai a tashe sa a cikin mutanen Zamanin Jahiliyya

To ka ga kenan dole kowa ya zamana yana da Malamin da ya yarda dashi wanda zai koya masa Sallah irin ta Annabin tsira ba Sallah irin ta al'adah ba

Wannan dalilin ne ya sa na rubuta littafin: "KURA KURAI 100 A CIKIN SALLARMU" , idan kana bukatar lectures din sai ka shiga Telegram dinka kayi searching "USMANNOOR ACADEMY", kana daga gida zaka gyara sallarka ta waya ba tareda kaje wani wajen ba kuma FREE ne, babu Registration

Ka ga kamar ni yanzu, zan iya kafa hujja da a qalla sama da Malamai guda 9 da na koyi Sallah a wajensu

1) Shaikh Muhammad Nasiriddin al-Albany (Rahimahullah)

2) Shaikh Jafar Mahmud Adam (Rahimahullah)

3) Shaikh Muhammad Auwal Albany Zariya (Rahimahullah)

4) Shaikh Assim Alhakim (Malaminmu ne a yanzu haka yana koyar da mu Seerah a makarantar ZAD ACADEMY dake Makkah)

5) Shaikh Prof. Mansur Isah Yelwa Esq (Hafizahullah)

6) Shaikh Aminu Daurawa (Hafizahullah)

7) Shaikh Tijjani Guruntum (Hafizahullah)

8) Dr. Abdallah Usman Gadon Kaya (Hafizahullah)

9) Shaikh Prof. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo (Hafizahullah)

Don Allaah ku turawa wasu su ma su amfana

Subhanakallahumma wabi hamdika ash-hadu anla'ilaha illa anta astaghfiruka wa'atubi ilayk

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments