𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Malam. Ni Magidanci ne ina da aure. To tun kwanakin baya matata ta yi tafiya ba ta dawo ba. To akwai wasu abokaina da suke harkar neman mata, rannan sai suka kawo 'yan matansu nan gidana, Nima ina gidan alokacin ashe sun kawosu ne da niyyar za su aikata lalata dasu. Naso in hanasu amma ina tsoron za su ga kamar na yi musu gadara tunda gidana suka zo. Na zauna cikinsu muna zance har shaiɗan ya rinjayeni har na yi zina da wata daga cikin matan nan da suka kawo. To tun daga ranar kullum sai na yi kuka saboda bakin ciki da tunane-tunane. Na kasa samun kwanciyar hankali domin tunda nake ban taɓa aikata wannan mummunan aikin ba sai ranar nan. Na rasa yadda zan yi. Shin Malam kana ganin Allah zai gafarta mun, ko kuwa sai na sanar da matata idan ta dawo, tunda kamar naci amanarta ne?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus
salam wa rahmatulLahi wa barakatuhu.
Hakika ka
tafka babban kuskure. Domin zina tana cikin Kaba'irori wato zunubai mafiya girman
laifi awajen Allah. Awani hadisi Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam cewa
ya yi "Bayan yin shirka da Allah, babu wani zunubi mafi girman laifi kamar
maniyyin da namiji ya sanyashi acikin mahaifar matar da ba ta halatta gareshi
ba".
Sannan bayan
haka ka cire kanka daga cikin sahun muminai ta dalilin wannan mummunan aikin.
Domin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ya ce "mazinaci ba zaiyi
zina alokacin da yake zina alhali yana mumini ba". Wato ana cire wa mutum
rigar imani ne alokacin da yake aikata zina ko sata ko shan giya. Ba za a dawo
da ita gareshi ba, har sai bayan ya tuba.
Tunda kayi
nadama kuma kana da niyyar tuba, to ga hanyoyin tuban kamar haka:
1. Yin
nadama bisa abin da ka aikata.
2. Ɗaukar niyyar har abada ba zaka sake aikata wannan zunubin
ba. Yanke alaqah tare da nisantar duk wani dalilin da zai kaika zuwa ga sake
aikata wannan laifin.
3. Dena
aikata laifin nan take ba tare da jinkiri ba.
Sannan yana
daga cikin cikar tubanka ka yanke alaqah da waɗannan miyagun
abokan naka domin akwai alamar watakil su sun riga sun saba da wannan mummunan
aikin. Ci gaba da hulda dasu zai iya sake jefaka cikin rudanin nan nasu. Kada
su sake yaudararka.
Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wasallam ya fadi muhimmancin abokai nagari da kuma illar haɗa abota da mutanen
banza, a inda ya ce : "kada kayi abota sai da mumini, kuma kada wani yaci
abincinka sai mai tsoron allah". (Abu Dawud, Tirmidhiy da Ahmad ne suka
riwaitoshi).
Malamai suka
ce wannan hadisin yana Kaɗaitar da mutum musulmi ne akan cewa lallai ya kasance
tare da mutanen kirki kuma ya guji abokantaka da mutanen banza misali kamar
kafirai, munafukai, ko masu aikata miyagun laifuka irin su zina, shaye-shaye da
sauransu. Domin kuwa abota takan chanza wa mutum tarbiyyarsa da halayyarsa.
Acikin wani
ingantaccen hadisi kuma wanda Imam Abu Dawud da Tirmidhiy suka riwaito ta
hanyar Sayyiduna Abu Hurairah, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam cewa ya
yi : "mutum yana kan addinin abokinsa ne. don haka kowanne daga cikinku ya
rika lura da irin mutumin da zai yi abota dashi".
Ma'anar
wannan hadisin ita ce: wato lallai ne ka rika zabar irin mutanen da zaka Qulla
abota dasu domin tarayya irin wannan takan yi tasiri wajen lalacewa ko
kyautatuwar tarbiyyar mutum da rikon addininsa. Kamar dai yadda Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wasallam ya fada acikin wani shahararren hadisi "mutum
yana tare da wanda yake qauna"
Don haka
nake baka shawarar cewa ka chanza wasu abokai na kirki waɗanda tarayyarka
dasu za ta amfaneka awajen Allah, banda irin waɗannan abokan banza
waɗanda sai kayi
nadamar saninsu aranar Alqiyamah.
Kaci gaba da
tuba da kula da ayyukanka na farilla da kyautatawa mahaifanka da makusantanka
da masu Qaramin karfi. Idan Allah ya so zai karɓi tubanka ya yafe
ma zunubanka. Amma ba sai ka gaya wa matarka abin da ya faru ba, domin kuwa
wannan ba ya cikin sharudan tuba, kuma zai iya zama dalilin lalacewar alakarka
da iyalinka ko zubewar mutuncinka awajenta.
WALLAHU
A'ALAM.
DAGA ZAUREN
FIQHU 07064213990
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.