Citation: Muhammad, A.I. (2024). Salon Shillo a Bakin Makaɗan Baka na Hausa. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 336-340. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.042.
SALON SHILLO A BAKIN MAKAƊAN BAKA NA HAUSA
Alhaji Ibrahim Muhammad
Fadar Mai girma Ɗan’alin Birnin Magaji, Birnin Magaji, Jihar
Zamfara
Tsakure:
An gabatar da wannan tsokaci domin shiga sahun marubuta maƙalu
domin karrama Farfesa Abdullahi BayeroYahya. Manufar wannan tsokaci shi ne a yi
nazarin wani salo wanda masana suka kira salon shillo a waƙoƙin
Hausa. Salo kamar yadda aka sani wata hanya ce cikin waƙoƙin baka da mawaƙa ke
bi domin isar da saƙo. An saurari waƙoƙin baka da aka samo a gidajen rediyo da
na wajen masu sayar da kaset-kaset, da yin nazarin waƙoƙin daga bisani, aka riski
cewa da wannan salo ne mawaƙa suka ci kasuwarsu da shi a cikin waƙoƙinsu. Salon shillo tsohon
salo ne a bakin mawaƙan baka.
Fitilun Kalmomi: Salo, Shillo, Makaɗan Baka, Hausa
Gabatarwa
Waƙa a ƙasar Hausa
sunanta waƙa. Sai dai a samu nau’o’inta. Ana cewa
waƙar baka, ana kuma cewa rubutacciyar waƙa. Waɗannan manyan nau’o’in waƙa su ne muka fi sani, duk da cewa, (Usman, 2021:03) ya zo da wani
kason a nasa bincike. A wannan tsokaci an nuna yadda wata fasaha ta babban shaihimmu na waƙa, ta yi mini tasiri wajen lalaben abin da zan gabatar
a wannan tsokaci. A cikin aikin (Yahya, 2016: 161)[1] an kawo
wannan salo da ma’anarsa da inda ake samun misalansa. An ɗauki
ɗaya daga cikin fitattu kuma tsofaffin mawaƙan baka, aka kuma ɗauki ɗaya
daga cikin waƙoƙinsa domin a yi nazarin wannan salo na shillo a cikin waƙar. Za a ga taƙaitaccen
tarihin mawaƙin da kuma sunan waƙar da wanda aka yi wa waƙar a matsayin shimfiɗa
kafin a shiga cikin
aikin gadan-gadan.
1.0
Ma’anar Salo
Salo wata
hanya ce ta daban da ba a saba gani ba. Ko kuma samun wata hanya ta daban domin
isar da saƙo in ji shaihin malamin salo wato
Yahya, 2016:28[2]
Kalmar salo
na nufin amfani da hanyoyi da dabarun jawo hankalin mai karatu ko mai sauraro
da marubuci ya yi amfani da shi, domin ya ƙara ma rubutunsa armashi. Wato ke nan “Salo”
hanya ce ko dabara ta yin wani abu ko bayyana wani abu[3].
1.1
Salon Shillo
Ɗarsau
Ɗaga hankali ko kwaɗaitarwa
wata dabara ce da mawaƙa ke amfani
da ita domin su sami damar isar da saƙonsu
cikin armashi. Mawaƙa kan ƙirƙiro wani
abu da zai motsa tunanin mai karatu, mai sauraro kan nace sai ya bi makaɗi
ko mawaƙi ko marubci har ƙarshen fasaharsa domin ya fahimci manufarsa. Irin wannan
kwaɗaitarwa kan ƙunshi ɗaga
hankali ko ba da mamaki, ko sanya dariya ko saka ɗauki
da murna, ko ban haushi, ko takaici ko ƙara
gishiri da sauransu[4].
Salon
shillo a wata fassarar shi ne jerangiyar da mawaƙi kan yi ta musamman a farkon waƙarsa wadda a dubin farko mai karatu ko saurare zai ɗauka
abin da mawaƙi ke faɗa
ba ya da wata nasaba da babban jigonsa ko saƙonsa, amma kuma haƙiƙani akwai wannan dangantaka[5].
Daga bayanan da suka gabata kan ma’anar salo da kuma ƙarin sharhi kan salon shillo za a matsa gaba a ga tarihin
waƙa da waɗanda
aka yi wa waƙar da kuma masu yin waƙen.
1.2 Tarihin waƙar “Kana
shire baban ‘yan ruwa, na Bello Jikan Ɗan
Hodiyo”
Wannan Waƙa an yi ta tsakanin shekarar 1963 zuwa 1966 duk kuwa da
yake an sha maimaita ta a lokutta daban daban, a wurare mabanbanta abun da ya
zama sanadiyar samun wasu ƙare - ƙare masu dama a cikinta daga baya.
Waƙar ta naɗe muhimman lamurran rayuwar wanda aka yi wa ita da ma
wanda ya yi ta.
Wannan Waƙar ita ce Bakandamiyar Makaɗa
Sa'idu Faru. Kamar wada ya sha faɗa a mafi yawancin hirarraki ko tattaunawar da aka yi da
shi cewa a duk lokacin da yake wasa, kiɗa da waƙa a sarari, ita ce waƙar da ya fi fara rerawa saboda ita ce yawancin jama'a ke
buƙatar ya rera masu. Ya yi wannan waƙa shekaru da dama kafin wanda ya
yi wa ita ya hau karagar sarautar Sarkin Musulmi a 1996.
2.0
Makaɗa Sa’idu Faru: Sanin wane shi a taƙaice
Makaɗa
Sa’idu Faru na daga cikin daɗaɗɗun makaɗan baka kuma makaɗan fada da suka
yi fice a ƙasar Hausa. Binciken wannan maƙala ya ɗora shi daga cikin makaɗan
sarauta. An haifi Sa’idu Faru a garin Faru, ƙarƙashin
Maradun ta cikin ƙasar
Zamfara ta yanzu a shekarar 1916. Laƙabinsa
Ɗan’umma. Abubakar Maikotso, wanda ake
yi wa laƙabi da Abubakar Kusu, shi ne
mahaifinsa. Abubakar Kusu ɗa ne ga Alu
Mai Kurya. Asalinsu
Gobirawa[6] ne. In dai ana maganar gadon
kiɗa, to Sa’idu Faru ya gadi kiɗa
ga uwaye da kakkanni, domin Alu Maikurya makaɗin
yaƙi ne, musamman ga mayaƙan ƙasar Gobir[7]. Sa’idu Faru ya yi wafati a
shekarar 1987 a garinsu Faru bayan gajeriyar jinya.
3.0
Muhammadu Macciɗo: Sarkin Kudun Sakkwato
An haifi
Alhaji Muhammadu Bello Macciɗo a garin Dange, ƙaramar
Hukumar Mulkin Dange/Shuni da ke Jihar Sokoto a shekarar 1926[8]. Mahaifinsa shi ne Sarkin
Musulmi Abubakar III, mahaifiyarsa
kuma ita ce Hauwa'u. Ya yi karatun Addinin Musulunci a garin Dange kafin ya
shiga makarantar ilmin zamani da ya kai shi har Zaria daga nan ya wuce Babbar
Kwalejin South Devon da ke ƙasar
Birtaniya tsakanin shekarar 1952-53. Ya riƙe muƙamin Uban Ƙasa/Hakimin Gundumar Talata Mafara da ke jihar Zamfara ta
yanzu tsakanin shekarar 1953 zuwa 1956. Alhaji Muhammadu Macciɗo
ya zama wakilin majalisar dokokin jihar Arewa a Kaduna a cikin shekarar 1954,
ya kuma yi aiki a En'a (NA) ta Sokoto a matsayin kansila mai kula da sashen
ayyuka kafin a canja masa wajen aiki zuwa sashen raya karkara da kuma sashen
aikin gona tsakanin shekarun 1950 da na 1960.
Tsakanin
1967 zuwa 1970 ya riƙe muƙamin Kwamishinan ayyukan gona da kuma harkokin lafiya a
tsohuwar jihar Arewa maso Yamma[9]. Ya zamo Shugaban
Rusasshiyar Jam'iyyar NPN da kuma mai bai wa shugaban tarayyar Nijeriya shawara
ta musamman a tsohuwar jihar Sokoto a ƙarƙashin mulkin shugaba Shehu Shagari tsakanin 1979 zuwa
1983.
A shekarar
1986 Alhaji Muhammadu Macciɗo ya samu shiga a cikin majalisar da ke taimaka wa
mahaifinsa, Sarkin Musulmi Abubakar III a wajen gudanar da sha'anin
mulki.
An naɗa shi Sarkin
Musulmi na 19 a cikin watan Afrilu na shekarar 1996, Allah ya yi masa wafati
Ranar 29/10/2006 sanadiyar haɗarin jirgin
saman
ADC Airline a Abuja. Allah ya jiƙan sa da
rahama, amin.
4.0 Dubarun Tattara Bayanai
An saurari
waƙoƙin
Sa’idu Faru daban-daban waɗanda ke cikin fayafai na rediyo, an kuma nazarci abin da
manazarta suka kalato na game da tarihinsa da fasihancinsa cikin waƙa, waɗanda aka taskace cikin kundaye da litattafai na adana
tarihin makaɗan baka. Haka
kuma an
tattauna da wasu ɗalibai da malamai masoya Sa’idu Faru inda suka bayyana
abin da
suka sani game da shi. Marubucin
wannan muƙala ya
tattauna da Makaɗa Sa’idu Faru, tattaunawa mai dama a kai dangane da fasihancinsa. Ta wannan tattaunawa aka
san dangantakarsa da uban gidansa, Sarkin Musulmi Muhammadu
Macciɗo. Kafin dai a shiga gadan-gadan ga nazarin ɗaya
daga cikin waƙoƙinsa, zai dace a shaidar da cewa, a wasu lokutta cikin
shekarun 1979 zuwa 1984 a lokacin da shi Makaɗa
Sa’idu Faru da tawagarsa sukan kai ziyara a Birnin Magaji, garin marubucin nan,
wajen Ɗan’alin Birnin Magaji Alhaji Muhammadu
Mode Usaman (1945-2005)[10]. Wannan ziyara ta kiɗa
da waƙa ce tsakanin uban gida da baransa mawaƙi. Abin da ake son a shaidar shi ne, wannan marubuci yana
daga cikin masu halartar wannan majalisi na Sa’idu Faru a lokacin da yake
baje kolin fasaharsa ta waƙa. Ɗaya daga cikin waƙoƙin da ake iya tunawa da ita ita ce /Mai ɗamara
Ɗan’Ali/Ɗan Shehu Sadaukin Sarki/. Akwai kuma wata waƙar mai amshi kamar hakan: /Alhaji Ɗan’Ali ci fansa/Abin biya kake Ɗan Shehu/.
Waɗannan
misalai ne na waƙoƙin Sa’idu Faru waɗanda ya
rera a garin Birnin Magaji Fadar Ɗan’Ali kuma
na Ɗan’Alin. Waɗannan
waƙoƙi
suna daga cikin waɗanda wannan marubuci da kaina yake riƙe rikoda ta naɗe waƙoƙi wadda ake
amfani da ita a wancan lokacin[11]doimn naɗe aikinsa
a lokacin da yake rera su.
Da rikodar Hajiya
Goshi matar Ɗan’Ali, wadda tana daga cikin masoya
Sa’idu Faru da waƙoƙinsa, marubucin yake naɗiyar
waƙoƙin
Sa’idu Faru cikin sabon kaset ɗin da take ba shi tare da rikodar. Takan ba marubucin
wannan rikoda tare da sabon kaset domin ya zauna kusa ga Sa’idu Faru (in yana
rera waƙoƙinsa)
ya naɗe waƙoƙin nasa a wannan lokacin.[12]
5.0 Nazarin
Waƙar /Kana Shirye Baban ‘Yanruwa/ Na Bello Jikan Ɗan Hodiyo/
Wannan waƙa wadda Sa’idu Faru ya tsara ya kuma rera zuwa ga
ubangidansa kusan shekaru 60 da suka wuce tana da turaku da yawa da ta yi wa
mai saurare guzuri da su. Mawaƙin ya yi
amfani da salon
shillo kamar yadda aka ambata a baya domin ya isar da saƙonsa ga masu sauraro. Shi makaɗa
Sa’idu Faru kafin ya bayyana saƙonsa na
gurin da yake yi ma Sarkin Kudun Sakkato Macciɗo
na ya gadi mahaifinsa Sarkin Musulmi Abubakar III a kan gadon Sarauta. Wannan
guri na Makaɗa Sa’idu Faru ya bayyana a ɗaya
daga cikin ɗan waƙa kamar
haka:
Halin ga da Bubakar yar riƙa,
Maciɗɗo kai ka shirin gado haka,
Halin ga da Bubakar yar riƙa,
Maciɗɗo
kai ka shirin gado haka,
Wannan ɗan
waƙa ya bayyana jigon waƙa na gurin zaman Macciɗo
Sarkin Musulmi bayan mahaifinsa Abubakar III. Baiti na gaba ya bayyana ko shi
kansa baya ga sauran al’ummar Hausawa da larabawa sun yi murna da jin wannan waƙa mai gurin masoyinsu ya zama shugaban al’ummar musulmin
duniya kamar haka:
Waƙag ga da niy maka Mammadu,
Na ji daɗinta Mamman Sarkin Kudu,
Waƙag ga da niy maka Mammadu,
Na ji daɗinta Mamman Sarkin Kudu,
Tun dak Kabi har Kano har Masar,
Har birnin legas har Bichi,
Kowa ya ji waƙar Sarkin
Kudu,
Ni ko daɗinta da nij jiya,
In da zaman daji mukai,
Da kay yi waƙar Sarkin
Kudu,
Mamman yaɗ
ɗaukan yar riƙa,
Mun san manyan mutane ƙwarai,
Mun san ƙananan mutane ƙwarai,
Mun kammala duk mun ƙasura,
Baiwa mu shidda muna biye,
Sarkin makaɗammu yana gaba,
Kowa tashi ƙawa daban,
Kowwa yai
taiɓa yai ƙaton ciki,
Kog ga shi
zamne ga inuwa,
Ko da makaɗin
sarkin Masar
yag ga
Sa’idu sai rainai yai haki.
Waɗannan
ɗiyan waƙar da suka
gabata, suna ɗauke da yabo daga mawaƙi zuwa ga ubangidansa, sannan ya ɗan
taɓo wani salon zuga, inda ya bayyana cewa ya samu yalwa da arziki
ga jikinsa da suturarsa har kusan duk wanda ya gan sa ba cikin takwarorinsa
mawaƙa na ƙasar Hausa ba, har na wata ƙasa kamar Larabawan Masar sai sun ji sha’awarsa.
Babban mutun mai da gaba biki,
Ana kai biki inga Burtuttuki,
Idon fasiƙi gun
marokan[13] biki,
Wada dud ɗan Sarki yaƙ ƙasura,
In ba alheri yay
yi ba[14],
Daudu ko
yai magana ƙarya ya kai.
Wannan ɗan
waƙa da ke sama, yana da ƙumshiyar habaici zuwa wasu ɗiyan
Sarki masu hamayya da ubangidan mawaƙin.
Saboda haka akwai habaici a ɗaya daga cikin turakun da mawaƙin ya yi amfani da su wajen isar da saƙonsa na jigon guri, Wannan salon sakaɗa
habaici yana daga cikin shillon da mawaƙin
ya ci gaba da yi, ya sa ya bar duniyar mutane, ya tafi duniyar tsuntsaye da
dabbobi domin ya yi hira da su kan masaniyarsu da ubangidansa.
Can na taɓa ‘yat tafiya kaɗan,
Sai ni ‘ishe suda[15] na kiyo,
Tana ta waƙas Sarkin
Kudu,
Rainai ya daɗe Sarkin Kudu,
Alisabbinane ɗan Amadu,
Allah Shi ƙara mai
nasara
Sai ni ‘ishe burtu[16] na kiyo
Yana ta waƙas Sarkin Kudu
Rainai ya daɗe
Sarkin Kudu
Alisabbinane ɗan Amadu
Allah Shi ƙara mai
nasara
Nic ce burtu waƙa akai
Yac ce lalle waƙa nikai
Waƙam Muhamman Sarkin Kudu
In niy yi ta za ni wurin kiyo
In na zo
abinci sai na ije
Daga
duniyar tsuntsaye, ya sake dawowa duniyar mutane, amma kuma ya sabka yankin ƙasar larabawa kuma a cikin ruwa ba bisa ƙasa ba. Wato cikin bahar maliya wasu ruwa waɗanda
ake tsallakawa a shiga ƙasar
Saudiyya.
Can na taɓa ‘yat tafiya kaɗan,
Na kai bakin bahar Maliya,
Sai ni ‘ishe Larabawan wurin,
Suna ta waƙas Sarkin
Kudu,
Rainai ya daɗe Sarkin Kudu,
Alisabbinane ɗan Amadu,
Allah Shi ƙara mai nasara,
A cikin waƙar an sanar da mai saurare tafiyar da akan yi ta zuwa
aikin Hajji a Ƙasar Saudi
Arebiya domin nuna cikakkiyar nasabarsa da Mujaddadi Shehu Usman ɗan
Fodiyo tagammadahullah birahamatihi wanda ya assasa Daular Usmaniya a Nijeriya.
Idan makaɗa Sa’idu ya gama tattaunawa da Larabawa, inda suka nuna
masa cewa su kansu, suna ƙaunar Mamman
Macciɗo saboda harskensa da muruwarsa yana taimaka musu wajen
ibadarsu ta yau da kullum. Daga nan sai Sa’idu ya sake dawowa aƙasarshi ta Hausa inda ya nuna cewa ai shi duk daular da
ya samu a duniya, snadin Sarkin Kudun Sakkwato Macciɗo
ya same ta, amma kuma idan bai yi kiɗa da waƙa ga ubangidansa ba, to kullum yana cikin ƙishirwa da yunwa. Ga ɗan
waƙar da ya bayyana hakan:
"Ka kai kamab Bello, swasswakiya,
Da kyauta da milki da ban gaskiya,
Kamar mu marok'anku galgajiya,
Ko da mun ɗamre doki ɗari,
Ko da
mun tsaida mato ɗari,
Ko da
mun tsaida jikka ɗari,
Ko da
mun tsaida dame ɗari,
Ko da
mun tsaida bawa ɗari,
Dub basu kashe muna ƙwarnahi,
Sai mun ɗunka
turaye
mun kiɗa.
Mawaƙin ya rufe wannan waƙa da jaddada jigonsa na Guri ya ga ubangidansa ya zama Sarkin Musulmi da wannan ɗan
waƙar da ke biye:
Baban Mai abu Faru na Mai’akwai,
Ɗan giwa komi tad daɗe,
Ta tabbata yin giwa yakai,
In ji Sarkin Maradun Sarkin Ƙaya,
Ɗan Giwa komi tad daɗe
Ta tabbata yin giwa yakai,
In ji
Sarkin Maradun Sarkin Ƙaya.
Naɗewa
Salon
shillon da aka ambata a shimfiɗar wannan tsakure a lamba ta 1.1, ya tabbata ta nazarin ɗiyan
wannan waƙa ta makaɗa
Sa’idu Faru. Kamar yadda fahimta ta haska ma wannan nazari da aka yi, an yi
amfani da turaku kamar na yabo da zuga da habaici wajen ganin an isar da wannan
saƙon wannan waƙa na jigon Guri daga Makaɗi
zuwa ga mai gidansa. An yi wasa wasa da salon shillo tsakanin duniyar mutane
zuwa ga ta tsuntsaye, an sake sakaɗa salon hira tsakanin makaɗi
da Larabawa, da kuma tsakanin makaɗi da tsuntsaye.
Wani abin
sha’awa shi ne, gurin Sa’idu Faru ya tabbata shekaru Talatin 30 da yin wannan
waƙa. Domin an naɗa
Sarkin Kudu Macciɗo bisa Sarautar Sarkin Musulmi a shekarar 1996. Ita wannan waƙa an yi ta a tsakanin 1963-1966.
Manazarta:
Boyd,
J. (2010)Africa : Journal Of the International African Institute Vol.
80.No I, Interpreting Land Markets in Africa, Published by Cambridge University
Press
Ɗangambo, A
(BS) “Gadon Feɗe Adabin Hausa” Littafin Da Ke Jiran Ɗab’i.
Ɗangambo, A
(2005) Rabe-raben Adabin Baka Da
Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa (Sabon
Tsari), Bench Mark Publishers, Kano
Gusau,
S. (2005) Makaɗa
da Mawaƙan Hausa, Bench Mark Publishers, Kano
Hirar da nayi da Makaɗa Alhaji
Ibrahim Sa'idu Faru /Halifan Makaɗa Sa'idu Faru, a Ranar 08/03/2018
Peoples Daily Newspaper, September, 2023: Muhammadu Macciɗo,
The 19th Sultan.
Usman,
B. B. (2021)
“Ruwa Biyu: Sabon Zubin Waƙoƙin Ƙarni na
Ashirin da Ɗaya” Takardar da aka Gabatar a Taron Mawaƙan Hausa na Zamani a NUT Hotel, Magadishu Layout Kaduna.
Tattaunawa Alhaji Sa’idu Faru a lokutta daban-daban.
[1] Na karanta wannan
salo a cikin littafin Abdullahi Bayero Yahya, (2006) Salo Asirin waƙa ɗab’in Guarantee
Printers, Sokoto.
[2] Yahya, A. B. (2006) Salo
Asirin Waƙa Guarantee Printers, Sokoto
[3] Dangambo, A.
(1995:252) (BS) “Gadon Feɗe Adabin Hausa”
Littafin da ke Jiran Ɗab’i.
[4]Ɗangambo, A, 1995
kamar a ɗure na 4, shafi na
253
[5]Yahya, A. B. (2006)
kamr a ɗure na 3, shafi na
162
[6] Tattaunawar da muka yi da magadin Alhaji Sa’idu Faru, …
[7] An samu tarihin makaɗa Sa’idu Faru a cikin littafin Makaɗa da
Mawaƙan Hausa
na Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau. 2005 Century Publishers Kano shafi na 117.
[8] Peoples
Daily Newspaper, September, 2023: Muhammadu Macciɗo, The 19th Sultan.
[9] Jean Boyd, cikin Africa : Journal Of the International African
Institute Vol. 80.No I, Interpreting Land Markets in Africa, Published by
Cambridge University Press, 2010.
Shafi na 10.
[10] Shekarar sittin da wannan basaraken ya yi mulki a ƙasar
Birnin Magaji. An haife shi a shekarar 1922, ya rasu a shekarar 2005.
[11] Rikoda wadda ake saka ma kaset mai zare na daga cikin aubuwan da
ba su daɗe da aka rage amfani da sub a,
saboda shigowar sidi, da filash, amma ba don har yanzu ba a a amfani da sub a.
Amma a wancan lokacin babu wani abu da ya fi su amfani wajen naɗe duk wata murya wadda za a amfana da ita zuwa gaba, a matsayin
wata na’ura ta adana tarihi.
[12] Bayan wasu
shekaru da ina gabatar da shirin kundin mawaƙan Hausa, na sha
komawa wajen Hajiya Goshi ta ara mini kaset-kaset na Sa’idu Faru domin in
amfana da su.
[13] Wannan kalma tana nufin matan da suke zuwa wajen yinin buki na
al’ada.
[14] Wannan jigon roƙo
[15] Suda tsuntsuwa ce.
[16] Burtu wani nau’in Tsuntsu shi ma, yana
siffa da tsuntsun nan mai suna Babba da jikka.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.