Citation: Babangida, A., Gadaka, H.U. and Aliyu, H.G. (2024). Mutuwa a Muryar Alhaji (Dr.) Mamman Shata Katsina: Nazarin Wasu Waƙoƙinsa. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 328-335. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.041.
MUTUWA A MURYAR
ALHAJI (DR.) MAMMAN SHATA KATSINA: NAZARIN WASU WAƘOƘINSA
Abubakar Babangida
Hassan Usman
Gadaka
Hauwa Garba Aliyu
Hausa Department,
Umar Suleiman College of Education, Gashua
Tsakure:
Wannan muƙala mai taken “Mutuwa A Muryar Mamman Shata Katsina: Nazarin Wasu Waƙoƙinsa”, ta taɓo yadda Marigayi Alhaji
(Dr.) Mamman Shata ya ambaci mutuwa a wasu waƙoƙinsa domin isar da saƙo ga
masu sauraro. An saurari waƙoƙin Mamman Shata an jujjuya su a littafi a matsayin hanyoyin
tattara bayanai. An ɗora
takardar bisa Ra’in zalaƙa domin ta haskaka nazarin. Mutuwa jigo ne na wa’azi wadda mawaƙa
(makaɗa, kamar yadda
wasu masana suke ƙira) suke bayyanawa a cikin waƙoƙinsu da nufin cim ma burinsu. An nazarci
wasu daga cikin waƙoƙinsa ta fuskar matakan nazarin waƙar baka, inda aka fi
mayar da hankali kan manufar wannan muƙala. Sakamakon binciken ya nuna cewa,
mawaƙin
yana ambaton mutuwa ne a cikin waƙoƙinsa domin isar da saƙo ta
fuskoki kamar haka: ta’aziyya
da fatan alheri da jimami da ɗaukan
hukunci a hannu da kuma bayyana ikon Allah. Muƙalar ana fata ta zama mai alfanu da
muhimmanci ga manazarta waƙar Alhaji Mamman Shata da ma waƙoƙin baka na Hausa a jumlace.
Fitilun Kalmomi: Mutuwa, Mamman Shata, Nazari, Waƙoƙi
Gabatarwa
Hausa yaren Hausawa, harshe ne mai daɗaɗɗan tarihi Al’ummar cikinsa sun
kasance masu hazaƙa da
hikimomi da kasuwanci da al’ummai masu yawan gaske. Sabodasun zarce duk wata baƙar fata yawan jama’a da girman ƙasa a faɗin duniya. Bunza, (2000) da Yakasai, (2013) suna da tabbacin
cewar, Mahaifar harshen ita ce Arewacin Nijeriya da Kudancin Nijer.
A Ƙamusun
Hausa, (2016:354) an bayyana ma’anar mutuwa da rasuwa ko ƙarshen ran mutum ko dabba ko duk
wani abu mai rai. A duk wurin da Bahaushe yake rayuwa yana da tabbacin cewa,
mutuwa na iya ɗaukar sa ko da jinya ko kuma
haka nan salin-alin. Hatta lokacin da Bahaushe yake cikin rayuwar jahiliyya,
ma’ana kafin ya karɓi addinin Musulunci ya san da
mutuwa na ɗaukar mutum, saboda ya yi yaƙe-yaƙe da dama da dauloli mabambanta
kafin ya tsinci kansa a yadda yake rayuwa yanzu. Wannan ya kai mu ƙara tabbatar da cewa, mutuwa ta
yi tasiri da kaka-gida a zuciyar Bahaushe. Kuma a bar tsoro ce da fargaba a
zuciyarsa a jiya da yau da kuma gobe. Haka kuma a duk inda Hausawa suke, suna
sane da kuma yin ɗari-ɗari da lallai mutuwa kan iya afka musu ta kowane irin hali.
Shi ya sa ma za a ga yadda mutuwa ta mamaye duniyar adabi da al’adun Bahaushe.
A rubutun zube za a ga ana ambaton mutuwa, haka tatsuniyoyi da wasanni da
labaran gargajiya da kuma muryar mawaƙan
baka da na rubutattu. Wannan ya ƙara
fito mana da yadda Bahaushe yake kallon mutuwa[1]
a rayuwarsa. Wannan takarda ta ƙuduri
dubamutawa ne a sasu daga cikin waƙoƙin Alhaji (Dr) Mamman Shata
Katsina. Muƙalarta
bayyana yadda mawaƙin yake
ambaton mutuwa a ƙoƙarinsa na isar da saƙo ga masu sauraro. A wasu lokuta
Mamman Shata yana ambaton mutuwa ne da nufin ta’aziyya ko jimami ko kuma faɗakarwada tsoron Allah da nuna buwaya irin ta Ubangiji. Muƙalar za ta duba abubuwa kamar
haka:
1.1 Farfajiya
Bincike
Nazarin ya iyakance ambaton mutuwa ta ɓangarori daban-daban da shata ke yi a ƙoƙarinsa na isar da saƙo
ga masu sauraro. Idan aka ci karo da wani abu ya shigo, sai ko domin ƙarin haske.
1.2 Hanyoyin
Tattara Bayanai
An saurari wasu daga cikin waƙoƙin da
Alahji Dr. Mamman Shata Katsina ya yi, an kuma juya su a takarda domin yin
sharhi.
1.3 Manufar
Bincike
Wannan nazarin mai taken mutuwa a muryar Mamman Shata,
takardar tana ɗauke da manufofi kamar haka:
a.
Domin gano mece ce mutuwa
b.
Fito da yadda ake bayyana mutuwa a fagen adabi, da kuma
adabin ma na baka.
c.
Bayyana mutuwa ta hanyoyi daban-daban cikin salon labari da
tarihi.
1.4 Ra’in Bincike
An ɗora wannan nazarin bisa Ra’in
bayani (descriptive theory). Na de Jump Mc Arthur (1992). Ra’i ne da yake
bayyana da kuma haskaka bincike.An zaɓi wannan ra’in ne domi bayyana
mutuwa a wasu waƙoƙin DR. Mamman Shata. Ra’in ya
fito da hoton Shata ƙarara a
duniyar harshe da adabi da kuma al’ada. Waɗanda suka ɗabakka Ra’in akwai Andrew Larry (2006).Shi ne Ra’in da
Babangida da Naseer da Ɗanja
(2021) suka yi amfani da shi. A nazarinsuna bayyana shirin game duniya a
harshen Hausa.
2.1 Tarihin Alhaji (DR) Mamman Shata
Katsina A Taƙaice
Ɗangambo,
(2013:4-15) cewa ya yi, “Kafin a nazarcikowane aiki na fasaha, waƙa ce ko labari, lallai ne a kawo
taƙaitaccen tarihin mawallafi.” An
haifi Alhaji (Dr.) Mamman Shata a garin Musawa ta jihar Katsina, a shekara
(1923) Shata ya yi sana’ar goro da alewa kafin ya fara waƙa saboda ƙiriniya irin ta yarinta, ba gada
ya yi a wurin iyayensa ba. Daga bisani Shata ya yi ƙaura da iyalansa zuwa birnin
Kano. Marigayin ya yi waƙoƙi[2]
da dama, wanda shi kansa bai san iya adadin waƙoƙin nasa
ba.
A lokacin mulkin soja na Janaral Yakubu Gawon, Shata ya samu
kyautar yabo a fagen waƙa,
kuma jami’ar Ahmadu Bello Zariya ta ba shi digirin girmamawa na (Dr.). Mawaƙin ya yi tafiye-tafiye a dalilin
sana’arsa ta waƙa.Ya
ziyarci ƙasashen
Afrika da ma ƙasashen
Yamma kamar Canada da Amurka da Birtaniya da Faransa da sauransu.Shata ya yi
harkar siyasa a rayuwarsa tun daga Jumhuriya ta farko. Ga misali ya yi NEPU[3] a
jumhuriya ta farko, ya yi GNPP a (1980) da kuma N.P.N. Ya taɓa rike miƙamin
kansila da kuma shugaban jam’iyar S.D.P na ƙaramar hukuma Kankiya ta jihar Katsina. Shata ya rasu a
shekarar (1999), an kuma binne shi a garin Daura kamar yadda ya bar wasiyya. Ya
bar mata uku waɗanda suka haɗa da Furera da Hadiza da Binta. Ya bar ‘ya’ya 19 da jikoki
28. Ya yi aure-aure da dama, wasu matan sun rabu ne, wasu kuwa mutuwa ce ta
raba su. Mahdi mai dogon zamani shi ne laƙabin
da ake yi wa Mamman Shata Katsina.
3.1
Ma’anar Waƙar Baka
Ƙamusun
Hausa, (2006:466) an bayyana waƙa
da cewa, “Wata tsararriyar magana da ake rerawa a kan kari ko rauji”.
Gusau, (2011:27) cewa ya yi waƙar baka fage ne wanda ake shirya maganganu na hikima, da ake
aiwatarwa a rera cikin rauji tsararre, haɗe da kiɗa cikin daidaita rerawa.
Sai dai Funtua, (2011:51) ƙarin haske ya yi inda yake cewa, tun fil’azal gargajiya ita
ce ta haifi waƙa da mawaƙan Hausa. Makaɗa sun tsira ne domin su raya al’adun al’umma.
Gusau, (2014:56) ya ƙara
da cewa, waƙar baka
wani zance ne shiryayye cikin hikima da azanci da yake zuwa bisa ƙa’ida da tsari da daidaituwa,
ana rera sautin murya da amsa amo na kari da kiɗa,
sau da yawa kuma tare da amshi. Shaihun malamin ya ci gaba da cewa, waƙa ta faru ne a wurin Hausawa tun
lokacin da suka fahimci farauta ta tudu da ta ruwa da kafa iyali a wuri guda.
Mashi, (1986) cewa ya yi waƙa haɗakar kalmomida kiɗa ne cikin wani tsari mai bayarda armashi ga mai sauraro, a
inda shi mai sauraron zai iya tantance wannan haɗaka
ta kiɗa da jerim kalmomi.
Shi kuwa Umar, (1980:34) ya tabbatar da waƙa tana zuwa ne a sigar
gunduwowin zantuka waɗanda ake ƙira baitoci ko ɗiyoyi kuma ake rerawa da wani irin sautin murya na musamman.
Sai dai Abba, da Zuladaini, (2000), sun bayyana waƙa da cewa, duk wata tsararriyar
magana cikin hikima da fasaha da aka ƙirƙira aka rera ta daki-daki tare
da taimakon amo; a wani lokaci kuma, ta kasance ɗauke
da wani salo na birgewa bisa wata ƙa’ida
ta musamman domin isar da saƙo.
Dukkan waɗannan ma’anonin an kawo su ne;
domin a ƙara
fahimtar me wannan takardar take nufi, kuma sun taimaka mini sosai a wajen gina
aikina.
A fahimtarmu waƙa
tana nufin shiryayyen zance mai ɗauke da hikimomi da azanci da
salo da kuma balagar magana. Furucin waƙa
ba kamar na magana ko karatun zube ba ne; ana furta ta ne cikin rerawa da zaƙin murya. A harshen Hausa ana
kallon waƙa ta
hanyoyi biyu, nafarko akwai waƙar
baka wadda ake rera ta ga jama’a ba tare da an rubuta ba. Hanya ta biyu kuma
ita ce, wadda ake rubatawa kafin a gabatar da ita ga masu sauraro. Masana da
manazarta ilimi a fannin waƙar
baka, sun bayyana asalin ta da ma’anarta ta fuskoki da dama.
3.2 Taƙaitaccen Tarihin Waƙar Baka
Kamar yadda Abba, da Zuladaini, (2000) suka bayyana asalin
waƙar baka yana ɗauke da ra’ayoyin masana daban-daban. Na farko akwai masu
cewa, waƙa ta samo
asali ne daga wurin wani bawan Allah mai suna “Sasana[4]”.
Shi wannan mutumin Sahabi ne wanda yake wa Annabi Muhammadu (S.A.W.) waƙa. Sun tabbatar da duk mawaƙan yanzu jikokinsa ne.
§
Ra’ayi na biyu shi ne waƙa ta
samo asali daga Daular Mali da kuma Songhai daga nan waƙa ta bazu ko’ina a faɗin duniya, har ya zuwa ƙasar
Hausa.
§
Ra’ayi na uku shi ne wanda
aka tabbatar cewa; waƙa da al’adar Bahaushe suna tafiya ne kafaɗa da kafaɗa. Ana ganin cewa,
yawace-yawacen farauta, da tsintar ‘ya’yan itatuwa da bautar iskoki da kirari
ga attajirai da jarumai da sarakuna su ne asalin waƙar baka a ƙasar
Hausa.
3.3 Mece ce Mutuwa?
Ƙamusun
Hausa, (2016:354) an bayyana ma’anar mutuwa da rasuwa ko ƙarshen ran mutum ko dabba ko duk
wani abu mai rai.
Shi kuwa Abraham, (1976:169) a cikin ƙamusun ɗin sacewa ya yi dakatawar duk wani abu mai rai ko mutum ko tsuntsaye
ko bishiyoyi.
Mutuwa[5] tana nufin
tsayuwar duk wani abu mai rai da nufin daina ko dakatar da aiki har a bada. Bunza,
(2013:19) ya tabbatar da cewa, mutuwa tana da sunayenta a Hausance tun kafin
zuwan Larabawa ko addinin Musulunci ƙasar
Hausa. Daga cikin sunayen nata akwai ɓingirewa da cikawa da shukawa da
kwanta dama da ƙarewa da
kaifaya da ƙarshe da
sauransu. Haka ma bayan zuwan Musulunci, Bahaushe ya sanya wa mutuwa sunaye
irin su wafati da faɗuwa da haura Gabas da wa’adi da
gabaci liman da Allah ya yi kira. Haka bayan zuwan Turawa ma Bahaushe yana da
sunayen da yake Ƙiran
mutuwa da su kamar ya shiga ambulan ya ja mayafinsa.
Bunza, (2013:425) ya ci gaba da cewa, mutuwa asalin kalmar
ba Bahaushiya ba ce. Aro ta aka yi daga harshen Larabci. Tana nufin tsayuwar
duk wani hanzari koaiki da mutum mai rai yake yi.
Bahaushe ya yi imani da mutuwa tun fil’azal. Ya yarda da
hanyoyi daban-daban da mutuwa takan riski mai rai. Ya ƙara kuma imani da cewa, mutuwa
tana iya ɗaukar mutum haka kawai ba tare
da wata rashin lafiya ba. Haka kuma ana mutuwa ta sanadiyar haɗari ko rashin lafiya ko fyaɗe
ko maita ko kambun baka da dai sauran hanyoyin mutuwa na gargajiya.Bunza,
(2013).
Bunza, (2013:447) ya ƙara
da cewa, idan muka yi waiwaye ra’in masana al’ada, za mu fahimci cewa, duk
fafitikar da masu rai ke yi a duniya, to mutuwa suke yi wa ita. Misali kamar yaƙe-yaƙe da noma da tafiye-tafiye da
kasuwanci da sauran hanyoyin inganta tattalin arziƙi duk tanadi ne na kariya ko ƙauracewa mutuwa. Domin tabbatar
da wannan lamarin na malam ga abin da Mahadi mai dogon zamani yake cewa:
Sannu da yaƙi,
Sannu da fama,
Sakkwato kyaftin.
(Shata waƙar
Muhd Sakkwato Kyaftin)
Waɗannan ɗiyanwaƙar
da Mamman Shata ya ambata suna ƙara
jaddada maganar Bunza, (2013:448), na cewa duk abin da mutum yake yi da shiga
da fice duk domin kare kansa ne daga mutuwa. Idan mutum ya yi sake ya tsaya; za
a iya cin sa da yaƙi[6]. Daga nan
kuma sai bauta sai mutuwa.
Kamar yadda aka faɗi a baya, waƙar baka nau’in waƙa ce da makaɗan Hausa ke yi dominisar da saƙo cikin rerawa da zaƙin
murya da rauji. Saƙon na iya
kasancewa ta hanyoyi daban-daban saboda haka; wannan takardar ta tsaya ne ga
ambaton mutuwa a cikin wasu waƙoƙin marigayi Alhaji (Dr.) Mamman
Shata Katsina.
Ga wasu misalai nan da aka zaƙulo masu ɗauke da mutuwa ko ta’aziya daga
wasu waƙoƙin Mamman Shata, kamar haka:
3.3.1
Dr. Mamman Shata Katsina ya yi wa marigayi Ciroman Gombe waƙar ta’aziyya. Ga abin da yake
cewa a cikin wasu ɗiyoyin waƙar:
Jagora: Kowa ya mutu bai yi
sauri ba,
Mu da muke ba mu daɗe ba,
Sai mun zo Ciroman Gombe,
Mutuwa ta min gaggawa ta,
ƊaukeCiroman
Gombe.
Amsh: Allah jiƙan
Ciroman Gombe.
(Shata: waƙar
Ciroman Gombe).
A wannan ɗiyoyin waƙar Shata ya nuna cewa; mutuwa ta
yi masa hanzari ta ɗauke Ciroma. Wannan ya tabbatar
da cewa, akwai ɓirɓishin
maguzanci cikin baitocin wannan waƙar.
Ga kuma ta’aziyya da aka bayyana kamar yadda Musulunci ya tanada.
3.3.2
A wata waƙarsa mai
taken Habibu Fari, mawaƙin
ya Ƙira mutuwa, duk domin isar da saƙo da gina tunaninsa ga masu
sauraro. Ga abin da yake cewa:
Jagora:Ya Allah don Rasulullahi
Don albarkar shaihunanka
Ya gafartawa Habibu fari.
Amsh: Allah ka jiƙan
Habibu Fari.
(Shata: waƙar
Habibu fari).
A waɗannan gunduwowin waƙar Mamman Shata ta’aziyya yake
yi ga waɗanda suka cika, kuma ya yi ta ne
kamar yadda addininsa ya tanada, ba kamar ta sama ba; da aka ci karo da ɓirɓishin maguzanci a cikin baitoci.
3.3.3
Haka a cikin waƙarsa da
ya yi mai taken “Duniya Labari.” Ga abin da yake cewa a cikin wasu ɗiyoyin waƙar
kamar haka:
Jagora: Ayyaraye duniya labari,
Ayyaraye duniya gishiri ce,
‘Yan yara ai sai mun ɗanɗana
Ta mu bar tawalau mun
Mace
Walau mun tsufa,
Amsh:
Ayyaraye duniya
labari.
(Shata: waƙar
duniya labari).
A wannan ɗiyoyin/gunduwowin waƙar, Mamman Shata yana faɗakar da al’umma cewar; mutuwa ta zama wajibi, duk inda mutum
ya kai ga bugun gaba, ko alfahari, ko taƙama,
ko milki ko ji da kai, dole sai ya mutu.
3.3.4
A cikin wata waƙarsa mai
suna “Wali”, mawaƙin ya
ambaci mutuwa a wasu ɗiyoyin/gunduwowin waƙar tasa, ga abin da Mahadin yake
cewa:
Jagora: Lamarin duniya shiga da fita
neHar in mun mutu sai labari,
Amsh:Wali ɗan Usmanu Salgare.
(Shata: waƙar
Wali)
A wannan ɗiyoyin/gunduwowin waƙar, Shata yana ƙara tunatarwa al’umma cewa,
tabbas duniya shigar shantun ƙadangare
ce, saboda haka, mawaƙin
yana jaddada lallai ko ana so ko ba a so mutuwa ta zama wajibi ga mai rai.
3.3.5
Ita ma waƙar da ya
yi wa Sardauna Shata ya tuna da mutuwa a cikin wasu gunduwowin waƙarsa kamar yadda yake cewa:
Jagora: Na san Kebbi don Ɗanhassan,
Na san Jega don Ɗanhassan,
Na son Kwantagora don Ɗanhassan
Albarkacinka duk na son su,
Allah jiƙan ka Baban Hassan,
Gama ranar tafiya lahira,
Ku tabbata babu zaman duniya.
Amshi:Sardauna bahago Ɗanhassan.
(Shata: waƙar
Sardauna)
A wannan gunduwowinin waƙar, Shata yana bayyana cewa, mutuwa tana cikin zukatan
mutane a kullum, alƙawarin
Ubangiji kuma ba ya tashi a kan mutuwa. Lallai mutuwa tazama dole ga dukkan
rayayye idan lokacinsa ya yi, babu jirkintawa, kuma babu dabara.
3.3.6
Akwai wata waƙar da shi
Mamman Shata Katsina ya yi wa wani bawan Allah mai suna Isyaku. Nan ma mawaƙin ya ambaci mutuwa a cikin waƙar kamar haka:
Jagora: Wo duniyar nan ba ta zama
ba ce,
Amshi:Isyaka ka dawo Lafiya.
(Shata: waƙar
Isyaku).
A waɗannan gunduwowin waƙar, mawaƙin ya ƙara fito wa ya jaddada wa mutane
cewa duniya fa barin ta dole ne, mutum ko yana so ko ba ya so dole sai ya mutu.
3.3.7
A cikin waƙar
“Ciroman Gombe” Shata ya ambaci mutuwa da nufin isar da saƙo ga masu sauraro. Ga abin da
Mahadin yake cewa:
Jagora: Da ni da Gombe sai wata rana,
Domin ba ciroman Gombe,
Shaida a mutanen Gombe,
Matanku zuwa ga mazanku,
‘Yan ƙanana zuwa ham manya,
Na ƙauye duk da na birni,
Ku da Alhaji sai wata rana.
‘Yan amshi: Allah ya jiƙan Ciroman Gombe.
A waɗannan gunduwowin waƙar, Shata ta’aziyya ya yi da
kuma bayyana yadda mutuwa take ɗaukar mutum; ko da ya kasance na
kirki ne a kowane lokaci, da kuma yadda take da ciwo da raɗaɗin a zukatan mutane. Mawaƙin ya nuna Ciroma a matsayin
mutumin kirki kuma adali.Wannan ya yi dai-dai da abin da Hausawa suke cewa, “rumfa
ta faɗi.” Idan wani mai taimakoko ɗaukar ɗawainiyar iyali ko al’umma a
kafaɗarsa; ya zama babu shiya mutu.
3.3.8
A waƙar malam Mustapha, likitan waƙar ya ambaci mutuwa a muryarsa,
duk domin gina tunaninsa ga masu sauraro kamar haka:
Jagora: Duk wanda yat taɓa Muɗɗaha,
Ɗan raka ko ya zage shi,
Babu dalili ‘Yan yara,
Ku yi masa duka har,
Ku kashe shi babu
shari’a,
Tun da ya zagi bawan Allah,
‘Yan
amshi: Malam Muɗɗaha ɗan raka.
(Shata: Waƙar
malam Mustapha).
A waɗanan gunduwowin waƙar shata ya nuna cewa, lallai
mutuwa tana afkawa mutum ba kawai ta hanyar rashin lafiya ba. A cikin ɗiyoyin waƙar
ta sama ya tabbatar da ana iya umarta a yi kisa bisa dalili na ta’addanci ko
ramuwar gayya ko ƙeta ko kuma
hukunci da bai kai ga kisa ba.
3.3.9
A cikin waƙarsa ta
“Mudi Ɗan Usmanu
Salgare” mawaƙin ya ƙara ambaton mutuwa a ƙoƙarinsa na gina tunaninsa, kamar yadda yake cewa:
Jagora:Baba ka kai ni ƙasashen Turai,
Tun ban tadda iyayena ba.
Mudi Ɗan
Usmanu Salgare.
‘Yan amshi:
(Shata: Waƙar
Mudi Ɗanusmanu Salgare)
Waɗannan ɗiyoyin waƙar
Shata yana faɗakar da mutane cewar, tabbas ɗan Adam yana da ƙuduri da yake buƙatar ya cimma a rayuwa, kafin
mutuwa ta riske shi. Lallai Shata ya ƙara
tabbatar da cewa, mutum yana da buri, kuma ya yi imani da mutuwa ta zama wajibi
a gare shi.Ya ɗauke ta tamkar jini da tsoka.
Shi ya sa yake cewa, “idan da rai da mutuwa.”
3.3.10
Haka a wata waƙarsa yana
ambaton mutuwa a cikin wasu ɗiyoyin waƙar, ga abin da mawaƙin yake cewa domin gina
tunaninsa:
Jagora:A da farko Mamman Shata,
Ka ga mutum komai nisa,
In na ganai zan gane shi,
Yanzun ba na ganewa,
Sai ya zo daidai gu na,
Kana sai in gane shi,
Daɗa
tsufa ya kama ni,
Nesa fa ta zo kusa kenan.
‘Yan amshi:Bawan Allah Mamman Ɗa.
(Shata: waƙar
Mamman Ɗa)
A cikin hoton waɗannan ɗiyoyin waƙar
ta sama. Shata yana tabbatar da cewa; lallai mutane sun yi imani da cewa, akwai
abubuwan da in suka bayyana gare su; to lallai mutuwa tana gab da ɗaukar su ko kuma suna kusa da mutuwa. Tabbas mutuwa ta
mamaye zukatan Bahushe ta kowane ɓangare.Lamarin zai ƙara tabbatar da mutuwa tana
cikin matakan rayuwar Bahuashe a jiya da yau da kuma gobe.
3.3.11 A
cikin waƙarsa ta
Amadun Gaya, a ƙoƙarin gina tunaninsa, mawaƙin ya ambaci mutuwa kamar yaddda
yake faɗi a wasu ɗiyoyin waƙar
kamar haka:
Jagora:Ga gawa nan babu mai
ita,
Ga ‘yan sanda za su bincike,
Mu mun bar shi wajen
Ba mu iske shi ba.
‘Yan amshi: Na gode Amadun Gaya.
(Shata: Waƙar
Amadun Gaya)
Shata a gunduwowin wannan waƙar, yana faɗakar da duniya; mutane sun saba
da mutuwa. Ba sa tsoran gawa, babban burinsu shi ne ɗaukar ta da gyara ta da kuma daraja ta zuwa makwancinta,
abin alfahari ne da gata a wurinsu. Idan aka duba hoton waɗannan ɗiyoyin waƙar cikin salon labari, za iya
jaddada mutuwa ta zamewa Bahushe tamkar shaƙar iska. A kulluyomin, yana tare da ita a zuciyarsa.
3.3.12
A waƙar “Gagarabadau”, mawaƙin ya ambaci mutuwa a wurin miƙar da tunaninsa a wasu ɗiyoyin waƙar
ga misali:
Jagora: Yara tsohonku zai mace,
Ba ku yanka ba tsohonku,
Tsohonku zai mace muku,
Mushe kuma ku yanka in,
Ba ku ci a gyara ma yara.
‘Yan amshi: Gagara badau namiji tsayayyen ɗan kasuwa.
(Shata: Waƙar
Gagarabadau)
A waɗannan ɗiyoyin waƙar,
cikin labari da rashin tausayawa. Mawaƙin
ya nuna wa duniya cewar; mutane ba su raga wa abokin gaba. Mutuwar abokin gaba
a wurin mutane, ba abin tayar da hankali ba ne. Wannan ya yi dai-dai da karin
maganar da Bahaushe yake cewa, “kyan abokin gaba mutuwa.”Saboda haka hoton
‘ya’yan waƙar, ya
bayyana mamaya da mutuwa ta yi wa duniyar Bahaushe. Kama daga kan falsafarsa da
dabaru da tausayi da ƙeta.
3.3.13
A cikin waƙarsa ta
“B.B. Faruƙu,” Shata
ya ambaci mutuwa a ƙoƙarin gina tunaninsa ga masu
sauraro. Ga misali:
Jagora: Ɗan tsakon da uwarsa ta kasa,
Allah ke ba shi abinci,
‘Yan amshi: B.B. Faruƙu
na Allah.
(Shata: waƙar
B.B.)
A cikin hoton wannan ɗiyan waƙar ta sama, Mamman Shata Katsina
ya bayyana yadda Bahaushe ya yarda da komai na Allah ne, musamman dangane da
abin da ya shafi mutuwa. Kuma Allah shi ne mai iko kan komai mai bayar wa ga
maraya, da kuma wanda ya so. Mutuwa kuma ta zama dole ga mai rai. Waɗannan ɗiyan waƙar sun fito da addinin Bahushe
da kuma yadda da ƙaddara da
jaddada mutuwa a duniyar falsafarsa da rayuwarsa duka.
3.3.14
Haka akwai wata waƙarsa da
ya gina tunaninsa a wasu baituka ta hanyar amfani da ambaton mutuwa kamar haka:
Jagora:Da gudu domin abokan gaba,
Malam Bello gwanda shahada,
‘Yan amshi :Malam Amadu Bello.
(Shata: waƙar
Amadu Bello)
Saƙon
da waɗannan gunduwowin waƙar suke isarwa cikin salo faɗakarwa ga jama’a, shi neduk da Bahaushe yayi imani da mutuwa
ba daɗi, da kuma tsoran ta, amma domin
ya ji kunya a idon duniya ko ragwanta, ko ƙasƙanci a wurin da bai dace ba, ya
gwammaci ya tunkari mutuwa gaba da gaba. Wannan ya nuna cewa, akwai lokacin da
mutum ko wani abu mai rai yake neman mutuwa da kansa. Hoton waƙar waƙar ya ƙara bayyana mutuwa na cikin
matakan rayuwar Bahaushe.
3.3.15 Mamman
Shata a wannan waƙar ta ƙasa, ya ambaci mutuwa kai tsaye
domin gina tunaninsa ga misali:
Jagora:Ban tuna komai ba baya Mamman,
Sai mutuwa sai tsufa na,
Amshi:Gode wa Mamman Ɗanmusa,
Mamman mai milkin Daurawa.
(Shata: Mamman mai milkin Daurawa)
A cikin ɗiyoyin wannan waƙa, Mamman Shata ya ambaci
mutuwa, saboda ya tabbatar da kullum tana ransa. Hoton waƙar cikin salon labara, maroƙin ya tabbatar wa masu sauraro
Bahaushe yana tsoron mutuwa a duniyarsa, saboda a duk wurin da ya tsinci kansa,
tana bibiyarsa, tamkar yadda yake shaƙar
limfashi, kuma ya ƙara fito
mana da bayani kan tsufa. Shata a cikin labara tsufa, wata sahihiyar hanya ceta
kusanci da mutuwa.
3.3.16 A
cikin waƙar Bashar
Ɗanmusa Shata ya ambaci mutuwa a ƙoƙarin gina tunaninsa. Ga misali:
Jagora: Sai mutuwa sai tsufa
Mamman,
Sai baɗi ran in ya kai,
‘Yan
amshi: Na gode
wa Bashir Ɗanmusa.
(Shata: waƙar
B. Ɗanmusa)
A cikin waɗannan gunduwowin waƙar tasa, Mamman Shata yana ƙara bayyana wa mutane cewar;
kowanne mutum a duk halin da yake ciki, to yana ƙoƙarin
kaucewa mutuwa, kuma kulluyomin mutum yana cikin tsoro da rashin tabbas da
fargabar mutuwa kafin ya kai ga cim ma burinsa. Tabbas tsufa wata hanya ce ta
kusantar mutuwa a kowane lokaci.
3.3.17
A cikin waƙarsa mai
taken “Hassan Sarkin Dogarai” mawaƙin
ya ƙara ambatar mutuwa a ƙoƙarin bayyana tunanisa. Ga abin da sarkin mawaƙan yake cewa:
Jagora: Tsaya komai za ka bawa,
Bawan sarki ga shi,
A nan ya maka godiya,
Kana taɓa sarki; ya sanya,
Damtse ya gama da kai.
‘Yan
amshi: Hassan
sarkin Dogarai.
(Shata: waƙar
Hassan sarkin dagarai)
A cikin waɗannan gunduwowin, Mamman Shata
ya nuna yadda sarki yake da mihimmanci a cikin al’ummarsa. Har ta kai da za su
iya yin kisa ko kashe mutumin da ya kawo wa sarkinsu wargi ko raini. Wannan ya ƙara fito mana da cewa, mutuwa
tana ɗaukar mutane ta hanyoyi da dama.
Kammalawa
Kamar yadda kowa ya sani ne, Alhaji Dr Mamman Shata Katsina
zakaran gwajin dafi ne a fagen waƙar
baka ta Hausa. Ya yi waƙoƙi masu tarin yawa, waɗanda Hausawa da dama da waɗanda
ba harshen Hausa ba ne ya haife su; za su iya cin karo da abin da ya shafi
rayuwarsu. Ga kuma abin rubutawa ko nazari a cikin waƙoƙin nasa. Mutuwa tana ɗaya daga cikin matakan rayuwar
Bahaushe, idan aka lura da waƙoƙin makaɗin, za a ga yadda yake jaddada kalaman mutuwa a cikin wasu ɗiyoyi waƙoƙin nasa; duk domin ya gina
tunaninsa da zai ɗauki hankalin mai sauraro.
Mamman Shata ya yi ta’aziyya, ya nuna jimamin mutuwa da ta’addanci da kuma
yadda take cin rai da rushewar al’amuran jama’a.
Manazarta
Abba, M. da Zuladayyani, B. (2000). Waƙoƙin Baka Na Hausa. Zariya: Gaskiya Coporation
Ltd.
Abraham, R. C. (2000). The
Dictionary of Hausa Language. Government Printing Press.
Abram A. H. (1953). The Mirror and the Lamp Orientation of
Romantic Theory. Oxford London: Oxford University Press.
Bunza, A. M. (2013). Death in Hausa Folkloric Perspective.
Being A Paper Presented at International Conference, in Honor of Professor
(Ambassador) Ɗandatti
Abdulƙadir OFR, Organized by Bayero
University. Pp1-19.
Bunza, A.M. (2013). Littafin Ruwan Bagaja A Ma’aunin Matakan
Rayuwar Bahaushe. In Humanities in
Sub-saharan World Ruwan Bagaja in Perspective. UNICAIRO/ UMYUK Special
Research in Humanities. Pp425-447.
Bunza, A. M. (2002). Rubutun
Hausa Yadda Yake da Yadda ake yin Sa. Ibrash Islamic Publications Centre
Limited. 31 Adelabu Street Surulere, Lagos.
CNHN. (2006). Ƙamusun.
Zariya: Ahmadu Bello University Press.
Ɗangambo,
A. (1990). Ɗaurayar Gadon Feɗe
Waƙa (Sabon Tsari). Kano: K. D. G.
Publishers.
Gusau, S. M. (2003). Jagoran
Nazarin Waƙar
Baka. Kano:
Benchmark Publishers Limited
Gusau, S. M. (2008). Waƙoƙin
Baka a Ƙasar Hausa:
Yanaye-yaneyensu da Sigoginsu. Benchmark Publishers Limited Kano Nijeriya.
Gusau, S. A. (2014). Waƙar Baka Bahaushiya (The Hausa Oral Song). Zariya:
N.N.P.C.
Hassan, S. (2013). Mutuntakar Abubakar Imam A Littafin Ruwan
Bagaja. Kundin Digiri Na Uku, Sashen Nazarin Harsunan Afrika. Jami’ar Ahmadu
Bello.
Mashi, M. B. (1986). Waƙoƙin Baka Na Siyasa. Kundin Digiri
na Biyu. Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sokoto.
Sarɓi, S.A. (2007). Nazarin Waƙe
Na Hausa.In Harsunan Nijeriya. Kano: Samarib
Publishers. Nijeriya.
Umar, M. B. (1980). Waƙoƙin Baka Madubin Rayuwar Al’umma.
Takardar Da Aka Gabatar A Taron Ƙarawa
Juna Ilimi Argungu COE, Palace.
Waƙoƙin Baka Na Hausa, (2011).
Department of Hausa Federal College of Education Katsina. Centuary Research and
Publishing Limited, Abuja Kano Kaduna Lagos Zariya.
Yakasai,
S. A. (2013). Jagoran Nazarin Walwalar
Harshe. Usmanu Ɗanfodiyo
University Sokoto, Nijeriya.
[1] . za a iya duba littafin Ruwab Bagaja
(1933) da Shaihu Umar (1933) da sauran waqoqin Hausa’ duk domin tabbatar da
yadda Bahaushe yake ganin mutuwa a al’adarsa.
[2]Jama’a da dama sun tabbatar da
cewa, baiwar da ta qara xaukaka darajar Mamman Shata a duniyar adabin Hausa ita
ce; yin waqa nan take ba sai ya shirya ba. Wasu daga cikin waqoqin da ya yi a
irin wannan yanayin sun haxa da waqar Canada center da Allah mai aradu mai
talata da Xanfulani da Dejin Ruhu da sauransu.
[3]Lokacin wannan siyasa an yi abubuwa
da dama a qasar nan tamu (Nijeriya) an yi waqe-waqe, an yi rikici da kashe-kashe.
An yi rabuwar dutsi hannun riga tsakanin masu mulki da talakawa da almajirai.
Domin qarin bayani za a iya duba aikin farfesa Ibrahim Malumfashi mai taken
Yankan Kunkurun Bala a Himma ta jami’ar Umar Musa ‘Yar adu’a Katsina.
[4]Domin tabbatar da maganar Sasana
uban mawaqan duniya gaba xaya ne, sai a saurari yadda Xanma’abban Shata yake
zuga sa yake ce masa “jikan Sasana”.
[5]Bunza, (2013:425-447) ya bayyana
cewa, matakan rayuwar Bahaushe ba su samu kulawar manazarta da xaliban Hausa
ba. Rashin kulawa da waiwayen matakan rayuwar mutane wajen nazarin adabinsu
kure ne babba.
[6]Yaqi yana xaya daga cikin abubuwa
na wahala da mutuwa da rushewar daula duk girmanta. Haka ya tava faruwa da
daular Romawa, suka bazu har ya zuwa qasar Hausa; duk dominneman mafaka don
tsirar da rayuwarsu. Duba Bunza (2002)
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.