SAƁANI TSAKANIN 'YAN FALSAFA DA MASU HANKALI A KAN ƊAUKAKAR ALLAH
Shi ya sa
magabata suka ce:
كل معطل مشبه
"Dukkan
Mai kore Siffofin Allah to Mai kamanta Allah da wani abu ne".
Ma'ana kafin ya kore Siffofin Allah sai da ya kamanta Allah da mutum, sai ya ga bai kamata haka ya kasance ba, sa'annan sai ya kore Siffofin, sai kuma ya afka cikin kamanta Allah da babu, ko kuma da abun da ba zai yiwu ba.
Saboda haka
wadannan 'Yan Falsafan da muke gani, kafin su kore daukakar Allah a saman
halitta sai da suka kamanta Allah da mutum, saboda su abin da tunaninsu ya ba
su shi ne; in an ce: Allah yana sama, kuma yana saukowa zuwa sama ta Duniya to
ai saman Nigeria ba ita ce saman KSA ba. Haka in an ce yana saukowa a kowane
dare to ai lokacin da 2/3 na dare ya yi a Nigeria to a America rana ce...
Haba Makaho
Dan Falsafa!
In ka fadi
haka, ai wannan kana misalta daukaka da sauka ne na mutane ba na Allah ba!
To wannan
tunani ne na mai karamin kwakwalwa, mai kuncin tunani, maras basira, mai
kwatanta daukakar Allah a sama da daukakar mutane a sama ko jirgi ko tsuntsu ko
sauran ababen halitta. Haka kuma yana kwatanta saukowar Allah daga sama da ta
mutane ko sauran halitta.
Ya Mai
kwatanta Allah da halitta!
Ya Mai
kwatanta Siffofin Allah da siffofin halitta!
Ya kamata ka
san cewa; Allah ba shi da makamanci.
{لَيْسَ كَمِثْلِهِ شَيْءٌ وَهُوَ السَّمِيعُ الْبَصِيرُ }
[الشورى: 11]
Da zarar ka
kamanta daukakarsa a sama da daukakar halitta, ka kwatanta saukowarsa daga sama
da saukar halitta, to ka kama hanyar bata, ka wayi gari "Mushabbihi"
(mai kamanta Allah da halitta), sai kuma ka afka cikin "Ta'atili" ka
zama mai kore ma Allah abin da ya tabbatar ma kansa na Daukaka a kan dukkan
halittu, da kore saukowarsa zuwa sama ta Duniya da ya tabbata ta harshen
Manzonsa.
Su abin da
wadannan jahilai masu wayo da kwazo marasa hankali suka manta shi ne; Ana iya
sanin abu ne ta hanyoyi guda uku:
1- Imma
saninsa ta hanyar hawas (gani ko ji...).
2- Ko ta
hanyar sanin makamancinsa.
3- Ko ta
hanyar ba da labari a kansa.
To Shi Allah
Madaukaki babu wanda ya taba ganinsa, ko ya san shi ta hanyar hawas.
Kuma ba shi
da makamanci, balle a ce an san shi da hankali ta hanyar sanin makamancinsa.
Don haka sai
dai a san shi ta hanyar Labarin da ya bayar cikin Littafinsa ko ta harshen
Manzonsa.
Saboda haka
ashe hanya daya ce kawai ta sanin Allah da Siffofinsa da sanin inda yake, ta
cikin Littafinsa da Hadisan Manzonsa, duk wanda ya karyata su ya kore siffofin
Allah da suka zo a cikinsu, ko ya yi tawilinsu to ya zama
"Mushabbihi", "Mu'attili", kuma "Muharrifi", wato
mai kamanta Allah da wani abu, kuma mai kore wa Allah Siffofinsa na kamala da
daukakarsa a saman dukkan halitta, kuma mai canza maganar Allah da karyata
hakikaninta.
Don haka mu
mun yarda Allah yana sama kamar yadda ya fada, ya daukaka a kan dukkan
halittunsa, kuma ya yi "Istiwa'i" a kan Al'arshinsa:
{الرَّحْمَنُ عَلَى الْعَرْشِ اسْتَوَى } [طه: 5]
Kuma yana
saukowa zuwa sama ta Duniya a kowane dare, kamar yadda Manzonsa ya fada, saboda
ba ya magana ta son rai, duk abin da ya fada Wahayi ne daga Allah.
Amma ba mu
san kamannin daukakar tasa da "Istiwa'in" nasa ba, saboda bai ba mu
labari ba, balle mu san cewa; za a samu matsala saboda saman Nigeria ba ita ce
saman KSA ba. Saman Argentina ba ita ce saman Australia ba.
Haka kuma ba
mu san kamannin saukowar tasa ba, balle mu san za a samu matsala a saukarsa a
cikin dare saboda lokacin da 2/3 na dare ya yi a Nigeria to a America rana ce.
Idan kuma 2/3 na daren America ya yi to na Austria ya fita. Idan na Austria ya
fita to na UK zai shiga!
Mu dai mun
san Allah Mai iko ne a kan komai, babu abin da zai gagare shi. Kuma daukakarsa
a saman halitta ba irin daukakar abin halitta ba ne, haka saukowarsa zuwa sama
ta Duniya ba irin sauka da abin halitta yake yi daga sama ba ne. Mu dai kawai
mun yi imani ne da gaibi, ba ma kutsawa yin bincike a kan gaibin, kamar yadda
Allah ya yabi Muminai inda ya ce:
{ الَّذِينَ يُؤْمِنُونَ بِالْغَيْبِ } [البقرة: 3]
Sabanin 'Yan
Falsafa masu inkarin gaibin, masu karyata Manzannin Allah, kamar yadda Imamul
Gazzaliy bayan ya gama karance Falsafar sai ya siffanta su da cewa:
وحكاية حاصل علومهم، فإني رأيتهم أصنافاً، ورأيت علومهم
أقساماً وهم - على كثرة أصنافهم - يلزمهم وصمة الكفر والإلحاد
المنقذ من الضلال (ص: 42)
"Labarin
Ilimin nasu kwacokom dinsa, na same su ne mabanbanta masu sabani, kuma na ga
Ilimin nasu a rarrabe yake cikin sabani, su kuma duk da yawan rarrabuwar tasu
amma SIFFAR KAFIRCI DA ILHADI TANA MANNE DA SU".
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.