Takarda Wadda aka Gabatar a Taron Ƙarawa Juna Sani na Ƙasa a kan Rayuwa da Gudummawar Sheikh Ahmad Sa’idu Maƙari a Sashen Fasaha da Nazarin Al'adu na Jami'ar Ahmadu Bello, Zariya Tare da Haɗin Guiwar Gidauniyar Ilimi ta TANMIYA Dake Nijeriya, Daga 29 ga Watan Janairu 2025 Zuwa 30 ga Watan Janairu 2025.
NAZARIN WAƘAR HATTARA 'YAN
SIYASA TA MALAM AHMAD MAƘARI
Daga
Musa Muhammad Labaran
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Bayero, Kano.
08161747863
muhammadmusalabaran@gmail.com
Da
Hifzullahi Ahmad Muhammad
Sashen Koyar da Kimiyar Harshe da Harsunan Ƙasashen
Waje
Jami’ar Bayero, Kano.
08133393733
hifzullahiahmad@gmail.com
Tsakure
Rubutattun waƙoƙin Hausa sun biyo
bayan zanguna aƙalla guda uku. Wato lokacin zuwan addinin Musulunci da
zuwan Turawa da kuma lokacin siyasa da sojoji. Wannan ya sa a farkon ƙarni na ashirin (Ƙ20) aka fara samun waƙoƙin siyasa masu jigogi
daban-daban. Kuma yawancinsu suna da zubi da tsari da salo da sarrafa harshe
irin na waƙoƙin ƙarni na goma sha tara (Ƙ19), wato lokacin
masu Jihadi. Wannan waƙa tana cikin waƙoƙin da aka rubuta a
cikin ƙarni na ashirin (Ƙ20). Babbar manufar
wannan bincike ita ce yin nazarin waƙar hattara ‘yan
siyasa domin fito da jigon da aka
gina waƙar a kansa tare da ƙananan jigogin waƙar da kuma zubi da tsari da salo da sarrafa harshe. An zaɓi mazahabar Ɗangambo (2007 da
2011) a matsayin ra’in da aka ɗora wannan takarda a kansa. An yi amfani da dabarar
bincike bi-bayani wajen yin sharhi da ƙalailaice saƙonnin da waƙar take ƙunshe da su da sauran
matakan nazari a matanonin waƙar. Binciken ya gano cewa, mulkin soja
shi ne ya fara haifar da ɓarna da rashin tsaro
da ake fama da shi a Nijeriya tun daga wancan lokaci, har ya yo naso izuwa
yanzu. Haka kuma, binciken ya gano cewa, adalci shi yake haifar da zaman lafiya
da kwanciyar hankali da yalwar arziƙi a tsakanin al’umma.
Amma duk lokacin da aka rasa adalci daga shugabanni, to duk wasu ƙofofin ɓarna sun buɗe.
Keɓaɓɓun Kalmomi: Nazari, Ahmad Maƙari, waƙa, siyasa, hattara.
1.1 Gabatarwa
Waƙoƙin Hausa Hausa sun
zama wasu mazubai waɗanda ake zuba saƙonni muhimmai na
gyaran hali ko faɗakarwa ko nusantarwa
da kuma adana tarihi domin hasko rayuwar magabata mai kyau domin a yi koyi da
su, da kuma saɓanin haka domin a
guje mata. Wannan ya sa waƙoƙin Hausa, musamman
rubutattu suke ƙunshe da jigogi daban-daban, ciki har da na siyasa da
tsarin mulki.
Tun lokacin da aka bawa Nijeriya 'yancin-kai
a shekarar 1960, akwai fararen hula da sojoji wadanda suka yi mulki a matakai
daban-daban. Waka Bahaushiya tana tafiya ne tare da al'adu da ɗabi'un Hausawa wadda
kuma ta ratsa zanguna aƙalla guda hudu. Wato lokacin zaman farko (lokacin
Maguzanci) da bayan zuwan addinin Musulunci da lokacin Turawa da Zamanin siyasa
da sojoji. Wannan dalili ya sa wannan waƙa ta keɓanci ambato a kan
yanayin yadda sojoji suka gudanar da mulki na ɓarna kuma ta yi kira ga 'yan siyasa a
kan su ƙauracewa irin ɗabi'u da halayen mulki irin na sojoji.
A wannan takarda, an yi nazarin wannan waƙa mai suna 'hattara
'yan siyasa' ta Sheikh Ahmad Maƙari, nazari na gaba ɗaya. An kawo ma'ana
da samuwar rubutacciyar waƙa ta Hausa. Haka kuma, an kawo tarihin
marubucin waƙar a taƙaice da salsalar waƙar da kuma shekarar
da aka rubuta Waƙar. Sannan an kawo ma'anar jigo da kuma bayanin jigon waƙar da zubi da tsari
da salo da sarrafa harshe na waƙar. A ƙarshe kuma aka kawo
kammalawa da manazarta.
An yi amfani da Mazahabar rubutacciyar waƙa ta Ɗangambo ( 2007 da
2011) a matsayin ra'in da aka dora wannan takarda a kansa. Kuma ra'i ne wanda
shimfiɗa wasu matakai na yadda
za a yi nazarin rubutacciyar waƙa ta Hausa.
1.2
Taƙairaccen Tarihin
Samuwar Rubutacciyar Waƙa a Ƙasar Hausa
Masana irin su Ɗangambo (1984) da Sa’id (1981)
da Yahaya (1979) da Gusau (2003) da (2008) da Auta (2017) sun tabbbatar da cewa
kafin zuwan addinin musulunci, Hausawa ba su da ilimin karatu da rubutu. Wannan
ya sa babu wata rubatacciyar waƙa da
Hausawa ke da ita kafin zuwan musulunci. Tun a wajejen ƙarni na (10) ne zuwa (11) ake zaton Musulunci ya fara zuwa ƙasar Hausa. Sai dai tarihi ya nuna cewa, Musulunci ya zo ƙasar Katsina ne a lokaci mulkin Muhammadu Korau 1320-1353. Sannan ya zo
Kano ne a lokacin mulkin Yaji Dantsamiya 1349 -1355. Bayan zuwan musulunci ne,
Hausawa suka duƙufa wajen koyon ilimin addini
da na Larabci. Bayan da suke sami ilimi addini da na Larabci, sai kuma suka
fara sarrafa harufan Larabci wajen rubuta harshensa da shi, wato ajami wanda da
shi ne aka fara rubuta rubutattun waƙoƙi na Hausa . Tarihi ya nuna
cewa, an fara samun rubutacciyar waƙar Hausa ne a ƙarni na (17). Wato a wannan
lokacin ne ake samu waƙar yaƙin Badar. Sai kuma a ƙarni na 18,
aka samu wasu malamai waɗanda suka rubuta waƙoƙi da dama, kamar Malam Shitu ɗan Abdurra’uf da
Malam Muhamamdu n a birnin Gwari. A ƙarni na 19 kuma aka sami bunƙasa da haɓakar rubutattun waƙoƙi. A sanadiyar Jihadin Shehu Usman Ɗanfodio. Shehu Usman ya rubuta waƙoƙi da dama tun kafin jihadi,
haka lokacin jihadi, sannan ya rubuta bayan jihadi. Sannan mabiyansa da
almajiransa ma sun rubuta waƙoƙi da yawan gaske. Kamar Abdullahi Ɗan Fodio da Nana Asma’u da Isan Kware da Muhammmad Bello da sauransu.
Rubutattun waƙoƙin Hausa sun bazu, sun
fantsama saƙo da loko na ƙasar Hausa, ta hanyar rerewa a masallatai da wuraren wa’azi da makaranta
da kuma wurin bara ga mabarata.
1.3 Ma’anar
Rubutacciyar Waƙa
Masana da manazarta irin su Yahaya (1984) da Ɗangambo (1981 da 1984
da 2007) da Umar (1982) duk sun bayyana ma’anar waƙa. Misali, Ɗangambo (2007) yana
cewa “Waƙa wani saƙo ne da aka gina shi kan tsararriyar ƙa’ida ta sauti, ɗango, rerawa, kari
(bahari), amsa–amo (kafiya), da sauran ƙa’idojin da suka
shafi daidata kalmomi, zaɓensu da amfani da su
cikin sigogin da ba lalle ne haka suke a maganar baka ba”.
Yahaya ((1984) na cewa “ Waƙa maganar hikima ce
da ake rerawa ba faɗa kurum ba, wanda ke
da wani saƙo da ke ƙunshe cikin wasu kalmomi zaɓaɓɓu, tsararru kuma
zaunannu.
Waɗannan kaɗan kenan daga masanan
da suka bayyana ma’anar rubutacciyar waƙa. Za a iya bayyana
rubutacciyar waƙa da cewa, waƙa wani azanci ne da
ake shirya shi tare da tsarawa bisa bin wasu keɓaɓɓun ƙa’idoji da sharaɗu domin isar da wani saƙo cikin ɗangwaye da baitoci ta amfani da hawa da saukar murya ko kari kuma a rera
ta.
1.4 Bayanan Sharar Fage
1.4.1
Taƙaitaccen Tarihin Marubuci
An haifi malam Ahmad
Sa'idu a 08-08-1947 a cikin garin Kusfa dake garin Zariya a Jihar Kaduna. Sunan
mahaifinsa malam Sa'idu ɗan malam Ahmad
Badikko. Asalinsu mutanen Ƙasar Libya ne wanda daga baya suka
koma ƙasar Morocco. Haka kuma, daga baya kakanninsa suka yiwo ƙaura zuwa ƙasar Katsina, wasu
kuma suka fantsama zuwa ƙasar Kano kamar zuriyar Sharif Hamza da sauransu. Daga
nan ne mahaifinsa malam Ahmad ya tafi izuwa garin Zariya neman ilimin addinin
Musulunci, inda a nan ne ya haɗu da manyan malamai na addinin Musulunci kuma ya karanta
Fannonin ilimin addinin Musulunci daban-daban a wurinsu. Wanda kuma a nan ne
aka haifi malam Ahmad Maƙari.
Zuriyar malam Ahmad
Maƙari
ta tuƙe har kan Annabi Sallallahu alaihi wa alihi wa sallam, ta
kan Sayyidi Hassan ɗan Aliyu ɗan Abu Ɗalibi ɗan Sayyida Faɗima 'yar Annabi
Muhammadu Sallallahu alaihi wa alihi wa sallam.
1.4.1.1 Neman
Iliminsa
Malam Ahmad Maƙari ya fara neman
Iliminsa ne tun yana da ƙananan shekaru a wajen mahaifinsa malam Sa'idu, har sai
da ya cika shekara talatin (30). Haka kuma, ya samu ilimai daban-daban a
Fannonin Musulunci da kuma harshen Larabci a wurin manyan malamai daban-daban
dake cikin garin Zariya.
A ƙoƙarinsa na ci gaba da
neman ilimi, ya shiga makarantar Shehu Tasi a shekarar 1957. Bayan wasu shekaru
kuma ya wuce izuwa Kwalejin Koyar da Malamai ta Larabci (ATC) dake Katsina a
shekarar 1973. A shekarar 1977ne malam ya samu shaidar daukar ɗalibi na karatun
Difloma a Sashen Koyar da Harshen Larabci da Addinin Musulunci dake Jami'ar
Ahmadu Bello Zariya. Sannan ya ƙara samun wata shaidar daukar karatun
na Difloma a kan harshen Hausa da Larabci da kuma addinin Musulunci a Jami'ar
Bayero dake Kano a 1981. Wanda kuma ya kammala digirinsa ne a Jami'ar ta Bayero
a shekarar 1986.
Malam Ahmad Maƙari malami ne da ya
shawara wajen bada gudummawa ga al'umma da koyarwa a matakan ilimi daban-daban.
Haka kuma, masani ne a kan fannoni ilimai na kimiyar harshe da rubutun waƙoƙi da sauransu. Haka
kuma, ya shawara wajen yin rubuce-rubuce a kan sha'anin addinin Musulunci kamar
ilimin matanin Hadisi da kimiyar Hadisi da ilimin zance da Aruli da sauransu.
Malam Ahmad Maƙari yana da ɗalibai masu yawa,
wasu daga cikinsu su ne:
Farfesa Arsalan
Muhammad, Sashen Koyar da Harkar Shari’a, Jami’ar Ahmadu Bello Zariya.
Farfesa Ibrahim Ahmad
Maƙari,
Limamin Masallacin Ƙasa dake Abuja.
Farfesa Yahuza
Suleman, Shugaban NBAIS
Farfesa Nasiru M.
Ibrahim, Sashen Koyar da Harshen Larabci, Jami’ar Jihar Kaduna.
Farfesa Mustapha
Yusuf, Sashen Koyar da Harshen Larabci, Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’aduwa Jihar
Katsina.
Alhaji Jafar Miftahu
Yahaya CEO, Alaƙat Construction and Property Deɓelopment.
Justice A.S Yarima,
Kadi, Shari’a Court of Appeal
Justice Mahadi
Muhammad Siraj, Kadi Shari’a Court of Appeal Kaduna.
Da sauransu.
1.4.2 Salsalar Waƙar
An samu wannan waƙa ce a cikin kundin
waƙoƙin Sheikh Ahmad Maƙari, wanda kundi ne
wanda ya ƙunshi waƙoƙinsa waɗanda ya rubuta da
harshen Larabci da kuma harshen Hausa. Haka kuma, an samu wannan kundi ne ta
hannun malam Dayyib.
1.4.3
Shekarar da aka Rubuta Waƙar
Wannan waƙa, waƙa ce wadda aka rubuta
ta a shekarar 1990. Wato a lokacin da sojoji suke ƙoƙarin miƙa mulki ga farar hula
kafin kuma daga bisani su sake ɗanewa kan karagar mulkin. Wato ita wannan waƙa babu ramzi a
cikinta na shekarar da aka rubuta, mawallafin ya bayyana shekarar da ya rubuta
ta ƙarara
a ƙasan
takardar da aka buga waƙar a ciki.
2.1 Jigo
Masana masu yawa sun
bayyana ma’anar jigo a fannin nazarin adabin Hausa. Daga cikinsu akwai Gusau
(1983) da Ɗangambo (2007 da 2008) da Mukhtar (1984) da Buhari (1988)
da ‘Yar’aduwa (1999) da Chamo (2011) da Halima, Ɗangambo (2012) da
Labaran (2024) da sauransu. Labaran (2024) yana cewa, “ jigo shi ne saƙon da mawallafi ya
gina waƙarsa a kansa kuma yake burin isar da shi ga waɗanda (wanda) abin ya
shafa”. Wato jigo shi ne haƙiƙanin manufa wanda ta
sanya marubuci ya rubuta waƙarsa domin isar da saƙon dake cikin waƙar ga al’umma ko waɗanda abin ya shafa
kai tsaye.
Babban jigon wannan
waƙa
mai suna ‘Hattara ‘yan Siyasa’ shi ne illar ‘mulkin Soja’.
2.1.1 Furucin Gundarin Jigo a Waƙar
Hattara ‘Yan Siyasa
Furucin gunfarin jigo
na nufin muhalli na farko da mawaƙi ya fara bayyana
jigon waƙarsa a cikin wani baiti ko ɗango. Wato wuri ne wanda mawallafi ya
fara ambaton ainihin gundarin saƙon da yake so ya isar
ga jama’a. Ɗangambo (2007) yana cewa “ jawabin jigo, ƙwayar jigo ce da ke
iya samu ƙunshe cikin wasu baitoci da ke nuna tabbacin manufar
mawallafin…” mawaƙa kan iya iya ambaton gundarin saƙon waƙoƙinsu tun a farkon waƙar, wasu kuma sai a
tsakiyar waƙar. Sai dai akan samu wasu daga cikin mawaƙa da kan yi amafni da
hikima wajen ɓoye manufar da suke
son isarwa. Wato ba sa fitowa ƙarara su nuna saƙon da waƙar take ƙunshe da su. Ga mai
nazari, idan aka samu waƙa mai irin haka, zai bi waƙar ne lungu-lungu ya
tattaro dukkan wasu saƙonni waɗanda za su iya bada haske a kan gundarin saƙon waƙar, sannan ya bayyana
jigon waƙar.
Wannan waƙa ba a bayyana
gundarin jigonta ba ƙarara, hasalima sai a tsakiyar waƙar muwallafin ya
bayyana jigon waƙar a cikin wasu baitoci. Ga muhallan da aka bayyana
gundarin jigon waƙar a ƙasa:
Mun sha wuya mun
farace lokacin Soja,
Allah ya sa kar a
maimaito irin na jiya.
In munka sake shiga
ni-‘yasu sai saura,
Ya taho ya wargaza
tsarin nan na Tarayya.
(Baiti na 39-40)
Allah ka sa mun yi
ban-kwana da sojoji,
Sai dai mu gan su a
Bariki banda kan hanya.
(Baiti na 58)
Sun ɓata tsari na kirki
wanda sunka taras,
Sun sace ɗimbin kuɗi sun kai gurin
ajiya.
(Baiti na 3)
Idan aka lura, za a
ga a cikin waɗannan baitoci na
39-40 da 58 da kuma na 3 muwallafin ya bayyana dalilin rubuta waƙarsa. Wato yana
bayyana irin illa da ɓarnar da mulkin soja
ya yi a Nijeriya har ta kai yana addu’ar kada Allah ya dawo da mulkin Soja.
Haka kuma, yake yin kira ga ‘yan siyasa kada su bi sahun irin yadda Sojoji suka
yi mulkin zalunci da ɓata ƙasa a Nijeriya idan
sun karɓi mulki. Kar ku ma su
yi abin da har Soja zai ƙara yin sha’war dawowa mulkin Nijeriya, domin kuwa idan
suka sake dawowa, to sai sun ruguza ƙasar baki ɗayanta saboda ɓarnar da za su ci
gaba da yi.
Idan aka karanta waƙar, za a ga ya kawo
wasu miyagun laifuka da ɓarnace-ɓarnace aƙalla guda 10 waɗanda aka fare su ko
aka yawaita aikata su a lokacin mulkin Soja saboda irin zaluncin da suke yi wa
al’umma da sakaci da kuma karya tattalin arziƙin ƙasa da sace kuɗin al’umma kuma suka
bar su cikin yunwa da fatara.
Bayan wannan babban
jigo na ‘illar mulkin Soja’, akwai kuma ƙananan jigogi waɗanda aka yi amfani da
su wajen gina babban jigon waƙar. Wato akwai jigon nasiha da wa’azi
da ta’aziya da gargaɗi da janhankali da
sauransu.
2.1.2 Jigo a Gajarce
Wannan wata dabara ce
ta taƙaita abubuwan da aka faɗa cikin waƙa domin fayyace
manufofin da waƙar ke ɗauke da su. Ɗangambo (2007) ya faɗa cewa “ a nan, za a
bi waƙar ne a taƙaice, ana taƙaita baiti bayan
baiti. Za a yi hakan ne ba tare da bayyana ra’ayi, sharhi ko wani dogon bayani
ba”. A taƙaice, wannan wata dabara ce da ake yi domin taƙaice duk abin da waƙa ta ƙunsa dangane da
manufofi bisa tsarin jadawali wanda zai ƙara haskawa ko fitowa
da mai karatu dukkanin saƙonnin da waƙar ke ƙunshe da su, a taƙaice.
A wajen gajarta jigo,
ana dubawa a ga cewa shin waƙar tana da jerin tunani, ko kuma an yi
tafiyar kura a cikinta wajen ƙuƙƙula saƙonninta.
Wannan waƙa ta ‘Hattara ‘yan
Siyasa’ ba ta da jerin tunani, wannan ya sa aka taƙaita jigonta ta
amfani da hanyar taƙaita jigo ta biyu, waro kamar haka:
1.Kira ga ‘yan siyasa
a kan daina murna domin za su hau mulkin Nijeriya, domin Sojojin sun ɓata ƙasar, sun bar musu
babban aiki na gyara: baiti na 1, 2, 7.
2.Furucin gundarin
jigo: baiti na 3, 39-40, 58.
3.Bayyana makircin
sojoji domin idan sun miƙa mulki ga farar hula, daga baya kuma su ƙara dawowa su ce ai
farar hula sun gaza. Saboda daman sun san sun ɓata ƙasar, farar hula ba
za su iya gyara ta ba: baiti na 4.8.
Bayyana irin abubuwan
da mulkin Soja ya haifar na ɓarna a Nijeriya kamar fashi da makami da yankan-kai da ƙungiyoyin asiri da
masu hana haƙar man fetur (Ogani) da rikicin manoma da makiyaya da
fataucin miyagun ƙwayoyi da damfara ta 419 da rikicin Bukasi da kuma
ayyukan Shi’a: baiti na 8-17,19,28.
4.Bayyana irin yadda
mulkin Soja ya ɓata tattalin arziƙin ƙasa wanda hakan ya
haifar da tsadar takin noma da ƙarancin man fetur da ɓata tsarin masarautin
gargajiya da karya darajar naira da ciyon bashisshika da sauransu: baiti na
20,23,27.
5.Magana a kan yadda
mulkin Soja ya lalata harkar ilimi a Nijeriya har ta kai ana samun yawaitar
yajin-aiki na malamai da sauran ma’aikatan Gwamnati. Haka kuma, da amfani da
takardun bogi: baiti na 24,26,30.
6.Bayyana yanayin
yadda mulkin Soja ya yi sanadiyar samuwar cin hanci da rashawa: baiti na 25.
7.Bayyana yadda
Gwamnatin Soja ta sace kuɗaɗen ƙasa suka kai su ƙasar waje: baiti na
31
8.Yin nasiha ga ‘yan
siyasa a kan su tsaya su yi abin da ya dace idan sun karɓi mulkin Nijeriya:
baiti na 33-36,40-41.
9.Bayyana halin ‘yan
siyasa na son zuciya da sace kuɗin talakawa: baiti na 43-47,52.
10.Tona asirin ƙasashen Turai na irin
yaudararsu a kan ƙananan ƙasashe ta fuskar taimako kuma su sace
dukkanin dukiyarsu: baiti na 48-51,53-55.
11.Yin addu’a ga ƙasa da ‘yan
ƙasa
a kan halin da ake ciki da kuma yin neman afuwa da gafara a kan waɗanda suka mutu
(Musulmai) a sanadin halin da ƙasa ta shiga: baiti na 56-60.
12.Baitin ƙarshe da yin nasiha
ga waɗanda ya rubuta waƙar domin su, a kan su
yi amfani da nasihar: baiti na 61.
2.1.3 Warwarar Jigo
Wannan waƙa an gina jigonta a
kan faɗakar da wani rukunin
al'umma, wato 'yan Siyasa a kan irin illar da mulkin sojoji ya yi a ƙasa Nijeriya a lokuta
mabambanta. Wato Waƙar ta yi kira a kan idan mulki ya dawo hannun farar hula,
su dauri su kyautata wa al'umma kuma su yi aiki tuƙuru domin ciyar da ƙasa gaba. Wannan ne
kawai zai sa Soja ya kasa ƙara dawowa kan karagar mulkin Nijeriya
ballanta har ya sake yin irin ɓarnar da ya yi a baya. Idan ka dubi wannan baitin dake ƙasa za a ga yana
cewa:
Mun sha wuya mun
farace lokacin Soja,
Allah ya sa kar a
maimaito irin na jiya.
Sojoji sun yi mulki a
lokuta daban-daban kusan sau shi da ko bakwai a cikin cikakken juyij mulki guda
biyar. A 15-01-1966 wasu matasan sojoji suka yi juyin-mulki inda a lokacin ne
aka kashe wasu manyan Arewa, ciki har da Tabawa Ɓalewa da Ahmadu Bello
da wasu daga manyan Kudu kamar irin su Akintola da sauransu. Haka kuma, suka ɗora Johnson Aguiyi
Ironsu a matsayin shugaban kasar Nijeriya na Soja. Tun wannan lokaci ne aka
fara samun ɓarna a Nijeriya da
zalunci da ƙudurce ramuwa da ta-zaunar-tsaye musamman a kan abin da
ya shafi shugabanci. Kashe su Sardauna ya yi wa mutanen Arewa ciyo sosai,
wannan ya sa suka shirya juyin mulki na ramawa, wato Soja ya ƙwaci mulki a hannun
dan'uwansa soja ta ƙarfin tuwo. Wato a 26-07-1966 ne sojoji suka ƙwaci mulki a hannun
dan'uwansu Ironso inda kuma suka ɗora sabon shugaba wato Yakubu Gawon.
Bayan da ƙasa ta koma hannun
sojoji sai abubuwa suka taɓarɓare, ƙasa ta fara lalacewa,
wannan ya sa wasu gungun sojoji suka yi sanarwar juyin mulki a 29-07-1975 a
lakacin da Yakubu Gawon ya tafi taron haɗa kan Afirka wanda aka yi a Kammala. Wanda
daga nan ne suka ɗora Birgediya Murtala
Muhammad. Sai kuma a 13-02-1976 aka ƙaƙarin juyin mulki har
aka kashe Shugaban Ƙasa Murtala Muhammad amma wannan juyin mulki bai yi
tasiri ba. Wannan ya sa mataimakinsa Olusegub Obasanjo ya ɗare kujerar ya ci
gaba da tafiyar da ita har zuwa wani lokaci. Bayan wannan, sojoji sun yanke
shawarar mayar da mulki ga farar hula wanda a ƙarshe aka yi zaɓe, kuma shugaban Ƙasa Shehu Shagari ya
samu nasara. Amma a 31--12-1983 wasu sojoji suka ƙara yin yujin mulki
inda suka ɗora shugaban ƙasa Muhammadu Buhari.
A lokacin Buhari,
yunwa ta yawaita da yajin aiki daga malamai da ma'aika da karya 'yan kasuwa da
rigingimu da ƙungiyoyin lauyoyi da ta'addanci irin na su Maitatsine a
Kano da sauran abubuwan ɓarna da suka cika
Nijeriya. Wadannan dalilai suka sa Ibrahim Badamasi Babangida ya yi wa
Muhammadu Buhari juyin a mulki a 27-08-1985.
A lokacin da
Babangida ya hau kan mulki an yi amfani da kuɗaɗen ƙasa wajen yin wasu
aikace-aikace na raya ƙasa na manyan ayyuka. Amma kuma a lokacin ne Nijeriya ta
samu kanta a yanayin da bata taɓa zata ba na lalacewa da taɓarɓarewar al'amura. Tun daga wancan lokaci
abubuwa ƙara gaba suke yi na lalacewar ƙasar har zuwa yanzu.
Wannan ya faru ne kuwa saboda irin mulkin da sojojin wannan lokaci suka yi,
inda har ta kai an hofantar da ɓangaren noma aka dogara kawai a kan ɗanyen man fetur, kuma
a ƙarshe
man taƙi samuwa ga 'yan ƙasa, wannan ya sa aka
fara samun rashin tsayayyen farashi. Haka kuma, duk wani ɓangare da ake samun
kuɗin shiga, sai da suka
hofantar da shi, suka koma kan man fetur kawai. Wannan shi ne ya yi sanadiyar
mutuwar noma a yankin Arewa. Sannan, aka ciyo manyan basussuka daga ƙasasehn waje da karya
darajar naira, wato dai mulki Babu ƙwarewa wajen tafiyar
da shi. Wannan ya sa talauci da yunwa suka ƙaru a ƙasar da ayyukan
ta'addanci da cin zarafin ƙananan mutane da yawaita da yaɗuwar cututtuka da taɓarɓarewar harkar ilimi
da kwararowar 'yan ƙauye cikin birane saboda rashin abubuwan more rayuwa da
talauci da kuma yunwa. Wannan ya sa malam yake cewa,
Sun ɓata tsari na kirki
wanda sunka taras.
Wato kafin zuwan
mulkin sojoji a 1966, Nijeriya ba ta fuskantar dukkanin irin waɗannan matsaloli. Wato
wannan tsari na sojoji shi ne silar haifar da talauci a Nijeriya wanda har ya
yi sanadiyar samar da wasu ayyukan ta'addanci da ɓarna. Wannan ya sa za a ga malam yana
cewa,
Ga 'yan fashi da
makami kowane hanya,
Da dare da rana suna
ta fashi ga mai tafiya.
Sabon salon damfara
sunarsa 419,
Ya zam ruwan dare ya
game ko wane shiyya.
'Yan ƙungiya na asiri masu
yankan kai,
Sun kasa yin
maganinsu bare farin kaya.
Wato yunwa da talauci
da mulkin sojoji suka haifar a wancan lokaci ya sa kowa ya nema wa kansa mafita
domin ya rayu, wasu ta hanya mai kyau wasu kuma ta hanya marar kyau kamar dai yadda
malam ya ambata a cikin waɗannan baitoci dake sama.
A shekarar da aka
rubuta wannan waƙa ce, wato 1990 aka shirya yi wa shugaban ƙasa na Soja wato
Babangida juyin mulki amma ba a samu nasara ba. Bayan wani lokacin 'yan siyasa
da manyan ƙasa suka matsawa shugaban ƙasa lamba a kan a
dawo mulkin farar hula saboda taɓarɓarewar da ƙasa ta yi a lokacin.
Wannan dalili ya sa Babangida ya yi murabus daga kujerar shugaban ƙasa, kuma ya ba wa
Ernest Shonekan shugabancin Nijeriya na riƙon ƙwarya kafin a yi zaɓe a 26-08-1993. Amma
Shonekan watanni uku kawai ya yi a kan mulki Janar Abacha ya yi masa juyin
mulki a 17-11-1993.
Bayan rasuwar Janar
Sani Abacha a shekarar 1998, aka yi zaɓe a 1999 inda daga nan har zuwa yau ake
gudanar da mulkin Nijeriya a kan tsarin mulkin farar hula. A lokacin da Janar
Babangida yake ƙoƙarin miƙa mulki ga farar hula, malam ya yi
kira ga 'yan siyasa a kan kada su yarda su bi irin tsarin mulkin sojoji na ɓata ƙasa da cin hanci da ɓarna idan sun karɓi mulki, shi ne malam
yake cewa,
In Kun ci sa'a ku Kai
aiki na san barka,
Naijeriya za ta
dawwama Babu jayayya.
In kun bi tsari na
'yan jarinka ne hujja,
Kuka sake tatse Ƙasarku za ku sha
kunya.
Amma duk da wannan faɗakarwa da jan hankali
da aka yi wa 'yan Siyasa, amma sai da suka dinga yin ɓarnar da har 'yan ƙasa suna buri da
kiraye-kiraye ga sojoji domin su yi juyin mulki su karɓi ƙasar. Lalle idan mai
karatu yay i la’akari da abubuwan da aka ambata na ɓarna da sojoji suka
yi lokacin da suke mulki da kuma irin kiraye-kirayen da 'yan ƙasa suke yi a yau, to
za a gane cewa, 'yan Nijeriya suna cikin wani matsananci hali wanda ya fi na
sojoji masifa a gare su. Abin da ya koro ɓera daga rami zuwa wuta, ya fi wutar zafi,
inji Hausawa.
Shugabanin siyasa na Nijeriya
aa yau, sun miƙa wulayarsu duka ga Turawa, wannan ya sa suka haɗa kai da su wajen
cutar da al'ummar ƙasa ta fuskoki daban-daban. Idan aka duba za a ga malam
ya yi kira ga 'yan siyasa cewa kada su aminta da Turawa a matsayin waɗanda za a riƙa domin kawo taimako.
Za a ga yana cewa,
Manyan ƙasashe dake cewa suna
yaƙi,
Domin su 'yanto ƙasashe wanda ke baya.
Ƙaryar tsiya, marasa tausai
da imani,
Waɗanda kan sa ruwan
bashi a kasa biya.
Gidanmu na kan tudu su
sun yi nasu kwari,
Komi ya kucce a gunmu
gare su za ya tsaya.
Idan aka dubi waɗannan abubuwa da
malam ya faɗa tun a wancan
lokaci, su ne suke faruwa a yanzu kwabo da kwabo kuma su ne suka saka ɗan ƙasa a halin da yake
ciki a yanzu na yunwa da talauci da cuta da ta'addanci da zalunci da damfara da
sata da mace-mace a sanadiyar yunwa, har ta kai ɗan ƙasa ba ya iya cin
abinci sau biyu a rana. An taɓarɓa harkar ilimi da
kasuwanci da noma da sana'o'i dama tattalin arziƙin gaba ɗaya. 'Yan siyasa sun ɓata Nijeriya sama da
yadda sojoji suka ɓata ta sau ninki ɗari. Allah ya gyara
mu ya kuma gyara ƙasarmu, amin.
3.1 Zubi da Tsarin Waƙar Hattara ‘yan
Siyasa
3.1.1 Zubi da Tsari na Gaba Ɗaya
Wannan waƙa mai suna ‘hattara
‘yan siyasa’, marubucin ya jeranta saƙonnin cikinta ta
yadda mai karatu zai kai ga inda ake so ya kai, kai tsaye ba tare da ya sha
wuya ba. Haka kuma, ya yi amfani da kalmomi masu makusanciyar ma’ana da juna da
jumloli dogaye da kalmomin fannu da tsofaffi da sauransu.
Wannan waƙa, waƙa ce wadda take ɗauke da baitoci
sittin da ɗaya (61). Haka kuma,
tana da ɗangwaye bibbiyu, wato
waƙa
ce ‘yar tagwai. Tana kuma da ƙafiya guda biyu. Wato babba da ƙarama. Babban ƙafiyar waƙar ita ce, ‘ya’. Wato
waƙar
‘yayiya’ ce. Sannan tana da ƙananan ƙafiya mai sauyawa a
cikin kowane baiti. Waƙar ta ƙunshi ƙananan ƙafiyoyi na ki, ri, ras, wa, ko, ka, na, ya, sa, kai, a,
ma, wo, to, ra, su, ba, ta, ƙi, ne, sur, mu, ci, ni, ja, mi, she, da, ce da kuma
do. Amma kuma ba ta da mabuɗi da marufi.
3.1.1.1 Gangara
A cikin wannan waƙa akwai baitoci inda
aka samu gangara a cikinsu. Wato saƙonni da aka ƙullo a cikin ɗango na farko, ba a
cika ma’anarsa ba sai a cikin ɗangon da yake biye da shi. Ga misalan wasu baitoci da
suke ƙunshe da wannan dabara ta gangara:
Sabon Salon damfara
sunarsa (419).
A wannan ɗango, mawallafin ya
fara bayanin wata sabuwar damfara da ta shigo Nijeriya. Saboda haka, da za a
bar wannan ɗango a haka,
ma’anarsa ba ta cika ba saboda ana buƙatar a ji menene
dalilin ambatar sunan damfarar? Wannan ya sa sai a ɗango na biyu ya
bayyana dalilin faro ma’anar a ɗango na ɗaya, inda yake cewa:
Ya zam ruwan dare ya
game kowane shiyyya.
Za a ga cikin wannan ɗangon aka cika
ma’anar ɗango na ɗaya. Haka nan, a
baiti na 38 an ƙara samun iirn wannan gangara, inda yake cewa:
Mulki idan dai da
zalunci yake tafiya.
A wannan ɗango, ya fara bayanin
halin da mulki da zalunci yake kasancewa, amma bai cika ma’anarsa ba sai a ɗango na biyu, inda
yake cewa:
Allahu ba ya bari
nasa kun ga kau aya.
Ma’ana, idan ana
mulki na zalunci, Allah ba ya barin sa. Ashe kenan, a ɗango na ɗaya ya fara furta
ma’anar sannan sai ya ƙarasa iyar da ma’anar a ɗango biyu.
An samu gangara da
yawa a cikin wannan waƙa kamar a baiti na 10, 13, 16, 17, 38, 40, 60 da kuma 61.
3.2.1.2 Saɓi-Zarce
A cikin wannan waƙa, a wuri ɗaya ne kawai aka samu
saɓi-zarce. Wato
tsakanin baiti na 15 zuwa na 16. Marubucin ya fara saƙa wata ma’ana a cikin
baiti na goma sha biyar (15) amma bai ƙarasa ba sai a cikin
baiti na goma sha shida (16). Ga waɗannan baitoci a nan ƙasa:
Kuma ga shi mu da maƙota ‘yan’uwan juna,
A Bukasi an jibge
sojoji ana niyya.
(Baiti na 15).
Sai an zubar da jinin
juna sabo da zato,
Wai yankunan na da ɗimbin mai da za a
siya.
(Baiti na 15).
Idan aka kalli waɗannan baitoci za a ga
cewa, mawallafin ya fara shirya wata ma’ana ce a cikin baiti na goma sha biyar
(15), wato bayani a kan faɗan yankina Bakasi da ake ƙoƙarin yi a tsakanin ƙasar Nijeriya da kuma
Kamaru. Amma bai cika ma’anar da ya faro ba sai da ya tsallaka izuwa baiti na
goma sha shida (16).
4.1 Salo da Sarrafa Harshe a Waƙar
Hattara ‘yan Siyasa
4.1.1 Salo
Salo zaɓi ne ko wani ‘yanci
da marubuci yake da shi wajen yin amfani da wasu ayyanannun dabaru ko hanyoyin
domin sarrafa kalmomi da jumlolin da ya yi amfani da su wajen shirya waƙarsa. Ɗangambo (2007) ya
bayyana salo da cewa, “ salo wani yanayi ne da ya ƙunshi zaɓi cikin rubutu ko
furuci. Wannan yana nufin yin amfani da wata kalma, lafazi, yanayi, hanya ko
tunani a maimakon wani”.
Akwai ire-iren salo
wanda ya haɗa da miƙaƙƙen salo da lamin salo
da salo mai kashe jiki da salo mai karsashi da tsohon salo da sauransu.
Wannan waƙa marubucinta ya yi
amfani da miƙaƙƙen salo wajen isar da saƙon da waƙar take ƙunshe da shi. Wato ya
yi amfani da yanayin saƙa jumlolin waƙar cikin yanayi mai
sauƙi
ta yadda duk wanda ya karanta zai gane abin da ake nufi. Ga wani misalin baiti
a ƙasa:
Rikicin tsakanin
manoma su da mai kiwo,
Ɓarna suke yin ma juna
ba batun diyya.
Idan aka karanta
wannan baiti, za a ga yana da sauƙin ganewa a kan abin
da yake magana, wato yanayin yadda ake samun rigingimu tsakanin manoma da
makiyaya, har ta kai da ana salwantar da rayuka. To, dukkanin ragowar baitocin
waƙar
a haka ya tsara su cikin wannan salo mai sauƙi kuma miƙaƙƙe.
3.1.1.1 Dabarun Jawo Hankali
Dabarun jawo hankali
wani salo da marubuta suke amfani da shi wajen kwatanta abubuwa biyu ko sama da
haka ta fuskar yanayi ko kuma tasiri. Akwai dabarun jawo hankali na kamantawa
na daidaito da fififko da gazawa da sauransu.
Marubucin wannan waƙa ya yi amfani da
dabarun jawo hankali na kamantawa ta daidaito a cikin baiti na 39 da kuma 46.
Ga yadda baitocin suke a ƙasa:
Mun sha wuya mun
farace lokacin soja,
Allah ya sa kar a
maimaito irin na jiya.
(Baiti na 39).
Idan aka dubi ɗango na biyu na
wannan baiti, kalma ta biyun ƙarshe, ya yi amfani da dabarar jawo
hankali ta kwatanci na daidaito. Wato ya yi ƙoƙarin kwatanta mulkin
soja wanda ya wuce da kuma mulkin soja wanda bai zo ba. Wato ya nuna cewa
kenan, tasirinsu iri ɗaya ne babu wani
sauyi duk da cewa ba lokaci guda aka yi su ba, kuma ba mutum guda ne ya yi ba.
Haka nan a cikin
baiti na 46 an sami irin wannan dabara ta kwatantawa. Ga shi misalin baitin a ƙasa:
Dun ta riga ta zame
mana ma kamar Sunna,
Koko a ce (Wajiba),
sata a kai ajiya.
(Baiti na 46).
A wannan baiti ma, an
sami wannan dabara ta kamantawa. Wato an kwatanta abubuwa guda biyu. Mawallafin
ya yi ƙoƙarin kamanta yanayin muhimmancin sata da sunna ko wajibi
a wajen ‘yan siyasa. Wato ya nuna yadda sunna ko wajibi yake a wajen Musulmi,
haka sata da zambo suka zama a wajen ‘yan siyasa. Dukkanin yadda ka amincewa ɗan siyasa, sai ya yi
sata matuƙar ya hau kan kujerar mulki.
3.1.1.2 Siffantawa
A cikin baiti na 20
an samu doguwar siffantawa wadda marubucin ya yi amfani da ita wajen siffanta
wani nau’in kuɗi na da kai tsaye. Ga
abin da yake cewa:
Ga kasuwar cunku ya
kasha kasuwar Naira,
Darajar sule goma
yau, shi ne kwabo a jiya.
(Baiti na 20).
A nan, marubucin ya
siffanta sule goma da kwabo ɗaya ta hanyar ɗaukar darajar kwabo ɗayan kuma ya ɗora ta a kan sule
goma. Wato ya siffanta kwabo ɗaya kai tsaye da sule goma domin nunawa al’umma irin
yadda mulkin soja ya lalata kuɗin Nijeriya ta hanyar karya darajarsa.
3.1.1.3 Samarwa da Korewa (I, A’a)
Wannan ita ma dabara
ce ta jan hankali wadda mawallafi kan yi amfani da ita don samun yarda daga
makaranci ko mai sauraro (Ɗangambo 2007, sh.53). Wato ya yi
amfani da kore wani abu kuma ya tabbatar da wani domin janyo hankalin mai
sauraro ko karatu ya fahimci saƙon da yake so ya isar cikin sauƙi.
Samarwa da korewa su
ne iyaye a cikin wannan dabara ta jan hankali, amma sun haifar da ‘ya’ya da
jikoki kamar yadda za a kawo ƙasa.
Samarwa + Samarwa
Sun ɓata tsari na kirki
wanda sunka taras. (bait na 3, ɗango na 1)
Ga jahilan nan matasa
masu yin Shi’a. (baiti na 12, ɗango na 1)
Korewa + Korewa
Kowa ya kama gabansa
a daina Tarayya. (baiti na 28, ɗango na 2)
Ƙaryar tsiya, mara sa tausai da imani. (baiti na 49, ɗango na 1)
Samarwa +Korewa
Taki akwai shi, idan
kasaye shi ba riba. (baiti na 23, ɗango na 1).
Ga kasuwar cunku ya
kasha kasuwar Naira. (baiti na 20, ɗango na 1).
Korewa
Allahu ba ya bari
nasa kun ga kau aya. (baiti na 38, ɗango na 2).
Dun kar ku ce muguwar
fata nake niyya. (baiti na 42, ɗango na 2).
Samarwa
In mai makami a hannu
da kansa ya koka. (baiti na 7, ɗango na 21).
Ya zam annoba a
wannan nahiya ku jiya. (baiti na 21,
ɗango na 2).
4.2 Sarrafa Harshe
Sarrafa harshe na
nufin yanayin yadda marubuci ya yi amfani da wata dabara wajen zaɓen kalmomi da
jumlolin da ya yi amfani da su wajen rubuta waƙarsa ta hanyoyi
daban-daban. Lamiɗo da Bara’atu,
Maikadara (2024) sun bayyana sarrafa harshe da cewa, “ wannan ya shafi
gwanintar harshe a waƙa, ta yadda za a yi amfani da wasu dabaru a sarrafa shi
ko a aiwatar da shi cikin hikima domin burge masu sauraro (ko karatu)”.
Daga cikin abubuwan
da ake dubawa a nazarin sarrafa harshe akwai kalmomin aro da tsofaffin kalmomi
da masu zurfin ma’ana da kalmomin fannu da karin harshe da zaɓaɓɓen kalmomi na rukunin
nahawu da sauransu.
4.2.1 Kalmomin Aro
Kalmomin aro ko baƙin kalmomi su ne
kalmomin da makaɗi ya ara daga wasu
harsuna ko wani harshe guda ya tsattsarma a cikin wadiyan waƙarsa domin ya burge
masu sauraro (Lamiɗo da Bara’atu,
Maikadara 2024, sh.211).
A wannan waƙa, an yi aron kalmomi
daga harsuna daban-daban, amma manya daga cikinsu su ne Larabci da Turanci.
Daga cikin kalmomin Larabcin da aka yi amfani da su akwai; mulki, jahilai, shi’a, diyya, kunya, kasuwa, daraja, sharri, nahiya, haƙƙi,
ilimi, Alƙawar, kullun, hujja, hisabi,galabaita, zalunci, aya,
Allahu, Sa’ili, hali, sunna, wajib, imani, rahama, nasiha da kuma zayyana. Haka kuma, akwai
kalmomin Turanci waɗanda aka yi amfani da
su a wannan waƙar kamar irin su ; kananzir,
soja, naira,bariki da sauransu.
4.2.2 Tsofaffin Kalmomi
Tsofaffin kalmomin su
ne kalmomin da ake amfani da su a da, wanda kuma aka sauya su da wasu kalmomin
daban sakamakon sauyawar zamani. Daga cikin tsofaffin kalmomi da aka yi amfani
da su a wannan waƙar akwai; dauri,
fatauci, cunku, sule, kwabo, farace da kuma tafarki.
4.2.3 Kalmomin Fannu
A kowane fanni ko
jigo za a iya samun kalmomin da amfani da su ya keɓanta ga wannan fannin
(Ɗangambo
2007, sh.50). Ma’ana, kowane jigo mutum ya ɗauka ya gina waƙarsa a kansa, akwai
kalmomin da suka dace da wannan jigo, kuma ana sa ran a ga sun bayyana a cikin
wannan waƙa. alal misali, jigon addini, ana sa ran a ga kalmomi
irin nasu Allahu da wa’azi da nasiha da sauransu.
Wannnan waƙa. waƙa ce wadda take da
jigo wanda ya shafi siyasa kai tsaye. Saboda haka an yi amfani da kalmomi waɗanda suka dace da
wannan jigo. Daga cikin kalmomi akwai; mulki,
tsari. Farin-kaya, rikici, kotu, man fetur, cin-hanci, takarda, ƙarya,
bashi, Nijeriya, ƙasa, jari-hujja, zalunci, kuɗi, buƙata da kuma Taryya.
4.2.4 Sauya Sifar Kalma
Sauya sifar kalma shi
ne ragi da mawaƙa kan yi a farki kalma ko tsakiyarta ko kuma ƙarshenta domin taƙaitawa ko daidaita
karin waƙarsu. Ɗangambo (2007) yana cewa “ mawaƙa sukan yi amfani da
‘yancin waƙa ko lalurar waƙa su sarrafa kalma da
sake wa kalmomin siffa da sauransu”. Akwai wurare a cikin wannan waƙa inda aka sauya ƙirar kalma. Ga wasu
misalai a ƙasa:
Giɓin Kalma |
Cikakkiyar Kalma |
|
Ɗau
|
Ɗauki
|
1 2 |
Bar |
Bari |
5 1 |
Zam |
Zamo/zama |
10 2 |
Kau |
Ko |
38 2 |
Idan aka dubi waɗannan kalmomi za a ga
mawallafin ya taƙaita su yayin furta su domin daidaita karin waƙarsa ko kuma wata
lalurar waƙa.
4.2.5 Amfani da Jumla a Waƙar Hattara 'Yan
Siyasa
Jumla na nufin jerin wasu kalmomi masu ma’ana wuri guda bisa wani ƙayyadajen tsari da harshe ya
tanadar. Wannan waƙa gaba ɗayanta an gina gangar jinita da
dogoyen jumloli. Alal misali:
Dama ku daina rawan kai za ku hau mulki.
(Baiti na 1).
Kuma ga shi mu da maƙota ‘yan’uwan juna.
(Baiti na 15)
Ga masu yaji na aiki
dun biɗar ƙari.
(Baiti na 30).
In kun ci sa a ku kai
aiki na san barka.
(Baiti na 35).
Allah ka yafe dukan
laifinsu kai rahama.
(Baiti na 8).
Idan aka dubi waɗannan ɗangwayen baitoci, an
zaɓo su daga farko da
tsakiya da kuma ƙarshen waƙar. Saboda haka, za a ga dukkaninsu
dogaye. Wato dai ba a yi amfani da gajeru da matsakaitan jumloli ba a cikin waƙar.
4.2.6 Giɓin Jumla a Waƙar Hattara ‘Yan
Siyasa
Ɗangambo (2007) yana
cewa “ sau da yawa za a ga akwai wurare a cikin waƙa inda za mu iya cewa
an bar giɓi wanda ake fatan mai
karatu ko mai sauraro ya cike da fahimtarsa. Wannan giɓi yakan shafi tsarin
jimla”.
An samu wurare da
dama a cikin wannan waƙa inda aka samu giɓin jumla, wanda mai karatu da kansa zai ƙarasa ko ya ƙaddara abin da ake
nufi a wurin domin samun tabbatacciya kuma ingantacciyar ma’ana. Ga misalan
wasu jumloli waɗanda aka samu giɓi a cikinsu:
Domin ku sake shiri,
kar ku zaman ƙarya.
(Baiti na 8, ɗango na 2).
Idan aka dubi wannan
jumla, za a ga an samu giɓi musamman a gurbin aiki
na ‘yi’. Wato jumla ya kamata ta kasance kamar haka; domin ku sake shiri kar ku yi zaman ƙarya.
In an yi yau kotu ce
ke tabbatar da shiya.
(Baiti na 18, ɗango na 2).
Idan aka dubi wannan ɗango, za a ga akwai
giɓi a cikinta musamman
idan aka yi la’akari da ita ta fuskar cikar ma’ana. Jumlar ya kamata ta kasance
kamar haka; in an yi tsarin sarautu, amma a yau kotu ce ke
tabbatar da shiya.
Bayar da hanci da
goro wajen biɗar haƙƙi
(Baiti na 25, ɗango na 1).
Haka nan, wannan ɗango ma an samu giɓin ma’ana ta fuskar
gundarin aiki mai madanganci da kuma gurbin doguwar nasaba. Ma’ana, an cire
wata kalma a cikin ɗango domin daidaita
kari, kuma aka barwa mai karatu ya ƙarasa da kansa. Ɗangon ya kamata ya
kasance kamar haka; Bayar da cin
hanci da na goro wajen biɗar haƙƙi
Gidan mu na kan tudu
su sun yi nasu kwari.
(Baiti na 50, ɗango na 1).
A wannan ɗango dake sama, an
samu giɓin kalma na bayanau.
Wato ya kamata ɗangon ya kasance
kamar haka; Gidanmu na kan tudu su sun yi nasu a cikin kwari.
Allah mun ɗaga hannayenmu dube
mu.
(Baiti na 56, ɗango na 1)
Haka shi ma wannan ɗango, an samu giɓi a cikinsa ta fuskar
wakilin suna. Ga dai yadda ya kamata ɗangon ya kasance; Allah mun ɗaga hannayenmu ka dube mu.
3.1.2.7 Karin Harshen
Waƙar Hattara ‘Yan Siyasa
Karin harshen a nufin
wasu ‘yan sauye-sauye da ake samu a tsakanin al’umma ɗaya masu amfani da
harshe ɗaya ta fuskar tsarin sauti
da kalma da kuma tsarin ginin jumla. A cikin wannan waƙa an yi amfani da
wasu kare-karen harshen Hausa. Ga wasu misalai a cikin jadawali:
Kananci |
Daidaitacciyar Hausa |
Zazzaganci |
Daidaitacciyar Hausa |
Sakkwatanci |
Daidaitacciyar Hausa |
In |
Idan |
Dun |
Don |
Tausai |
|
Mai i |
Mayar |
Shashi |
Sashe |
Biɗa |
|
Me |
Menene |
|
|
Tai |
|
Ba |
Babu |
|
|
Daɗa |
|
Sukai |
Suka yi |
|
|
Ishe |
Tarar |
Yai |
Ya yi |
|
|
|
|
Kullun |
Kullum |
|
|
|
|
4.1 Kammalawa
Waƙoƙin Hausa, musamman
rubutattu, suna ƙunshe da wasu saƙonni na musamman.
Wannan ya sa waƙa ta zama wata hanya ta musamman wajen koyar da al'umma
wasu keɓaɓɓun ilimai a rayuwar
yau da kullum da faɗakar da su a kan wasu
muhimman abubuwa ta fuskar nusantarwa da jan-hankali da gargaɗi da kuma kwaɗaitarwa.
A wannan waƙa, an faɗakar da al'umma a kan
illar da mulkin sojoji yake da shi, musamman idan aka yi la'akari da yadda suka
yi mulki a Nijeriya, kuma suka taɓarɓara tsarin ƙasar daga mai kyau
zuwa mummunan yanayi. Haka kuam, waƙar ta yi kira ga 'yan
siyasa da kuma sauran 'yan ƙasa a kan kar su yadda su bari soja ya
ƙara
dawowa ya mulki Nijeriya. Wannan ya sa ya mawallafin ya bayyana irin ɓarnar da sojoji suka
yi iri daban-daban yayin da suke mulki.
Wannan takarda ta yi
nazarin wannan waƙa mai baitoci sittin da ɗaya (61) ta fuskar jigo da zubi da
tsari da kuma salo. Wato, an yi nazarin gundarin jigon waƙar, wato jigon faɗakarwa da taƙaita jigo da kuma
warwarar jigo. Haka kuma, an fitar da zubi da tsarin waƙar ta duban yanayin
yadda mawallafin ya tsara carbin tunaninsa wajen sassaƙa saƙonnin da waƙar take ƙunshe da su. Sannan
aka fito da muhallan da aka samu gangara da saɓi-zarce a cikin waƙar. Haka kuma, an
bayyana salon waƙar gaba ɗaya da cewa salo ne miƙaƙƙe kuma mai armashi ta
yanayin yadda aka yi amfani da dabarun jawo hankali na kamantawa da siffantawa
da samarwa da korewa da zaɓen kalmomi na aro da tsofaffi da na fannu da sauransu.
Takardar ta gane
cewa, mulkin Soja shi ne ya fara ɓara duk wani kyakkyawan tsarin da ƙasa Nijeriya take da
shi tun bayan da ta samu 'yancin-kai. Haka kuma, ya taɓarɓara tattalin arziƙin ƙasar tun daga wancan
lokaci har zuwa yau. Haka kuma, an fahimce cewa, mawallafin ba ya amfani da
dabarun jawo hankali na jinsintarwa a cikin waƙarsa, wannan ya sa waƙar ba ta ɗauke da zambo ko
habaici kai tsaye.
Manazarta
Auta, L.A.
(2017). Faɗakarwa a Rubutattun Waƙoƙin
Hausa.
BUK Press.
Bugaje,
M.H. (2011). Wa’azi a Rubutattun Waƙoƙin Mata na Ƙarni na Ashirin.
Kundin Digiri na
Ɗaya.
Zariya: Sashen Koyar da Harsunan Afirka, Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya.
CNHN.
(2006). Ƙamusun Hausa. Kano. Jami’ar Bayero ta Kano.
Chamo,
I.Y (2011). “Jigo a Fina-Finan Hausa”. A cikin Algaita Journal of Humanities
Sashen
Koyar da Harunan Nijeriya da Kimiyar Harshe, Jami’ar Bayero, Kano Vol.12. No.1 (sh. 66).
Ɗangambo,
A. (2007). Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa. Kano: Kdg Publishers.
Ɗangamob,
H.A. (2012. “Salon Sarrafa Jigo a Adabin Baka na Hausa”. kundin Digiri na uku
Sashen
Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.
Gusau,
S.M (2014). Mu Koyi Ibada. Kano:
Century Res/earch and Publishing Limited.
Lamiɗo, I., da Maikadara,
B.I (2024). “Salon Sarrafa Harshe a Waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru:
Nazari
a Waƙar Amadu Sarkin Kiyawan Ƙauran Namoda”.
Takarda Wadda aka Gabatar a Cikin Four Decades of Hausa Royal Songs:
Proceedings From the International Conference on the Life and Songs of Makaɗa Sa’idu Faru. Sashen
Koyar da Harshe da Al’adu, Jami’ar Gwamnatin Tarayya, Gusau.
Labaran,
M.M. (2024). Waƙa Maƙunsar Ilimi: Nazarin Jigon Koyar da
Ibada a Wasu Waƙoƙin
Malam
Nasiru Kabara. Takarda Wadda aka Gabatar a kan Rayuwa da Gudummawar Malam Nasiru
Kabara. Tsangayar Fasaha da Addinin Musulunci, Jami’ar Bayero, Kano.
Ilyas,
A.H. (2023). Sheikh Ahmad Maƙari
Sa’idu Zariya:
An Icon of Education and Social Transformation. Tanmiya Education Foundation.
Sani,
M.A.A. (1999). Tsarin Sauti da Nahawun Hausa. Ibadan Uniɓersity Press.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.