Citation: Darma, A.Y. and Aliyu, L. (2024). Nazarin Turken Yabo da Gargaɗi a Cikin Wasu Waƙoƙin Mawaƙan Baka. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 315-318. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.039.
NAZARIN TURKEN
YABO DA GARGAƊI
A CIKIN WASU WAƘOƘIN MAWAƘAN BAKA
Abdullahi Yakubu
Darma
Lawal Aliyu
Sashen Nazarin
Harshen Hausa, Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita, Dutsin-ma, Jihar Katsina
Tsakure
Mawaƙan baka na Hausa sun yi fice a wajen shaʼanin gudanar da waƙoƙi na
gargajiya. Shahararrun mawaƙan baka ba su tsaya a wannan ƙasar ba kawai, domin kuwa sun shiga waɗansu ƙasashe
da dama irinsu Nijar da Ghana da Kamaru duk a kan shaʼanin gudanar da waƙoƙi don nuna fasaha da ɗimbin hikimomi da bayyana
falsafarsu da kuma baje kolin basirorinsu a tsarin zamantakewa na al’ummar
Hausawa. Manufar wannan takarda ita ce yin nazarin turken yabo da gargaɗi a waɗansu waƙoƙin. Za
a daɗa fito da irin
hangen nesan mawaƙa a kan yabo musamman yadda mawaƙan kan yabi iyayen gidansu da kuma gargaɗi a kan aiwatar da illar
muganta a tsarin zamantakewar maʼana
yadda za a rinƙa sara ana duban bakin gatari. Haka kuma bincike ya hau wani
ra’i da aka ɗora binciken a kai sai aka
kawo sakamakon bincike da kammaluwa da manazarta.
Fitilun Kalmomi: Turke, Yabo, Gargaɗi, Waƙoƙin Baka
Gabatarwa
Hausawa mutane masu hikima da fasaha da basira da baiwa da
Allah ya hore masu iri-iri. Irin waɗannan hikimomi da basira da
fasaha, sukan fito ƙarara ta
hanyar waƙa ta baka
ko rubutacciya. Da wannan ne masana da manazarta suka fito da ma’anar waƙa da cewa, Furuci ne (lafazi ko
saƙo) a cikin azanci da ake
aiwatarwa ta hanyar rerawa da ɗaiɗaitar
kalmomi cikin wani tsari ko ƙa’ida
da kuma yin amfani da dabaru ko salon armashi.’ (Ɗangambo 1982). Gusau (2008) ya ce, waƙa wani zance ne shiryayye cikin
hikima da azanci da yake zuwa gaɓa-gaɓa bisa ƙaʼidojin shiryawa da daidaitawa a rera a cikin sautin murya da
amsa-amon kari da armashi da kiɗa.
1.1 Ra’in Bincike
Dangane da ra’in da aka ɗora
wannan bincike kuwa, an ɗora binciken a kan Ra’in turken
waƙar Baka Bahaushiya (WBB).
Farfasa Sa’idu Muhammad Gusau ne ya assasa wannan ra’in a shekara ta (1993)
kuma ya ƙara ɗabbaƙa
shi a shekara ta (2014). Wannan ra’in ya samu ƙarɓuwa a wajen masu nazarin waƙoƙin makaɗan baka na Hausa da ɗimbin mabiya.
1.0
Su Wane ne Mawakan Baka?
A Ƙoƙarin yi wa binciken adalci da
gata, yana da kyau a kawo ɗan taƙaitaccen tarihin asali da
samuwar waƙa. Masana
da manazarta adabin baka sun yi ƙoƙari wajen bayyana asali da
samuwar waƙar baka a
cikin al’ummar Hausawa. Ana zaton Hausawa sun sami kiɗa da waƙa
ne daga wajen tsofaffin daulolin Africa, watau Mali da Songhai. Da ma can ita
daular Mali suna da makaɗan fada daga baya da ta shuɗe sai Songahai ta gajeta sai ta gaji irin waɗannan kaɗe-kaɗe. (Ibrahim 1583). Gusau (2023) ya ce, Hausawa sun ƙagi waƙa ne ta hanyar farauta da
kirare-kirare daga baya nan kuma ta daɗa bunƙasa a sakamakon noma da yaƙe-yaƙe. Ashe kenan waƙar baka aba ce daɗaɗɗiya wadda aka fara ta tun
lokacin daɗaɗɗe
mai nisan gaske.
Su kuma mawaƙan
baka su ne, masu amfani da kayan kiɗa don ya taimaka wajen daɗin muryar waƙarsu
kuma sukan sanya tufafin gargajiya ne idan zasu yi waƙoƙinsu. (Ibrahim, 1983:1). Mawaƙan baka su ne yawanci suka gaji kiɗa da waƙa
daga wajen iyayensu da kakanninsu waɗanda suke baje kolin ɗimbin basirar su da hikimarsu a wajen aiwatarda waƙoƙinsu (Hira da Farfesa Bishir Aliyu Sallau na Jami’ar Tarayya
Dutsin-ma a ranar 18/9/2023).
Kenan asalin waƙar
baka ya faru ne daga cuɗanyar Hausawa da waɗansu tsofaffin dauloli inda wannan cuɗanyar ta yi tasiri a wajen, su kuwa mawaƙa duba da yadda masana da
manazarta a kan adabi a iya cewa su ne mutanen da mafi akasari su ka gaji waƙa daga iyayen su da kakanninsu
don kare martabar gadansu na asali.
3.0 Ma’anar Turke
Masana da dama sun yi ƙoƙari wajen bayar da ma’anar turke
kamar haka:
Ƙamusun
Hausa (2006:446) ya bayyana turke da cewa wani guntun itace da ake kafawa don ɗaura dabba a jikinsa.
Gusau (2008:370) ya bada ma’anar turke kamar haka saƙon da makaɗi yakan zaɓa ya gina waƙarsa ya tarye kansa da kansa ya
zuɓa ɗiyanta
bisa wasu zaɓaɓɓun
kalmomi da za su doshi wata babbar manufa.
A bisa fahimta kuwa a iya cewa turke wani babban bango ne da
mawaƙi yake jingina waƙarsa domin isar da saƙon manufarsa.
3.1 Ma’nar Yabo:
Yabo na ɗaya daga cikin halaye da mawaƙan baka suke amfani da shi wajen
gudanar da waƙoƙinsu don bayyana irin namijin ƙoƙari da wani mutum yake aikatawa ta hanyar kyauta a gareshi
konuna halin kyautatawa ga al’umma. Yabo yana nufin waɗansu maganganu da ɗabi’ar halayyar Hausawa suke
aikatawa wato kalma a mai ɗaɗi
da aka ambata ga wani (CNHN, 2006:476). Don haka wataƙila da wannan ne mawaƙan baka suka tsunduma a wajen
yabon mutane a ƙasar
Hausa.
3.1.1 TurkenYabo a Wasu Waƙoƙin Mawaƙan Hausa
Wannan bincike ya dubi misalan waɗansu waƙoƙi da mawaƙan baka suka fito da shi domin
yaba gwarzayensu musamman a kan abin da ya shafi halin kyautatawa da abinda iya
mulki da kare martabar addini.
Musa Ɗankwairo
yabo a wata waƙoƙinsa in da yake yabon Sardaunan
Sakkwato inda yake cewa:
Bangon tama mai wuyar karo
Bajimin Sa Kashim Uban Zagi
Bello ɗan Hassan,
Mai martaba Abdullahi
Mai martaba Moyi da Atto da uwar
Daje,
Mai martabar Isan Kware, Autan
Shehu
Mai martabar Ibrahim mai ƙahon karo,
Sadauki ɗan sadauki,
Kakanninka waliyan Allah ne
Ba ba’a ba ko can,
Ko lahira ma taulahinmu na nan
Can wajen hannunsu na dama.
(Musa Ɗanƙwairo: Waƙar Sardauna)
Alh. Musa Ɗanƙwiro ya fito da babban saƙonsu na turken yabo a ɗiyan waƙarsa
na 9 dana 11 a waƙar ya
wuce raini ba a yi mai shi.
Makaɗa sarkin taushi sarkin katsina
ya yabi sardauna dangane da sha’anin mulki da jarumta da kuma addini a waƙarsa inda yake cewa:
Idon batun mulki ne, ba a gaya
ma kome,
Bello shi ak kakanka sun sani ba
wai ba
Idan batun addini ne ba a gaya
ma kome,
Usmanu Shehu shi ak kakanka, sun
sani ba wai ba.
Idan batu yaƙine ba a gaya ma kome,
Atiku shi ma kakanem, sun sani
ba wai ba,
Atiku yai yaƙi,
duk ƙasa ga ba’a korai ba,
(Sarkin Taushin Katsuina: Waƙar Sarkin Katsina)
A wannan waƙa
makaɗin sarkin taushin Katsina ya
fito da tunken yabo na iya mulki ne na 1 dana 2, haka kuma makaɗa sarkin taushin Katsina ya fito da turken jarumtaka a ɗa na ta waƙarsa.
Sha’anin addini kuwa makaɗa
sarkin taushin Katsina ya fito da turke na 3 a waƙarsa.
Makaɗa galadiman kotso Alhaji
Abdurrahman ya yabi sarkin Kano Muhammad Sanusi ta fuskar kawo cigaban ƙasa a wata waƙarsa inda yake cewa:
Na ayyukan gona sun kyawu,
Zamanin mamman na abashe,
Shinka badankama marar auki,
Du sun kasheta, yanzu kilaki
mukanci,
Ankas tsohuwar gyaɗa marar auki,
Saiko mace tsugune muke shukawa,
Mai abkin ‘ya’ya ga manoma,
Gontamaru rogo du, an kasha
Mu yanzu sai ɗon waru mukanci.
(Makaɗa Galadiman Kotso: Waƙar Sarkin Katsina)
Makaɗa Galadiman kotso ya fito da
bayanai irin cigaban da Kano ta samu a zamanin sarkin Kano Muhammadu Sanusi na
I ta fuskar aikin gona don kuwa suna da ire-iren shuka ga manoma. Za a iya
tabbatar da su dukkan ɗiyan waƙar makaɗa Abdurahman Galadiman Kotso.
Don haka waɗannan misalan waƙoƙin na mawaƙa
da binciken ya zaƙolo na a
matsayin misalan gina turken yabo a waƙoƙin baka na garajiya domin isar
da saƙonsu.
3.2 Ma’anar Gargadi
Gargaɗi na nufin jan kunne ko yin
kashedi ko horo (CMHN, 2006:159).
Anan makaɗa na amfani da gargaɗi wajen shirya waƙoƙinsu na gargajiya domin yin horo
da hani a zamantakewar al’umma don faɗawa zuwa a wani mummunan yanayi
ko kiyaye doka da bin umurnin shugabannin ƙasa.
3.2.1 Turken Garaɗi
a Wasu Waƙoƙin Mawaƙa Hausa
A tattare da wannan ɓangaren binciken nan ya dubi waɗansu mawaƙa
da suka shirya waƙoƙinsu a wannan turke domin jan
hankalin jama’a a kan waɗansu halaye masu kyau da kuma
akasin haka.
Kamar a cikin waƙar
Dr. Mamman Shata ya fito da turken gargaɗi a waƙarsa inda yake cewa:
Ni dai tsorona sarki Allah
Sannan tsorona ramin mugunta.
(Waƙar Gargaɗi mai gina ramin mugunta ɗa 1).
Haka kuma (Dr) Mamman Shata ya ƙara fito da turken gargaɗi a ƙaɗansu waƙoƙarsa kamar haka
Kai dai maigina ramin mugunta
To ka gina daidai kwabrinka
Wata ƙila kai ka faɗa.
(Waƙar
gargaɗi mai ina ramin mugunta da na 2).
Haka kuma, a wani ɗan waƙar makaɗin Mamman shata ya sake fito da turken gargaɗi inda yake cewa:
Gama a naka aikin daidai
Ka bar shi ka nufo wani kangun,
Kana biɗar ka bata mai shi.
Wannan ne ina ramin mugunta.
(Mamman Shata: Waƙar Maigina Rmin Mugunta).
Haka kuma, a cikin waƙar
Alh. Adamu ɗan maraya Jos ya fito da turken
gargaɗi a wata waƙarsa kan aure inda ya ce:
Maigida da uwargida
In an yi faɗa don annabi
Don Allah bar saurin fita
Da can kina ko gidan miji
Ɗan kwali shi za ya yi
Rigar sawa shi ya yi
Zanan ɗaurawa shi za ya yi
Agogon hannu sai ya yi
Tuwon dawa in zaki ci
Maigida yai tanadi
Sannan sakwara in za ki ci
Tuwon shinkafa kin jiya
Maigida yai tanadi
Uwa da uba ya kula dasu
Duk taskar Allah zaku ci
To yanzu da ba ki da maigida
Wannan abu duk ke za ki yi
Haka kinga asara taki ce
Maigida kai zan maka gargaɗi
Kai ma wannan matarka ce
Ruwan wanka ita za ta kai
Sharar ɗaki ita za ta yi
Ta tuƙa abinci ka zoo ka ci.
(Ɗanmaraya Jos: Waƙar Maigida da Uwargida)
Duba da wannan waƙa
ta makaɗin Dr Alh. Adamu Ɗan maraya Jos za a iya cewa ɗiyan waƙarsa
na uku ya fito da turken gargaɗi.
Haka a ɗiyan waƙarsa na 20 ya fito daturken waƙarsa inda yana gargaɗin maigida akan kula da matarsa.
Haka kuma, Dr Mamman Shata a wata waƙarsa ya fitoda jigon gargaɗi a waƙar
kuɗi a kashe su ta hanya kai kyau
misali:
Kuɗi
a kashe su ta hanya mai kyau
Ka tuna yadda ka sami kuɗinka,
Ka sha wuya ka sami kuɗinka,
To ka kashe su ta hanya mai
kyau.
Kuɗi
a kashe su ta hanya mai kyau.
(Mamman Shata: Waƙar
Kuɗi a Kashesu ta Hanya Mai Kyau)
Dr. Mamman Shata ya fito da turken gargadi a wannan waƙa a ɗiya na 4.
Haka ma a wani ɗan waƙa Dr Mamman Shata ya ƙara fito da turken gargaɗi kamar haka:
Duk wuyar shi duk ɗaɗin shi,
In ka sami kuɗinki ka tara
Indai kai niyar ɓadda su,
To ka kasha su ta hanya mai
kyau.
(Mamman Shata: Waƙar kuɗi a kasha su ta hanya mai kyau).
5.0 Kammalawa
Wannan takarda ta bijiro da yabanai masu nasabar irin yadda
mawaƙan baka suke bayar da
gudummuwarsu wajen shirya waƙa
mai ɗauke da turke daban-daban wanda
a ciki a ka yi nazarin turken yabo da na gargaɗi
domin isar da sako ko hannun ka mai sanda ga al’umma, domin gyara halayya.
5.1 Sakamakon Bincike
Sakamakon wannan bincike an fahimce yadda mawaƙan baka ke shirya waƙoƙinsu a kan turken yabo wanda sukan dubi waɗansu mashahuran mutane masu daraja a cikin al’ummar Hausawa
akan wani abin da za a yaba masu alalmisali sha’anin addini da na tsarin mulki
da kuma jarumtaka inda ake kawo misalan waɗansu waƙoƙi na yabo da waɗansu mawaka suka wake irin waɗancan mutane a cikin al’umma. Haka kuma wani sakamakon
bincike ya fito da yadda mawaƙa
suke shirya turken gargaɗi a mabanbanta waƙoƙinsu domin jawo hankali da hani da horo da kuma yin
hannun-ka-mai sanda a zamantakewar yau da kullum ta rayuwar Hausawa.
Manazarta
C. N.H.N (2006). Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero, Ahmadu Bello University
Press.
Dangambo, A. (1982). ‘Jigon
Ban Dariya a Adabin Hausa’ Takardar da aka gabatar a taron ƙarawa juna sani, Kano: Sashen
Koyar da Harsunan Nigeria, Jami’ar Bayero.
Farfesa Bishir Aliyu Sallau. An
yi hirar a Jami’ar
Tarayya ta Dutsin-ma, a ranar 18/9/2023.
Gusau S.M. (2018). Diwanin Makaɗan Baka na Hausa (Juzi’ina Uku). Kano: Country Research and
Publishing Limited.
Gusau, S.M (2015). Mazhabobin
Ra’I da Tarke a Adabin da Al’adu na Hausa, Kano: Century Research and
Publishing Limited.
Gusau, S.M (2023). ‘Jagoran
Nazarin Waƙar
Baka’ Kano:
Bothmark Publishers Limited.
Gusau, S.M. (2008). Waƙoƙin Baka a Ƙasar
Hausa: Yanaye-yanayensu da sigoginsu, Kano: Bothmark Publishers Limited.
Ibrahim,
M.S. (1983). Kowa ya sha Kiɗa. Ikeja, Laos: Longman Nigeria
Plc.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.