Ticker

6/recent/ticker-posts

Kurciya Jawabi Ne Sai Mai Sani Ka Ganewa: Sarkin Musulmi Muhammadu Maccido a Ma’aunin Makada Sa’idu Faru

Citation: Bunza, A.M. (2024). Kukan Kurciya Jawabi Ne Sai Mai Sani Ka Ganewa (Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo a Ma’aunin Makaɗa Sa’idu Faru). Four Decades of Hausa Royal Songs: Proceedings from the International Conference on the Life and Songs of Makaɗa Sa'idu Faru, 3(3), 21-28. www.doi.org/10.36349/tjllc.2024.v03i03.003.

KURCIYA JAWABI NE SAI MAI SANI KA GANEWA
(Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo a Ma’aunin Makaɗa Sa’idu Faru)

Daga

Aliyu Muhammadu Bunza
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato

Tsakure

Ayyukan da aka yi kan adabin waƙa sun fi na kowane ɓangaren adabi yawa a nazarin Hausa. Mawaƙan baka na Hausa ba lungun rayuwar Hausawa da ba su waƙe ba. Sa’idu Faru a cikin makaɗan fada ba ƙyalle ne ba. Alhaji Muhammadu Macciɗo Sarkin Kudun Sakkwato ne maigidansa. Makaɗa Sa’idu Faru ya yi wa Sarkauna da ‘ya’yan sarauta da yawa waƙa, amma na Sarkin Kudu Macciɗo sun fi yawa da shahara. An yi amfani da dabarar bincike ta ga-wuta-ga-masara wajen tace waƙoƙinsa domin a hango wuraren da ya yi kukan kurciya game da yadda maigidansa zai kasance. A taƙaice, duk wanka da kamar jurwayen da ya yi na fatar Sarkin Kudu Macciɗo ya kasance jagoran gidansu da hawa gadon sarautar Sarkin Musulmi sun tabbata bisa ga kasancewarsa Sarkin Musulmi na (19). Tunaninsa na yadda zaɓen Sarkin Musulmi Macciɗo zai kasance ya tabbata. Yadda ya yi hasashen mutuwarsa haka ya kasance. Da yawa jifa cikin duhu yana kasancewa kamar ga bakin boka, haka ko ta kasance. Akwai buƙatar manazarta adabi su fara tunanin nazarin adabinsu a kimiyance fiye da tsayawa kan salo da jigo da turakun tussan adabinsu. Sakamakon wannan ɗan nazari ya nuna muna ruwa na ƙasa sai ga wanda bai tona ba. Samun sababbin abubuwa cikin adabin yanzu aka fara. Kowane zango na adabi da ire-iren abubuwan da za a tsinta a ciki.

Gabatarwa

Adabin baka babbar taska ce ta binciken kowane ilmi na rayuwar mutanen da suka rayu da shi, domin babu cigaban duniya da ya fara da rubutu. Ashe rubutu wata fasaha ce da ta tsira bayan da tunanin mutane ya kammala, kimiyyar fannonin rayuwa da yawa sun bunƙasa, sai fasahar taskace su ta bayyana da baya. Daga cikin ressan adabin baka, babu mai gwada tsawo da adabin waƙa ba ta yi masa kere ba. Ga alama, da waƙar baka da magana zozo-zozo suke tafiya a tarihinsu. Don haka, a ƙunshiyar waƙar baka babu irin saƙon da ba a tsinta a ciki, sai dai wanda hangen mai hange bai hango ba. Tunanin wannan takarda shi ne, ɓarke laya na wasu kuramen ɗiyan waƙar makaɗa Sa’idu Faru a kan rayuwar maigidansa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo Abubakar III waɗanda ya yi a matsayin wanka da kamar jirwaye kuma suka kasance kamar a bakin boka bayan su duka sun bar duniya (Allah Ya gafarta musu). A lokacin da makaɗa Sa’idu ya yi su, suna matsayin “kukan kurciya”; bayyanar da suka yi gare mu a yau ƙiri-ƙiri muka kasance masana ga manufarsu.

Kwakkwahe Tunanin Matashiya

A zatona, babu mai musun kasancewar babbar matashiyarmu “karin magana”. Haka kuma, karin magana wani babban kogi ne daga cikin manyan kogunan adabin baka. To, riwayoyin karin maganar nan akan ji su ga bakunan magabata da ajin kalmomi daban-daban kamar haka:

a.   Kukan kurciya jawabi ne mai hankali ka ganewa.

b.   Kukan kurciya jawabi ne sai mai sani ka ganewa.

c.    Kukan kuricya jawabi ne sai mai hankali da mai lura.

Abubuwan kula gare mu ɗalibai shi ne, tattare da sassaɓawar muhallin kalmomi da daɗi ko ƙari cikin waɗannan riwayoyi za mu ga kowace daga cikin su ta kawo:

a.   Kalmar kurciya sananniyar tsuntsuwa ce a ƙasar Hausa.

b.   Kukan da kurciya ke yi.

c.    Cikin kukan akwai hikimomi/saƙon da ya kamata a kula.

d.  Kukan da yake ba magana ne buɗe ba, da ilmi ake fashin baƙinsa.

e.   Masanan su ne, waɗanda aka yi gaban idonsu ko ma’ilmanta su yi kirdado.

A ɗan nawa bincike, wai ko, anya! Asalin karin maganan ba “kukan kuricya” kawai yake ba? Dalilina kuwa shi ne, kalmar jawabi “Larabci” ce daga “jawab” kuma ga alama “kurciya” ta riga ‘Larabci” shigowa ƙasar Hausa. Haka kuma, adabin Larabci bai kawo kurciya a ƙarƙashin inuwar hikimomin da Bahaushe ya saka ta ba.

Hanyar Ɗora Bincike

Ba zan ɗora bincike bisa tafarkin ‘yan duba ba, domin makaɗa Sa’idu Faru da maigidansa Sarkin Musulmi Muhammadu Maccidɗo Abubakar III, ba su bi hanyar nan ba. Wannan ya sa na yi tunanin ɗora binciken a kan wasu fitattun zantukan makaɗan fada masu cikakken ilmin fada da sanin mutanenta da ire-iren yanaye-yanayenta. Na farko, na lalubo maganar marigayi Aliyu Ɗandawo a fagen da yake wasa Sarkin Kabi Isma’ila a faɗarsa:

Jagora: Magaba abin da sun ka hwaɗi,

Yara: Ai mai da hwaɗi ɓanna na,

Gindi: Shugaban tahiya Sarkin Kabi mai Sudani,

: Ila marin rugga ɗan Yaƙuba sa gurfani.

Babu shakka idan magabaci ya gawurta da yawa za a taras da cewa, maganarsa nashin ƙasa ce babu kure. Sakamakon ganin abu yau, da gobe, da ire-iren sauye-sauyen da yake yi, ke sa su yanke hukunci a taras sun sara a kan gaɓa. Makaɗa Ibrahim Narmabaɗa ya taɓa wata magana da yake cewa:

Jagora: Maidamma,

: Ya hwaɗi sai an yi ka sarki.

Yara: Ta ko tabbata ka yi.

Gindi: Iya gaba ginshimin Malam Dikko ɗan Buhari.

Magabata sun hango sai ya hau gadon mahaifinsa sai ga shi Allah Ya tabbatar da shi sarki. Wanda duk aka haifa a gidan sarauta yana fatar ya wayi gari a kan gadon. Ire-iren waɗannan hasashe da ake yi wa ‘ya’yan sarauta ana kiran su “fata”. Idan fata ta cika ita ce, “Kukan kurciya” da mawaƙi ya yi. Idan kushe ɗan sarauta aka yi aka nisantar da shi ga gadon gidansu a al’adance an “kafa masa kara” idan karan ya tsayu “baki” ya kama shi. Dubi misali a wata da’awar Dr. Narambaɗa da ke cewa:

Jagora: Ka ga ɗan Sarki da kunnuwa da hwaɗi,

Yara: Ga shi da ƙarya ga shi da rowa,

Yara: Ko ga girmama shi ba shi sarki.

Gindi: Masu gari mazan gabas tsayayye,

: Sarkin Rwahi ya wuce a rammai.

A cikin wata waƙar Sarkin Bukkuyum Alhaji Muhammadu Makaɗa na cewa:

Jagora: Ɗan sarki mai gajeren wuya,

Yara: Shi ƙarshe nai ginak kwakwara.

Gindi: Muhammadu mai gida Bukkuyum.

Kunnuwa da faɗi, da ƙarya, da rowa, duk ba su hana a yi sarauta in an ƙaddaro. Haba! Yaushe gajeren wuya ya zama wani dalili na naƙasa ga siyasa? Waɗannan duk “kafa kara” aka yi, in sun tabbata baki ya kama mai su. To ire-iren waɗannan ɗiyan waƙar makaɗa Sa’idu Faru da suka ambaci Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo nike son in ɗan taɓo gwargwadon fahintata. Don haka na dahi kafaɗar Dr. Ibrahim Abdulƙadir Maidangwale Tubali Narmabaɗa a zancensa na yi wa magabata hangen sa a faɗarsa:

Jagora: Ɗan bajini shi ka zama bajini,

Yara: Yai bobakali yai tozo,

Yara: Ɗan akuya na kallo.

Gindi: Na yaba ka da girma Audu ƙanen mai daga,

: Kanda mu san kowa kai mun ka sani Sardauna.

Hausawa sun ce, sanin asali kan sa kura cin kanjilo. A ce bajini ya haifi ɗa, ba abin mamaki ba ne ya zama bajini. Fatar da ake yi masa ke nan, kuma fatar ta cika ya kasance bajini.

Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo

Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo ɗa ne ga Sarkin Musulmi Abubakar III (1903-1988). An haife shi ranar 20 ga Afirilu, shekarar 1928 a garin Dange. Shi ne Sarkin Musulmi na 19. Allah Ya yi masa rasuwa cikin haɗarin jrigin sama na kamfanin Aviation Development Company (ADC) da ya tashi daga Abuja zuwa Lagos ranar 29 ga Oktoba, 2006. Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo Abubakar III na da gurabu guda bakwai gare mu ɗaliban bincike:

a.      Shi ne ɗaya daga Sarakunan Musulunci da ya gada daga mahaifinsa.

b.      Shi ne na biyu daga cikin Sarakunan Musulunci da suka yi karatun Boko.

c.       Shi ne na biyu daga cikin Sarakunan Musulunci da suka hau mulki zamanin mulkin Soja.

d.     Shi ne Sarkin Musulmi na farko da ya riƙa muƙamin siyasa.

e.      Shi ne Sarkin Musulmi na farko da ya mutu sanadiyyar haɗari.

f.        Shi ne Sarkin Musulmi na biyu da ya hau bayan tumɓuke wanda ke kan karaga.

g.      Shi ne Sarkin Musulmi na farko da aka yi wa taron ilmin nazarin waƙoƙin da mawaƙinsa ya yi masa.

Makaɗinsa Sa’idu Faru mawaƙin sarauta ne, ya yi waƙoƙi da yawa ga sarakuna, da ɗiyan sarauta, daban-daban amma kasancewar Macciɗo mai gidansa, waƙoƙin da ya yi masa sun zarce na sauran yawa.

Kukan Kurciya a Ma’aunin Adabi

Ba Sa’idu Faru ya fara yin kukan kurciya a waƙoƙinsa ba, hasalin ma gabanin a haifi Sa’idu Faru akwai karin maganar kukan kurciya. Muradin kukan kurciya a adabi shi ne:

a.   A yi hannunka-mai-sanda ga wani abu gabanin aukuwarsa.

b.   Ya zo ya auku ko kusa ko da nisa.

c.    Mutanen da suka shaida shi suna da masaniyar an ce zai kasance.

d.  Masana kaɗai ke da asirin sanin kukan kurciyar bisa ga gogewarsu

Ga ɗan misalin share fage daga cikin sassan adabin Bahaushe da al’adunsa:

“Da haka muka fara kuturu ya ga mai ƙyasfi”.

Kuturu a nan shi ne masani kuma malamin da ya san halayyar cutar kuturta. Ya san da cewa, ba a dare ɗaya kawai za a tashi a rasa yatsu ba ko jiki ya bushe, fuska ta ƙaƙƙamure. A’a, kaɗan-kaɗan abin ke faruwa har ya game jiki. Wa ya san da haka? Wa ke da wannan ilmi? Sai wanda ciwon ya kama ko waɗanda suka gaji cutar a gidansu. Don haka, “kyasfi” a nan, zaman kukan kurciya yake masu masaniya a kansa su ne kutare. Idan muka nazarci ɗan gajeren labarin da na samo a Sakkwato wajajen shekarar 1982 a unguwar Giɗaɗawa za mu ƙara fayyace kukan kurciya a al’adance:

An ce wani Bayarbe ne ke zaune a garin (Wurno/Raɓa?) tun wajajen shekarar (1950s). Ya aikata wani laifi aka kai shi kotun Alƙali Umaru na garin. Alƙalin ya ci shi tara ta wajen “fam biyar”. An ce, a lokacin sai ya share shekara biyar bai gama biyan tarar ba, domin kuɗi sun ƙaranta a hannun mutane. Ya yi ta biya shekara da shekaru kotu kawai yake yi wa biɗa. Alƙali Umaru Alƙalin kotun Musulunci ne da sai wanda ya goge ga karatun zaure za a ba kotu. To! wata rana Bayarbe na ganinsa, ga wani yaro almajiri ya zo yana bara, sai ya daka masa tsawa da cewa: “Tafi ki ba mu wuri, ka da ki sake tahowa sagonmu, in kin sake, za mu buge ki, shegiya kawai, mutumin banza”. Matar Bayarbe ranta ya ɓaci da ganin mijinta na zagin ɗan yaro rataye da allo don ɗai ya zo bara shagonsu. Ta ce wa mijin; “Haba Oga, yaya za ka yi haka? Laifin me ya yi maka? Ai yaro na kowa ne. Kai! Wannan ba cau”. Mijin ya ce: “Rufe bakinki, mutumin banza, ai irinsu ne, in ta girma ta zama Alƙali Umaru”.

Shi “Oga” kukan kurciya ya gani ya san su Alƙali Umaru daga ƙaratun allo aka fara, daga nan kuwa in an ƙasaita sai a zama Alƙali a yi ɗanyen hukunci irin wanda aka yi masa.

Macciɗo a Ma’aunin Sa’idu Faru

Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo yana da rawanin Sarkin Kudu a zamanin mulkin mahaifinsa Sarkin Musulmi Abubakar III. Sarautar Sarkin Kudu sarauta ce da ake ba ɗiyan sarakuna. Sarauta ce kamar kowace sarauta da ake bai wa ɗiyan sarki, sai dai ta Sarkin Kudu Macciɗo ta fi shahara musamman a tafashen Sa’idu Faru. Bisa ƙa’idar tsarin waƙoƙin Sa’idu Faru na Sarkin Kudu Macciɗo za mu ga hoton kukan kurciya kamar haka:

Hangen Wasu Ɗabi’u na Ɗaukaka

Kowane makaɗin fada ƙoƙari yake ya gamsar da masu sauraronsa cewa, maigidansa maɗaukaki ne. Idan muka dubi irin yadda makaɗa Sa’idu Faru ya tsaro irin ɗaukakar Sarkin Kudu Macciɗo, za mu ga kukan kurciya ne yake ƙoƙarin yi na buƙatar da ke gaba. Ga yadda ya tsara kukan kurciyar:

Jagora: Maganag ga da za ni hwaɗa maka,

: Gagarau ɗan Alu kai min gafara,

Yara: Wada duk aka gadon ɗaukaka,

Yara: Wada duk aka gadon ƙasura,

Yara: Wada duk aka gadon cigaba,

Yara: Mamman ka gadi Abubakar.

Gindi: Kana shire baban ‘yan ruwa,

: Na Bello jikan Ɗanhodiyo.

Roƙon da makaɗa Sa’idu ya yi na faɗar a gafarta masa da abin da ya biyo bayan roƙon gafarar ba su yi kunnen doki ba. Roƙon gafarar kukan kurciya ne domin abin da ya biyo baya fata ce ake yi masa. Yi wa ɗan sarki fatar hawan gadon mahaifinsa yana tare da abubuwa guda biyar:

a.      In dai uban ya rasu a gada.

b.      In ko an tuɓe uban a gada.

c.       In uban ya yi murabus a gada.

d.     In an hukunta uban da laifin da bai cancanci dogewa ba. Shi sauka, a gada.

e.      In ko uban ya aje da kansa bisa wani uzuri ya nemi alfarma a ba ɗa.

Babu mai fatar waɗannan abubuwa biyar ga mahaifinsa. Dole ko sai ɗaya ya wakana za a gaji uba. Waɗannan abubuwa dukkansu a yi jaje ne ba na madalla ba, don haka ya roƙe shi gafara. Kamar ga bakin boka, a ƙarshen mulki Sarki Abubakar zamanin mulkin Shagari ƙarƙashin jam’iyyar NPN, an ce masarautar Sakkwato ta nemi a ɗauke wa Sarki Abubakar III nauyin aikin sarauta a ba Sarkin Kudu, wanda a lokacin yana kwamishina a mulkin Gwanna Shehu Muhammadu Kangiwa. Masu jiran gado suka yi tsaye da cewa sai dai ya yi murabus, a yi zaɓe sabo. Kukan kurciya ya tabbata a nan, ai a rufe ɗan waƙar cewa ya yi:

“Mamman ka gadi Abubakar”.

Gindin waƙar ma, wani kukan kurciya ne “Na Bello”, “Jikan Ɗanhodiyo”. Ɗanfodiyo ya jagoranci jihadin tabbatar ɗaular Musulunci, Bello ne Sarkin Musulmi na farko don haka, Sarkin Kudu sai ya yi. Waɗannan abubuwa duk sun bayyana bayan mutuwar makaɗa Sa’idu Faru.

Ɗora Shi Gadon Mahaifinsa

Makaɗa Sa’idu Faru a cikin wasu ɗiyan waƙoƙinsa yana kukan kurciya da nuna kai tsaye sai Sarkin Kudu Macciɗo ya gaji mahaifinsa. Babu wai, kowane ɗan sarki fatarsa ke nan kamar yadda makaɗa Dr. Ibrahim Abdulƙadir Maidangwale Tubali Narambaɗa ke cewa:

Jagora: Kowane ɗan sarki,

: Son shikai shi zan sarki.

Yara: Sai in ba ta samuwa,

: Ta tabbata ko ban hwaɗi ba,

: In gandu yas samu ya hi gamana.

Gindi: Ibrahimu na Guraguri,

: Mai Shinkahi bajinin zagi,

: Mu dai Allah Shi bar muna kaya.

Makaɗa Sa’idu Faru ya yi wa Sarkin Kudu kukan kurciya da cewa:

Jagora: Ka gadi Bello ka gadi Moyi,

Yara: Saura ka kai inda Maihausa yak kai,

: Na Magaji Maimartaba ɗan Mu’azu.

Gindi: Farin cikin Musulmin duniya,

: Maimartaba na Abubakar,

: Ƙi fansa Alhaji Macciɗo.

Ƙoƙarin kawo waɗanda Macciɗo ya gada musamman Bello, da Moyi, da “Maihausa” kukan kurciya ne na nuna hawa sarautar Musulunci ta gaba ɗaya. A dubi ɗan waƙar farko na gindin waƙar cewa ya yi:

“Farin cikin Musulmin duniya.

Sarkin Kudu aka yi wa waƙar, amma aka nuna farin cikin duniyar Musulmi ne gaba ɗaya. Waɗannan abubuwa duk martabar mahaifinsa ce ake yi mishi kukan kurciya da ita, tun yana Sarkin Kudu, har Allah Ya ƙaddare shi da hawa gadon mahaifin nasa.

Ambaton Sa Magajin Mahaifinsa

A koyaushe makaɗa Sa’idu Faru na nuna bai wuce gona tai da iri ba ga Sarkin Kudu ya tsaya a ‘yan waƙe-waƙensa. Abin da yake ƙoƙarin nuna wa duniya shi makaɗin ɗan Sarkin Musulmi ne, bai kai ga darajar yi wa Sarkin Musulmi waƙa ba, amma kuma yana ƙoƙarin kwatanta Sarkin Kudu da Sarkin Musulmi. Ga zancen ƙarara daga makaɗa Sa’idu:

Jagora: Halin ga da Bubakar yar riƙa.

Yara: Macciɗo ɗai ka shirin gado haka.

Sa’idu Faru ya yi wa Muhammadu Macciɗo waƙa a lokacin yana Sarkin Kudun Sakkwato kuma Sarkin Musulmi Abubakar ke sarauta. Ya nuna irin halayen da Sarkin Musulmi Abubakar III ke da su ya ce:

“Macciɗo ɗai ka shirin gado haka.

Cewar da ya yi “Macciɗo ɗai” ɗai ɗin nan tana zaman shi kaɗai a cikin ‘ya’yan sarautar lokacinsa. Ya ƙara da cewa, “shirin” wato ya riga ya shirya a koyaushe lalurar hawan gado ta taso. Hausawa sun ce, shirin shiga ruwa tun tudu ake kimtsa shi. Makaɗa Sa’idu Faru ya yanke hukuncin Sarkin Kudu ya san hanya kamar yadda malamin kiɗi Dr. Ibrahim Narmabaɗa ke cewa:

Jagora: Ah! Ji wanda bai san hanya ba,

: Ya yi sabko amma fa ya ɓace ya dawo.

Yara: Ila da yat tahi bai ɗora tambayar kowa ba.

Gindi: Ginshimin Haliru Uban zagi na Malam Isa,

: Gagarau jikan Shehu Iro mai Shanawa.

Babban kukan kurciya a nan shi ne faɗar “Gado haka”. Bisa ga hasashe makaɗa Sa’idu ya yanke hukuncin Sarkin Kudu Macciɗo zai gaji Sarkin Musulmi Abubakar. Ga irin hasashen Sa’idu Faru kai tsaye Sarkin Kudu zai kasance Sarkin Musulmi bayan ƙare sarautar Sarkin Musulmi Abubakar. Mai ƙaddarowa ya ƙaddaro da haka, amma cikin wani tsari irin nasa tsari sai da Sarkin Musulmi Ibrahim Dasuƙi ya yi sarautar Musulunci Sarkin Kudu Macciɗo ya yi. Kukan kurciya dai ya tabbata ga fassarar da aka samu ta kasancewar Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo Sarkin Musulmi na (19). Yadda duk al’amari ya kasance an sara a kan gaɓa.

Kiran Sa Sarkin Musulmi Kai tsaye

Daga cikin fatar da makaɗa Sa’idu Faru ke yi wa Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo shi ne, ya zama Sarkin Musulmi. Duk wata magana da ya yi mai nuna zuwa ga wannan batu ba ta yi ficen wannan ɗan waƙa ba:

Jagora: Dubi ƙahwakka zuwa bisa hannuwa,

Yara: Ka san Shehu na ba wata za’ida.

Jagora: Sarkin Musulmin wataran kake,

Yara: Da imani da mu’ijjiza na nan ga Malam Macciɗo.

Wannan zance ya tsallake wanka da kamar jirwaye ya zama filin wuri dabon Ɗankama. An ambaci abu ƙarara ba a sa rana ba balle a ƙayyade lokaci an dai ce: “Wataran” Bahaushe ko cewa ya yi: “Wataƙila mai hana wa Bature ƙarya”. Da “wataƙil” da “wataran” ma’auninsu ɗaya a nahawu da sarfu da Balaga Bahaushiya. Yau ga shi, abu kamar ƙaddara in ji Buzu da ya sha kayen raƙumi. Wannan kukan kurciya fashin baƙinsa a fili yake domin Sarkin Kudu ya kasance Sarkin Musulmi bayan da Sa’idu Faru ya riga ya koma wa Mahaliccinsa. Ga al’ada da nahawu, idan ɗan’adam ya ce wani abu zai auku wataran, ba a tsammanin abin ya faru yana raye. Don haka Hausawa suke da karin maganar da ke cewa, “Wata rana sai labari.” Ke nan, kukan kurciyar Sa’idu Faru ya tabbata, Alhaji Muhammadu Macciɗo ya zama Sarkin Musulmi bayan da Sa’idu Faru ya koma ga Mahaliccinsa. Allah Masani!

Yi Masa Tarbo Irin na Sarkin Musulmi

Fatar da makaɗa Sa’idu Faru ke yi wa Sarkin Kudu ya sa, ya kawo jawabin yadda aka yi masa tarbon ban kwana da zai je aikin Haji irin tarbon da ake yi wa Sarkin Musulmi na kowane zamani. Ya fara da cewa:

Jagora: Bajiri ɗan gagara gasa amalin sarakuna,

Yara: Toron giwa ɗan Audu ƙanen Ali Ɗan’iya,

Jagora: Zuwan da kai Haji na Alu,

Jagora: Sai murna kaɗai mukai,

Yara: Sai babbar fata wadda akai sauka lafiya.

Jagora: Garin da kaz zo Mafara sai murna kaɗai akai,

Yara: Alƙalin Mafara yai tariyar baba makaye.

Jagora: Da mun zo Maru ko Banaga yai tariya.

Yara: Duk da mutane nai mun ka ishe zaune godabe,

Jagora: Sannu Banaga an sarki ya gaishe ka,

Yara: Sannu Banaga Allah shi yi ma albarka,

Yara: Sai wata rana ɗan mainasa babba ya wuce,

Jagora: Da mun ka tai Danmarke,

Yara: Mun ishe Sarkin Fillani Bunguɗu ya kawo,

Jagora: Duk da mutane nai sui tariyab baba makaye,

Jagora: Gasau da kaz zo Sarkin Kudun Gusau yai tariya,

J/Yara: Mai ‘Yandoto Gusau da shi da Kwatarkwasawa,

Yara: Ga Ƙaura ta kawo, ga kuma Zurmi da Moriki,

Jagora: Ga kuma Zurmi da Moriki ga kuma Isa Maradun,

Yara: Ga kuma Sabon Birni,

Jagora: Mamman ya kwana Gusau,

Yara: Ya isa Filin Jirgi,

Jagora: Ga sauran sarakuna,

Yara: Za su wurin ban kwana,

Jagora: Ga shi ga Sarkin Daura ga Alhaji Nasiru,

Ga kuma Sarkin Gwandu.

Irin wannan tariya babu wanda ake yi wa irinta in ba Sarkin Musulmi ba. A duba sosai, an tattaro sarakunan daular Zamfara da Gobir da Gwandu da Daura gaba ɗaya tarbon Sarkin Kudu. Anya! Ba Sarkin Kudu ne za a yi wa tarbo ba, kukan kurciya ne na kasancewarsa Sarkin Musulmi na gaba in Allah Ya so. Alhamdu lillahi Allah kuwa Ya so. Wannan kukan kurciya karatunsa sambai yake.

Hoton Sarkin Kudu Macciɗo a Karagar Sarautar Musulunci

Makaɗa Sa’idu dai ya yanke hukuncin Sarkin Kudu ya riga ya hau gadon sarautar Musulmunci a wata waƙar Sarkin Kudu da yake cewa:

Jagora: Toron giwa yana abin da ya kai,

: Ya shigo dawa.

Yara: ‘Yau namu suna ta gaisai,

Jagora: Suna ba da gaskiya,

Yara: Bil’amu na cikin sabara.

Jagora: Ya soke kainai,

Yara: Zomo ya taho ya wuce ya gai da toro.

Jagora: Shi yi yarda Allah ka wa kowa nagarta.

An riga an yi zaɓe, toron giwa ya kere kowa an zaɓe shi an naɗo sarakuna sun zo sun yi caffa. Babu ikon da zai rasa masu adawa, da ‘yan-ba-mu-so, ƙin miƙa wuya da Bil’amu ya yi, bai hana wa zomo zuwa ya yi caffa ba. Zomo ya yarda da cewa sarauta ta Allah ce, ba da ƙarfin tuwo ake zuwa a ɗebo ta ba. Wataƙila zomo ya tuna da karatun malamin gidansu Dr. Narambaɗa da ke cewa:

Jagora: Sarauta ban da nufin Allah ce,

Yara: Da ɗibat ta akan yi da ƙarfi,

Yara: Waɗanga da nag gaza ganewa,

Yara: Da sun ga ana haka nan da sun yi,

Jagora: Wane a dangana tun ga uwaye,

Yara: Ba duka ɗan sarki ba ka samun sarki.

Gindi: Gogarman Tudu jikan Sanda,

Maza su ji tsoron ɗan Maihausa.

Matsalar da Sarkin Kudu Zai Ci Karo da Ita a Zaɓe

Babu shakka a wajen Allah taskokin gaibi suke babu wanda ya san su sai shi kaɗai. Wannan ba za ta hana a furta wata magana ta yi daidai da wani gaibi ba, domin da mai maganar da gaibi, duk wanda ya yi gaibi, da mai magana, ya yi su. A bagiren nazarinmu sai muka kira shi “kukan kurciya”. Makaɗa Sa’idu Faru ya ce:

Jagora: Gurbin giwa sai ɗanta,

Yara: Zomo anka aza yab bar gidan na.

Da Sarkin Musulmi Abubakar III ya rasu (Allah Ya gafarta masa), sai Allah Ya ba, Sarkin Musulmi Ibrahim Dasuƙi (Allah Ya gafarta masa). Bayan cire Sarki Dasuƙi, sai Allah Ya ba Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo (Allah Ya gafarta masa). Da ya rasu sai ɗan Sarki Abubakar Muhammadu Sa’adu ya hau, har yanzu dai tana nan gurbin Sarkin Musulmi Abubakar kamar yadda Hausawa ke ce wa: “Ja ya faɗo, ja ya ɗauke”. Kukan kurciya a nan, fashin baƙinsa a bayyane yake.

Kirdadon Mutuwar Sarkin Kudu a kan Gadon Sarautar Musulunci

‘Yan maganganu da ke fita daga bakin makaɗa Sa’idu Faru game da Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo sun cancanci a nazarce su. Ni, a ɗan nawa bincike makaɗa Sa’idu Faru ya yi hasashen mutuwar Sarkin Kudu a kan abubuwa uku:

a.   Na farko a kan gadon sarautar Musulunci zai mutu.

b.   Na biyu jirgin sama zai kashe shi.

c.    Na uku Sa’idu Faru zai riga Sarki Macciɗo mutuwa.

Mu ɗan nazarci wannan ɗan waƙa cikin natsuwa mu ga saƙon yadda yake:

Jagora: Jirgi ya tashi bisa,

Yaro: Jama’a sai hwaɗin sukai,

Jagora: Lafiya dai ɗan Audu,

: Hattara da girgije.

Yara: Manya sun ishe manya,

: In ji mutanen Jidda.

Jagora: Suna ziyartar juna,

Yara: Bawan Allah jikan bawan Allah na Alu,

Jagora: Muna gare ku idan mun ka haɗe,

: Gobe lahira.

Fashin Baƙi

a.      A cikin jirgin sama ya yi haɗari su 100 suka mutu.

b.      Jirgin sai da ya tashi ya daidaita sama’u sosai ya yunƙura.

c.       Daidaitar jirgi a sararin samaniya an keta hazo a shiga giragizai.

d.     Zancen hattara da girgije ya yi canjaras da daidaitar jirgi a sararin Subhana.

e.      Manya sun ishe manya, ma’ana manyan duniya sun ishe manyan duniya da lahira (Allah), wato Allah Ya kira su.

f.        Ziyartar juna ishara ce da ba za a dawo ba, zaman duniya ya ƙare.

g.      Faɗar “bawan Allah jikan bawan Allah” ai ta’aziyya ce makaɗa Sa’idu ke yi na rashin uban gidansa. Allahu Akbar!

h.      “Muna gare ku idan mun ka haɗe gobe lahira” nuni ne ga Sa’idu zai riga wucewa, to in ya riske shi suna fatar samun ceto gobe lahira. Allah Ka cece mu!

i.        Rufe ɗan waƙar nan da faɗar “gobe lahira”. Kukan kurciya ne sai mai sani ka ganewa.

Sakamakon Bincike

a.   Kukan kruciyar makaɗa Sa’idu Faru a kan samun sarautar Ubangidansa Muhammad Macciɗo ta tabbata, ya zama Sarkin Musulmi na 19.

b.   Hasashensa na maye gurbin Sarkin Musulmi Abubakar daga cikin ‘ya’yan cikin Abubakar ta tabbata ga sarakuna biyu, Macciɗo da Sa’adu.

c.    Hasashen mutuwarsa ta sanadiyyarta da tazarar mutuwarsa tsakaninsa da uban gidansa ta tabbata. Allah Shi ne mafi sani.

Naɗewa

Na yarda da Hausawa suke cewa, duk abin da wayo ya ɓoye hankali na gano shi. Da yawa abubuwan da ke fitowa a bakunan mutane sai a ga sun zamo kamar an san da za su auku. A al’adance, tsananin soyayya ga wani abu, ko tsananin ƙiyayya gare shi, ko daɗewa tare da shi, ko cikinsa, na sa a ji zantuka barkatai da wasu daga ciki su kasance. Makaɗa Sa’idu ya rayu da marigayi Sarkin Kudu Macciɗo a zamanin da yake Sarkin Kudun Sakkwato. Ya yi masa waƙe-waƙe da yawa da fata daban-daban, waɗanda da yawa daga cikinsu Allah bai nuna masa su ba. Allah Ya yi rasuwar makaɗa Sa’idu Faru a matsayin makaɗin Sarkin Kudun Sakkwato Muhammadu Macciɗo Abubakar III haka kuma, Allah Ya yi wa Sarkin Kudu Macciɗo rasuwa a matsayin Sarkin Musulmi na (19) a daular Sakwkato. Allah Ya ji ƙansu da mu, Amin! A koyaushe ake tattauna irin wannan bagire na rayuwa a riƙa tunawa da tunanin Bahaushe da ke cewa, sanin gaibu sai Allah; maganar kowa jifa cikin duhu ce ta Allah kaɗai ce nashin ƙasa babu kure. Alhaji Umaru Nasarawa Wazirin Gwandu na cewa:

Wanda bai wuce shi yi kwana ba,

Bai wuce shi mance abinai ba,

Wanda bai san rabonai ba,

Yaushe za shi gano min nawa?

Manazarta

Bunza, A. M. (2009). Narambaɗa, Lagos: Ibrash Publication Centre 31, Adelabu Street.

Bunza, A. M. (2013). In ba ka San Gari ba Saurari Daka: (Muryar Nazari Cikin Tafashen Gambo) Cairo: Elkods Printing Press House.

Burton, S. H. (1954). The Critism of Poetry. London: Longoman.

Daba, H. A. (1978). “Hausa Oral Poetry: A Case Study of Adamu Ɗanmaraya Jos”, M.A. Thesis, Khartum: University of Khartum.

Ɗandatsi, A. (1975). “The Role of Oral Singer in Hausa/Fulani Society: A Case of Mamman Shata”, PhD, Thesis, Indiana: Indiana University.

Furniss, G. (1996). Poetry, Prose and Popular Culture in Hausa, International African Library, London: Edinburgh Library Press.

Gusau, S. M. (1983). Jagorar Nazarin Waƙar Baka, Kano: Benchmark Publishers Limited.

Gusau, S. M. (1988). “Waƙoƙin Makaɗan Fada: Sigoginsu da Yanaye-Yanayensu” Kundin PhD, Kano: Jami’ar Bayero.

Hamidi, M. F. (1992). “Garba Supa: Rayuwarsa da Waƙoƙinsa”, Kundin BA, Kano: Jami’ar Bayero.

Omar, Y. M. (1970). Kissar Annabi Yusuf, Zariya: NNPC.

Rasmussen, D. (1974). How Does A Poem Mean? New York: Houghten Mifflin.

Umar, L. D. (1981). “Sa’idu Faru da Waƙoƙinsa”, Kundin BA, Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.

Yahya, A. B. (1997). Jigon Nazarin Waƙa, Kaduna: Fisbas Media Services.

Sa'idu Faru

Post a Comment

0 Comments