Ticker

6/recent/ticker-posts

Jagoran Jawabi a Taron Karawa Wa Juna Sani Na Kasa Da Kasa Kan Rayuwa Da Wakokin Makada Sa’idu Faru

Jagoran Jawabi a Wajen Buɗe Taron Ƙasa Da Ƙasa Da Sashen Nazarin Harsuna Da Al’adu Na Jamii’ar Tarayya Ta Gusau, Jihar Zamfara Nijeriya Ta Shirya Domin Karrama Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo Sarkin Musulmi Na Goma Sha Tara (19), Ta Nazarin Waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru, Makaɗin Sarkin Kudu Macciɗo Da Wasu Manyan Sarakunan Ƙasar Hausa, Ranar 5/5/2024.

Ø  Ɗanmajisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar Ƙananan Hukumomin Maru da Bungudu, Hon. Abdulmalik Zubairu (Zannan Bunguɗu).

Ø  Shugaba da ‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Zamfara.

Ø  Maigirma Kwamishinan Ilmi na Jihar Zamfara, Alhaji Wadatau Mawaki.

Ø  Manya- Manyan baƙin da ke wakiltar Iyalan Gidan Sarkin Musulmi na Sha Tara (19), Alhaji Bello Muhammadu Macciɗo Abubakar na III.

Ø  Iyalan Gidan Alhaji Sa’idu Faru ƙarƙashin Jagorancin Makaɗa Ibrahim Sa;idu Faru.

Ø  Manya- Manyan masana na nesa da na kusa waɗanda suka samu damar halartar wannan taro.

Ø  Maimartaba Sarkin Zamfaran Anka kuma Shugaban Majalisar Masarautun Jihar Zamfara, Alhaji Attahiru Ahmad Muhammad (CON).

Ø  Wakilin Mai’alfarma Sarkin Musulmi Dr. Muhammad Sa’ad Abubakar III CFR, Sarkin Katsinan Gusau, Alhaji Ibrahim Bello OFR.

Ø  Babban Maimasaukin baki, Shugaban Jami’ar GwamnatinTarayya ta Gusau Farfesa Mu’azu Abubakar Gusau.

Ø  Masu Martaba Sarakunan Talatar Mafara, Maru, Kwatarkwashi da Shinkafi.

Ø  Sauran jama’a maza da mata.

Assalamu alaikum wa rahamatul lahi ta’ala wa barakatuhu.

Bayan gaisuwa ga manyan baƙi, an nemi in yi jawabi a kan taron ƙasa da ƙasa game da tarihin rayuwa da kuma waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru, Allah ya yi masa gafara, amin.

Haɗuwarmu a wannan bagire a yau, domin mu karrama Mai’alfarma Sarkin Musulmi na goma sha tara (19), ta fuskar nazarin waƙoƙin da Sa’idu Faru ya aiwatar zuwa ga Sarakunan ƙasar Zamfara da kuma waɗanda ya yi wa babban Ubangidansa Sarkin Kudun Sakkwato kuma Sarkin Musulmin Daular Usumaniyya (1996-2006).

Alu Maikurya Bagobirin da ya yi zamani da Sarakunan Daular Gobir yana yi musu kiɗan yaƙi. Bayan watsewar Daular Gobir, sai ya koma yi ma Sarakunan Zamfara kiɗan fada tsawon zamani, wannan shi ne kakan Sa’idu Faru. Domin shi Alu, mahaifi ne ga Abubakar Kusu, mahaifin Sai’du Faru.

Mahaifiyar Sa’idu sunanta Halimatu mutumniyar ƙasar Banga ce. Banga yanzu gunduma ce a cikin ƙasar Ƙauran Namoda, ta jihar Zamfara.

An haifi marigayi Makaɗa Sa’idu Faru a garin Faru, gundumar Masarautar Maradun da ke Jahar Zamfara a shekarar 1916.

Sa’idu Faru ya fara halartar fagaigan waƙar mahaifinsa yana ɗan ƙarami tun bai iya saka bante ba, wato bai san me ake ce ma waƙa ba (1920). Mahaifinsa yana yawo da shi gidajen Sarakuna bisa kuturin doki domin aiwatar da waƙa. Daga bisani sai ya zama ɗan karɓin waƙa. Duk wannan ya faru tun kafin Sa’idu ya kai shekaru bakwai da haihuwa. Har yana shaida wa Alhaji Hamza Sanusi Funtuwa wanda ya shirya wata tattaunawa da shi inda yake cewa ko da na fara zuwa amshin waƙa ina ɗan ƙarami har in nish sha hura cikina sai ya yi kamar tulu haka nan sai in yi ta kwana har a gama waƙa ban san an yi an gama ba (yayidariya).

Tun ina ɗan amshi har na fara jan ragamar waƙa. Sa’idu Faru bisa shawarar da suka yanke (tsayar) da ‘yan uwan haihuwarsa (Alhaji Mu’azu, da Mamman) cewa su dakatar da (hana) mahaifinsu yin kiɗa, domin a fahimtarsu mahaifinsu ya wuce a ce yana goggoriyon waƙa da shi da makaɗan wannan lokaci saboda shekarunsa sun yi nisa, sai suka hutar da shi da ƙarfi da yaji. Sakamakon haka ne, Sa’idu ya ɗauki shugabacin jagorancin ragamar kiɗan gidansu.

Waƙar farko da Sa’idu ya fara yi a matsayin mai cin gashin kansa ita ce ta Sarkin Yamman Faru Alhaji Ibrahim ɗan Sarkin Ƙayan Maradun Abubakar, wato ya fara da gida ke nan.

Kai ay yau ko gobe Maradun2x,

Turawa sun ba da wasiƙa,

Baabu mazan da ka ja maka2x,

jikan Atto bani Usumanu Atiku2x

Ruwa da Kada ɗibgau na Magaji2x,

Sai Tsofon wawa ka shi gar su,

Dawaya kora ɗimau na Wakili2x

 

Wato wannan ita ce waƙa ta farko da Sa’idu ya fara gabatarwa yana mai cin gashin kansa bayan sun dakatar da mahaifinsu daga kiɗa.

Daga Faru sai ya fara fita, inda ya mai da gabansa shi ne Banga, wato inda aka auro mahaifiyarsa. Sa’idu ya gadi Sarakunan Banga ta fuskar kiɗa a wajen mahaifinsa, saboda maihaifinsa ya yi wa Sarakunan Banga kiɗa cikinsu har da Sarkin Yaƙi Abdu. To sai Sa’idu ya fara da Sarkin Yaƙin Banga Saleh Abubakar, wanda ya yi Sarauta daga 1934-1963.

Daga nan sai Mesa tas so ta haɗe Sa’idu Faru. Domin Marigayi Maigirma Sarkin Kiyawan Ƙauran Namoda, Abubakar Garba (1952-1960) shi ya ɗauko Sa’idu daga Banga ya mayar da shi zuwa Ƙauran Namoda.

Daga can ne Zurmi suka ji amon Sa’idu Faru a lokacin Sarkin Zamfaran Zurmi Sulaiman Muhammadu Sambo (1951-1970). Wato yana Ƙaura, yana Zurmi yana komawa Faru.

Ana cikin wannan yanayi, sai ƙaddarar Allah ta riga fata, aka ɗauko Muhammadu Bello Macciɗɗo Sarkin Kudu ɗan Sarkin Musulmi Abubakar na III Allah ya gafarta musu, aka kawo shi Mafara a matsayin Uban ƙasa a shakarar 1953, wannan ne sanadin da Sa’idu Faru ya ji ƙamshin gidan Mujaddi, sai yas sheƙa da gudu zuwa Mafara yak kama Sarki Muhammadu Macciɗo. Ga abin da yake cewa a cikin ɗiyan waƙarsa da ke biye:

Mahamman dalilinka nis sanTalata,

Muhamman dalilinka niz zamni Hausa.

 Bayan an mayar da Marigayi Sarkin Kudu Muhammadu Bello Macciɗo garin Sakkwato a shekarar 1956, Sa’idu bai dai yarda a bar shi baya ba, sai ya sa takalminsa ya bi shi. Sakamakon shaƙuwa da soyayyar da ke tsakaninsa da ubangidansa har ta kasance Sa’idu Faru bai iya hita waƙa zuwa wani gari sai Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo ya amince. Za mu fahimci haka, domin ko a cikin waƙoƙin da ya yi wa Sarkin Kudu, wadda ya kira a matsayin bakan damiya mai gindin waƙa:

Kana shirye baban ‘yan ruwa,

Na Bello jikan Ɗanfodiyo

Wannanyaɗauke ta a matsyinbakandamiya tai ta Sarkin Kudu Macciɗo, ya ce duk inda yaj je hira, jama’a suna neman su ji wannan waƙa, to haka nan wannan tare tac cigaba ana ta yi.

Sa’idu Faru yana shiga wurare da dama, wasu wurare idan ya yi waƙa sai a yi tsammanin Sarkin Yanka ne aka yi ma waƙa. Misali a waƙar Sarkin Tudun Falale Marigayi Muhammadu Bala ɗan Sarkin Mafaran Gummi Muhammadu Maidabo

Sarkin Tudun Falale,

Gogarman Magaji Ummaru,

Ba yau ko mazan jiya sun san kana da martaba,

Ya riƙa da gaskiya Muhammadun Muhammadu,

Karsanin gidan Maisaje shirinka ya yi kyau,

Yac ce maihwadaɗaniyya,

Ga sarkin kiɗinku ya zaka,

na so a bani doki wani sansami abin suka,

Idan ka ji wannan waƙa za ka yi tsammanin sarkin yanka ne, to a lokacin shi Tudun Fafale marigayi Muhammadu Bala ɗan Sarkin Mafaran Gummi Muhammadu Maidabo, dagaci ne.

Haka ya kasance, wani lokacin sai ka ji kamar wannan sarki na ƙoƙarin tashi ya farma wata ƙasa lokacin da aka aika Sarkin Gabas Shehu ɗan Sarkin Bauran Dange Muhammadu Ɗangwaggo, ɗan Malam Usuman ɗan Sarkin Musulmi Mu’azu, ɗan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello, ɗan Mujaddadi Shehu Usmanu bn Fodiyo tammada hullahu bi Rahamatihi, a garin Talata Mafara a matsayin uban ƙasa. Shi ma akwai waƙoƙin da ya yi masa, sai ka yi tsammanin matsayin Shehun ya kusan kai ga na Sarkin Kano.

Madara da zuma na jekadiya Shehu,

Baaba, jikan Alu babba Maisaje,

Suna ta tsoronka, kai baka jintsoro,

Baba halin Abu yay yi Mai Rabah,

Mun yi hwarin-ciki, sai arerewa,

Da kar riƙa duniya ta yi kyau Shehu,

Yau Mahwara hwarautarmu ta yi nama,

Mun yi hwarin-ciki sai arerewa,

Mai biyas sarkin ƙauye wawa na,

Shi mi yac ci, mi za shi ba taro,

‘yaƙ ƙasa tai kwatancin ta Garbadu

Irin wannan sai mutane su zaci Sa’idu Faru ya yi ma Sarkin yanka waƙar ne.

Ana cikin irin wannan yanayi Sai ya soma zuwa Yawuri wurin Marigayi Maimartaba Alhaji Muhammadu Tukur Abdullahi (1955-1981) ciki ya yi maganganu masu hikima inda ya ke koɗa kansa, ya ce ga waƙa nan guda tara ta niy yi ma amma na baro takwas gida sai in ka yi murna da zakkuwammu, in aika ko yanzu su taho cewa da su waƙoƙin tara. Mu ka kiɗi in ji Sa’idu, don mu Allah yaw wa gudummuwa da waƙa har wata na ije wata, saboda isa irin ta Sa’idu Faru.

Daga Yawuri sai margayi Sa’idu yag gangara zuwa Kano, wajen Sarkin Kano Ado Bayero yay yi masa waƙa, yaw wasa shi. Daga Kano yaw wuce Zariya a lokacin naɗin Maimartaba Sarkin Zazzau Alhaji Dr. Shehu Idris a shekarar 1975, ya yi masa waƙa mai nuna yanzu shi ne babba a gidan Sambo. Ya ce Allah ya biya maka buƙata, kai ab babba a gidan Sambo.A nan ne ya ɗan shaguɓanci ‘yan Sarki yana cewa, da a ce ba a ba ni Sarki, gara a ba ni a yi mini gori, komi nij ji ban ji zahi ba.

Shi Sa’idu Faru waƙarsa sarauniyar waƙa ce, ta sarakuna, ba ya zuwa garkar kowa da turunai in ba sarki ko ɗan sarki ko mai riƙe da wata sarauta ba. Idan akwai to masana suna saurare.

Haka Sa’idu Faru ya cigaba da yi yana nan mallaƙe da Muhamadu Bello Macciɗo ɗan Sarkin Musulmi Abubakar na III ɗan Malam Usman ɗan Sarkin Musulmi Mu’azu, ɗan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello, ɗan Shehu Mujaddadi Tagammadahul lahu bi Rahamatihi.

Haka suka yi ta yi har zuwa lokacin da Allah ya yi ma Sa’idu Faru wafati a shekarar 1987. Cikin waƙoƙin Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo ya riga ya ba shi Sarauta. Shi gare shi Sarkin Musulminai ne. Don a cikin wata waƙarsa ta Macciɗo yana faɗin cewa:

Sarkin Musulmin wata ran kake,

Da Imani da mu’ijjiza

Na nan gun malamMacciɗo tun ga Alu mai Saje nij jiya

Ka kai kamab Bello sassakiya

Da kyauta da mulki da ban gaskiya

Haka za ka ji ya jero abubuwanshi, yana nuna ma mutanen duniya, shi fa garai Muhammadu Macciɗo Sarkin Musulminai ne.

Sarkin Musulmin wata ran ka ke, sai ga wata ranar ta faru Allah bai gwada ma Sa’idu Faru ba, Allahu Akbar!!!.

Wato taren Sa’idu Faru da Muhammadu Macciɗo ta kai tare ta kai ƙud da ƙud, domin a wata tattaunawa da na ji an yi da shi a gidan Rediyon Jihar Kaduna (KSMC) a ranar 15/8/1970 karkashin jagorancin Malam Hamza Sanusi Funtuwa yana tambayarsa kamar haka:

Malam Hamza: To wai kai Sa’idu kullum sai in ji kawai kullum kana maganar Sarkin Kudu Macciɗo, shin Sarkin Kudun ga shin wane ne nashi?

Sa’idu Faru: At! Kai ranka ya daɗe ba ka san Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo ba?

Malam Hamza: Ah a ah

Sa’idu Faru: Shin wane gari kake?

Malam Hamza: A Funtuwa nike.

Sa’idu Faru: Af toh kai ba ni mamaki, da Katsina kake da sai in ce Sarkin Kudu ya amshe tutan nan ta Mujaddadi da anka bayat Katsina, amma tunda Funtuwa kake, ba ni ganin laihinka.

Don Sarkin Kudu Macciɗo saboda adalcinshi, to ni ina ganin ni ban ma san abin da zance ma ba, don ni ban da shi, ban san kowa ba.

Ga shi a cikin waƙoƙinai yana faɗin

Ban wuce gonata da irina ba,

Inda Sarkin Kudu nits tsaya

Saboda haka wannan tare ta haifar da alkhairurrukkah (alkhairai)

Saboda Sarkin Kudu Macciɗo,

Mun san manya mutane ƙwarai,

Mun san ƙananan mutane kuma,

Mu shidda, ni da makaɗana muna kammale

Kowa ta shi ƙawa ta isai,

Sarkin Makaɗa yay taiɓa yay ƙaton ciki,

Kowag gam mu zanne ga inuwa,

Ko da Makaɗin Sarkin Masar yag,

Ga Sa’idu sai rai nai yay haki.

To yanzu wani abin al’ajabi da ya faru, da niƙ ƙirga ainihin ƙungiyar Sa’idu wadda khalifansa Malam Ibrahim Sa’idu ke jagoranta sai nig ga su bakwai ne, nic ce ahah, ikon Allah, ko gado ne?

Bayan wafatin Sa’idu Faru a 1987, ya bar matan aure biyu,ya bar ɗiya sha biyu (12) Shidda maza shidda mata cikinsu hadda shi wannan Malam Ibrahim ɗin

Taren ba ta ƙare ba tskaninsu da shi Sarkin Kudu Macciɗo. Shaidu ni ke watan Apirilu na shekarar 1996 lokacin da Allah ya tabbatar ma da Sa’idu fata tai, ga Sarkin kudu Muhammadu Macciɗo, Gwamnatin Jahar Sakkwato a ƙarƙashin jagorancin Kanal Yakubu Mu’azu (Ritaya) ta faɗi cewa an bai wa Muhammadu Macciɗo sarautar Sarkin Musulmi na 19, Shi Ibrahim Tabbas a gabana yaz zo da turaye, ya yi waƙoƙi waɗancan da suka yi tare da mahaifinsa yak kuma yi nashi, yana cewa:

Sarkin musulmi Macciɗo

Muhammadu Ɗan Bello,

Gidan Mamman Bello duk yau yana hannunka,

Muhammadu Ɗan Bello

Gidan Mamman Bello duk yau yana hannunka,

Wato wannan na nuna ainihin tare, waccan tare ce da ankayi da mahaifin Ibrahim da Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo tun shi na Sarkin Kudu, bai yanke wannan tare ba.

Yanzu ga mu tare da Maigirma Ubandoman Sakkwato, Hakimin Sabon Birni Alhaji Malami Sheik Muhammadu Macciɗo sun zo saboda girmamawa da karramawa,da mutuntawa, na tabbatar da shi Malam Ibrahim ƙila bai rasa ce ma Ubandoma wani abu ba don wannan tare ta ƙara tashi.

Da wannan nike cewa masananmu da suka taru zuwa anjima zai baje koli wanda zai sa a samar da wani kundi wanda ba za a mance ba, wanda zai koma abin bibiya domin tuna rayuwa da kuma fasahohin Marigayi Sa’idu Faru ɗan Abubakar Kusu, ɗan Alu Mai Kurya, Bagobirin da yac canye Zamfarawa.

Wassalamu Alaikum wa rahmatul lahi ta’ala wa barakatuhu.

Sa'idu Faru

Post a Comment

0 Comments