Citation: Tambawal, A.Y. (2024). “In Ka Ƙi Ji Ba Ka Ƙi Gani Ba”: Nazarin Mummunan Ƙarshe ga Masu Miyagun Halaye a Cikin Wasu Fina-finan Hausa. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 521-527. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.064.
“IN KA ƘI JI BA
KA ƘI GANI BA”: NAZARIN MUMMUNAN ƘARSHE GA MASU MIYAGUN HALAYE A CIKIN WASU FINA-FINAN
HAUSA
Na
Aishatu Yahaya Tambawal
Sasehn Nazarin Hausa, Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari,
Sakkwato
Tsakure
Mummunan ƙarshe, wani ɓangare wanda rayuwa kan samu kanta a ciki a sanadiyyar
aikata wani mugun hali, lokacin gudanar da rayuwar da ta gabata. Wannan na iya
kasancewa a bayyane cikin zahiri ko a fina-finai. Wannan takarda ta waiwayi
yadda fina-finan Hausa a matsayinsu na wasan kwaikwayo sukan fito da mummunan ƙarshe ga mutanen da suke aikata miyagun halaye a cikin
tsarin fim. An yi sharhin fina-finan tare da nuna yadda ƙumshiyarsu take cike da kwaikwayon halayyar mutane kai
tsaye ko a kaikaice domin isar da saƙo ga al’umma. Bugu da ƙari, takardar ta
nuna yadda waɗannan fina-finai sukan ilmantar ta hanyar yin gargaɗi da kashedi da
hannunka mai sanda ga al’umma domin su guje wa aikata miyagun ayyuka da nufin
kauce wa aukawa cikin mummunan ƙarshe.
Fitilun Kalmomi:
Mummunan Ƙarshe, Miyagun Halaye, Fina-finan
Hausa
Gabatarwa
Masana da manazarta da dama sun ba da gudunmmuwa daban-daban
a kan fim da amfaninsa da illolinsa ga rayuwar al’umma. Ɗaya daga cikin muhimmancin fim ga rauwar al’umma shi ne, faɗakarwa da wayar da kan al’umma da kuma ilmantar da su a kan ɓangarori daban-daban na rayuwa. Kamar yadda bayanan masana
suka nuna, fim ya samo asali ne daga wasan kwaikwaiyo wanda a yau ya kai ga
wani babban mataki cikin al’ummar Hausawa. Bincike ya nuna cewa wasan kwaikwayo
ko kuma fim kutse ne da Bahaushe ya sami kansa a ciki, wanda ya sababba
canzawar wasu al’adunsa da adabinsa na dauri waɗanda
ya gada kaka da kakanni. Domin samun isar da saƙon wannan takarda, an kawo ma’anar fim da tarihinsa da kuma
wasan kwaikwayo. Haka kuma, an tattauna a kan miyagun halaye da ake samu cikin
fina-finai da kuma mummunan ƙarshen
da ke biyowa baya ga masu aikata irin waɗannan
miyagun halaye. Takardar ta samu nasarar hakan ne ta hanyar kawo misalai da yin
sharhin wasu fina-finan Hausa masu nuni da faɗakarwa
ga irin waɗannan halaye. Takardar ta yi ƙoƙarin kammalawa ta
hanyar kawo sakamakon bincike da manazarta da kuma ratayen wasu
fina-finai.
Bitar Muhimman
Ayyuka
Wasu daga cikin muhimman ayyuka masu alaƙa da wannan bincike da aka ci karo da su, akwai Adamu (2002)
bincike ne da aka gudanar a kan matsayin mata cikin fina-finan Hausa. Yayin da
aikin Hassan (2012) ya bibiyi takaicin mata a fina-finan Hausa. Shi kuma Zango
(2021) ya yi aiki a kan zamantakewarmu a yau. A cikin wannan aiki mai binciken
ya nazarci fim ɗin Babban Gida. Binciken Aminu (2012) ya fuskanci raha a
wasan kwaikwayon Hausa. Aikin ya yi ƙoƙarin Kwatance
tsakanin Wasannin Karambana da na Dan’ibro.”
Akwai aikin da suka yi inda aka tattara mukala aka buga a
matsayin littfin wanda ya Wannan littafi ya taskace takardun da aka gabatar a
wani babban taro aka sha’nin film aka mayar da su a matsayin littafi. Magaji
(1999) aiki ne da ya waiwayi matsayin kunya da mutunta jama’a cikin al’adar
Bahaushe. Shi kuwa Abubakar (2012) ya yi nazarin keɓaɓɓun kalmomin fim da sinima da majigi. Akwai kuma aikin Waya
(2021) a bayabayan nan ya waiwayi tsarin jumla da kalmomin ‘yan fim a harshen
Hausa.
Mene Ne Fim?
Yana da matuƙar
muhimmanci kafin a bayyana tarihi fim a san ma’anar shi kan shi fim wato, idan
aka ce fim me ake nufi?
‘Yar’aduwa (2007:30) ya bayyana ma’anar fim kamar haka:
Fim hikma ce mai motsi da take ɗauke da mutane, (wato hotonansu maza ko mata, yara ko manya)
ta amfani da na’urar ɗaukar hoto ta musamman tare da baiwa mutanen (kowanensu)
damar aiwatar da wasu ayyuka ta fuskar kwaikwayo ko waninsa, a wani lokaci da
aka keɓe, wanda shi wasan kwaikwaiyon yake ɗauke da wani saƙo na musamman kan nishaɗi da
wa’azi da soyayya da tarihi ko wanin haka, zuwa ga al’ummar duniya.
Daga wannan ma’ana, ana iya fahimtar cewa fim wani ɓangare ne na hanyoyin sadarwa na zamani wadda take samar da
gani da ji da motsi, domin amfani ga mutane masu yawa ta harshen da kowace
al’umma take iya fahimta.
Babbar manufar fim ita ce samar da nishaɗi da faɗakar da al’umma,
yayin da masu aiwatar da fina-finan sun ɗauki
hanyar a matsayin aiki ko sana’a kamar yadda kowane aikin hannu yake, wato dai
sun ɗauke shi a matsayin hanyar samun abin masarufi ko abinci.
‘Yar’aduwa; (2007:38).
Tarihin Samuwar
Fim
Fim yana da daɗaɗɗen tarihi a ƙasashen
Turai. Ya fara samuwa ne a daular Girkawa da Romawa. Bayanai sun nuna cewa fim
a wancan lokaci ana aiwatar da shi ne domin nishaɗi
ga sojojin da ke fagen fama da kuma manyan mutane domin a ɗebe musu kewa. A wannan lokaci, makaɗa da mawaƙa
da masu maganganun hikima da tatsuniyoyi da sauransu sun yi fice a wannan
zamani (Adamu, 2004:83-99).
Tarihi ya nuna cewa an fara samar da fim a Nijeriya a
shekarar 1903, a wajajen wannan lokaci ne aka nuna fim na farko a Ikko (jihar
Lagos) a ɗakin taro na Harbert Macauley (Opobo, et al 1979:2). Daga
baya gwamnatin mulkin mallaka a shekarar 1912 ta gabatar da ƙa’idojin aiwatar da fim. Wannan doka ita ta hana aiwatar da
kowane irin wasan kwaikwayo ko sinima har sai ya cika sharuɗɗan da gwamnatin ta gindaya. Wato, sai an tace fim a muhallin
da gwamnati ta ba wa lasisi (umurni) (Ugor, 2007:2), duk wanda ya karya wannan
doka ya gamu da fushin gwamnati. A inda aka fito, harkar aiwatar da fim da
gudanar da shi a wannan lokaci tana hannun baƙi. Su suke shigowa da fitar da fina-finai a Nijeriya. Haka
aka ci gaba har bayan da Nijeriya ta sami ‘yancin kai. Wato, ‘yan ƙasar Labanon (ƙwarori) da Indiyawa su suke riƙe da wannan harka ta fim.
Galibi, jigogin fina-finai a wannan lokaci ba su wuce nuna
muhimmancin shugabanni ‘yan mulkin mallaka a kan ‘yan ƙasa. Turawan sun yi haka ne domin su ƙara samun damar shanya garinsu don cimma burinsu. Don haka,
kasancewar rashin cikakkun ‘yan ƙasa a wannan lokaci a harkar fim ya faru ne saboda burin
Turawa ‘yan mulkin mallaka na mulkin al’umma bisa tsarinsu da tunaninsu. Bugu
da ƙari, dokar da suka kafa a shekarar 1912
ta hana ‘yan ƙasa samun damar
shiga kowace irin harka ta fim, ko da kuwa kasancewa cikin masu taimakawa wajen
aiwatar da wasu harkoki ne na fim (Okome Hynes, 1997:29)
A shekara ta 1933 aka gabatar da hukumar kula da fim ta ƙasa wadda ta ɗauki
alhakin kula da fina-finan da ake yi na ƙasa da kuma waɗanda
aka shigo da su (Ugor, 2007).
Bayan an sami ‘yancin ƙasa a tsakanin 1960 zuwa 1970, shugabannin wannan lokaci sai
suka sake bibiyar tsarin fim aka sanya shi ƙarƙashin jerin
tattalin arzikin ƙasa a tsakanin
tsarin siyasa da al’adu da ayyukan hannu. Ekwuazi, (1991) ya bayyana cewa a
shekara ta 1963 aka fitar da ƙa’idoji
da dokoki na shirya fina-finai. Kula da waɗannan
dokoki yana ƙarƙashin ofishin babban Ministan Al’adu na gwamnatin tarraya.
Ga jerin ƙa’idojin da aka
gindaya na shiryawa da samun karɓuwar
fim na gida da na ƙasashen waje,
kamar haka:
•
Kada
ya kasance fim ɗin zai kawo hatsaniya ko rikici ga al’umma
•
Kada
ya kasance akwai ɓatanci ko nuna cin rashawa
•
Kada
ya kasance ya karya dokar ƙasa
ko aikata laifuffuka
•
Kada
ya kasance an muzanta ‘yan Afirika da sauran ɗabi’unsu.
•
Kada
ya kasance an nuna ƙabilanci da
bambacin addini da abin da zai jawo tashin hankali, (Ekwugzi, 1991: 158).
A shekarar 1987 aka haɗa
wannan bayani a matsayin “rahoton bayan taro” wanda ya ƙunshi ilmantarwa da faɗakarwa
tare da nishaɗantarwa wajen aiwatar da fim. Wato shi ya tabbatar da yunƙurin da gwamnati ta yi wajen ci gaban al’adu da haɗin kan ‘yan ƙasa
gaba ɗaya. Duk da haka, a ‘yan lokuta wannan ƙuduri ya wargaje da wasu dalilai da suka shafi siyasa.
A shekarar 1993 aka samar da Hukumar Tace Fina-Finai da
Bidiyo ta Ƙasa (wato,
National Films and Ɓideo Censorship
Board (NFWCB). Wannan hukuma ta fara aiki a ƙarƙashin dokar da aka
kafa ta ƙasa, wadda ta
shafi aikin gudanar da fina-finai ta shekarar 1963-64 mai lamba 85, wadda aka
rubuta a tsarin kundin ƙasa mai lamba 20
(kundi na 80) ranar 1 ga Satumba, 1993 (Ugor, 2007). Kafin wannan lokaci an
fara samun fina-finai saboda dalilai da dama waɗanda
suka shafi harkar siyasa da gurɓatar tattalin arziƙin ƙasa da
zamantakewar al’umma a tsakanin shekara ta 1980 zuwa 1990 (Lawuyi, (1997:12);
Okome and Hynes, 2000:12); Okome, (1997:12); Adesanya, (2000:12); Ukadike,
(2001:12) da Ogunleye, (2004:12).
Ko da yake, duk da cewa an kafa waɗannan hukomomi na kula da harkar fim a Nijeriya, amma ba ta
sake zane ba. Hukumomin kwastan a gabansu ake wucewa da fina-finai waɗanda ba su dace ba, kuma ba tare da sun hana ba. Waɗannan al’amura da makamatansu sun daɗa kashe fina-finan da ake aiwatarwa a cikin gida, hasali ma,
su suka kashe na gidan.
Gabatar Da Wasan
Kwaikwayo A Taƙaice
Dangane da wasan kwaikwayo ana iya cewa: “Ranar bikin farar
kaza balbela ba gayya ce ba”. Masana da dama sun tofa albarkacin bakinsukan
wannan batu. Alal misali, inda ya nuna
wasan kwaikwayo shi ne kwaikwayon wani mutum ko kuma wasu mutane lokacin da su
ke yin wani aikin. Shi kuwa Yahaya (1978:44) nuna cewa, tun daga jin sunan
“wasan kwaikwayo” ya riga ya bayyana kansa, wato akwai kalmar “wasa”, wato abin
da ba gaskiya ba ko raha. Akwai kuma kalamar “kwaikwayo”, wato aikata wani abu
don kwatanta yadda ake yin sa.
A fahimtar Crow (1983:2) wasan kwaikwayo wasa ne inda ‘yan
wasa kan sauya kama da aikata wasu ayyuka idan an tattarasu su suke haifar da
labari don nishaɗantar da masu kallo. A ra’ayin Ado, (1994) cewa ya yi,
“wasan kwaikwayo yana nufin kwatance a kan rayuwa ta yaƙini, musamman ma ga shi ɗan’adam
ta kwaikwayo yake koyon muhimman tadawulin rayuwa kamar magana ko sana’a. Wasan
kwaikwayo yakan doshi matsalolin rayuwa ne kai tsaye ya yi musu
hannunka-mai-sanda. Ado U. (1994).
Shi kuma ‘Yar Aduwa (2007), cewa ya yi, “wasan kwaikwayo
kamance ne na wasu halaye ko na yanayin rayuwa wanda masu hikima sukan shirya
gudanar da shi ta hanyar annashuwa da raha da nishaɗi don cim ma wata manufa”. Haka kuma ya ƙara da cewa, “Wasan kwaikwaiyo ya ƙunshi duk wani wasa da waɗansu
suke koyi da halaye ko ɗabi’un wasu mutane domin masu karatu ko kallo”.
Ɗangambo (1984) yana cewa:
Wasan kwaikwayo, kamar yadda sunan ya nuna, wasa ne da ake
gina shi a kan wani labari ko wata matsala ta rayuwa da ake aiwatar da shi a
sifa ta zahiri domin nuna wa jama’a.
A bayanin Ahmed (1987) ya nuna cewa fim ya samo asali ne
daga wasan kwaikwayo, kamar yadda yake cewa: “Wasan kwaikwayo da aka fara yi
wani mutumin Kano ne ɗan kasuwa, da ake kira Haji Ahmadu masu kwani Kano wanda ya
rubuta a shekarata 1902”.[1]
Daga ma’anoni da bayanan da aka gabatar a sama, ana iya
fahimtar cewa, wasan kwaikwayo ya taka muhimmiyar rawa wajen samar da
fina-finai, musamman idan muka duba shahararren littafin nan da Baturen nan Mr.
R. M. East ya rubutawa a shekarar 1932, mai taken The siɗ Hausa Plays. Bayanai sun nuna cewa wannan littafi ya samu ne sakamakon
kafa Hukumar Ɗab’i da Fassara ta
Ƙasa, wadda gwamnati ta kafa a shekara
ta 1929 inda aka buƙaci ‘yan ƙasa su yunƙura
domin aiwatar da fassara a ƙarƙashin jagorancin Mr. C. E. J Whitting.
Bugu da ƙari,
an fassara litattafai da dama da suka haɗa da Wasan Marafana Alhaji Abubakar Tunau da
kuma Zamanin Nan Namu na Shua’ibu Maƙarfi (Yahaya, 1988:96).
Don haka wasannin kwaikwayo na dandamali da wasannin
gargajiya sun taka muhimmiyar rawa wajen samuwar fina-finan Hausa.
Me Ake Nufi Da
Miyagun Halaye?
A Hausa, idan aka ce wa mutum ‘mugu’, ana iya siffanta shi
da, cuta ko ƙeta ko zalunci ko
cin amana. A ra’ayin Sa’id (2006:348) anba da ma’anar ‘mugu’, shi ne “Mutum mai
mummunan hali na cuta, daidai da macuci ko ɓarawo
ko ƙwaro”. Watau ‘miyagu’ jam’i ne na
kalmar ‘mugu’. Haka kuma, kalmar ‘mugu’ tana nuni ga hali ko ɗabi’ar da mutum yake yi koyaushe, halinsa ne, wanda kowa ya
san shi da shi. Don haka, a taƙaice
miyagun halaye su ne ke sa mutum ya zamo wata siffa a cikin al’umma wanda ake
yi masa wani kallo na rashin kamala na zama cikakken mutum mai halayen kirki.
Akwai miyagun halaye da dama waɗanda Bahaushe ke
kallon ɗan’uwansa da su a matsayin mutumin da ba shi da hali mai
kyau, kamar sata da ƙeta da zalunci da
hasada da cin amana da ƙazafi da ƙarya da zamba da kishi da sauransu.
Waɗannan duk halaye ne da ake iya duba mai aikata su a matsayin
mutum mai miyagun halaye a cikin al’umma. Haka kuma, sukan sa mutum ya zama
abin ƙyama ga iyayensa
da danginsa da maƙwabtansa
‘yan’uwansa da ma sauran al’umma baki ɗaya.
Me Ake Nufi Da
Mummunan Ƙarshe?
Wannan kalma ta ‘mummuna’ ta bayyana kanta, saboda da
Bahaushe ya ji an ce mummuna ya san abu ne maras kyau. Don haka, ana samun
mummunan ƙarshe ne a
sakamakon aikata wata ɗabi’a ko wanzar da wani hali maras kyau. Sa’id (2006:350) ya
bayyana kalmar ‘mummuna’ kamar haka:
Abu maras kyan gani ko magana maras daɗin ji
Don haka, akan samu mummunan ƙarshe na rayuwa sanadiyyar aikata wani mugun hali a cikin
mu’amala ko zama da mutane. A cikin Suratul Zalzala (99: 7-8) Allah (SWT) ya yi
nuni ga aikata alheri bisa ga aikata sharri. Ayoyin sun bayyana cewa idan mutum
ya aikata alheri, komai ƙanƙantarsa zai ga alherin. Idan kuma ya aikata sharri, komai ƙanƙantarsa zai ga
abinsa a ƙarshe.
Daga waɗannan bayanai, ana
iya taƙaitawa da cewa,
mummunan ƙarshe na zuwa ga
mutanen da ke aikata mummunan aiki. “Bahaushe kan ce, “Ba ka shuka gero ka
girbi shinkafa ba.” Wannan magana gaskiya ce. Koyaushe Bahaushe kan yi amfani
da karin magana domin faɗakarwa ga jama’a domin su kiyaye.
Miyagun Halaye da Ƙarshensu a Wasu Fina-Finan Hausa
Miyagun halaye, ɗabi’u
ne da ake shiryawa a cikin fina-finan Hausa domin su zama manuniya ga masu
kallo ko saurare. Ana shirya waɗannan wasannin
domin su yi hannunka-mai-sanda ga masu aikata irin halayen da aka kwaikwayo ta
hanyar nuna wa jama’a yadda ƙarshensu
ke kasancewa sanadiyar zalunci ko cin amanar da suka yi a baya. Wannan maƙala ta kalato wasu fina-finan Hausa masu nuni ga mummunan ƙarshe a cikinsu domin tattaunawa. Alal misali a cikin fim ɗin Aljannar Mace (2000) na Kamfanin Tumbin Giwa Kano, an
nuna halayen surukai marasa kyau musamman iyayen miji masu musgunawa da
takurawa matan ’ya‘yansu. An kawo Hajiya a matsayinta na mahaifiyar Ishaƙ, shi kuma yana da matarsa Salma. Ishaƙ yana son matarsa matuƙa, ita ma tana sonsa sosai. Suna zaune cikin so da ƙauna, har ya kasance saboda ƙauna yakan taya matarsa a aikace-aikacen gida ita kuma ya ce
ta zauna ta huta, musamman lokacin da ta fara laulayin ciki. Amma Hajiya ta
hana ta sake wa a rayuwarta ta aure. Takan zo gidan ta ci mutuncin Salma, ta
hana su sakewa. Girki ma, sai ta ga dama za a yi a gidan. Ya kai ma har Hajiya
ta kulle ɗakin girki da ma’ajiyar abincin gidan wai ta rinƙa aiko musu da abinci daga gidanta. Duk irin abubuwan da
Hajiya ke yi wa Salma, zagi da cin mutunci, Salma ba ta taɓa ɗaga kai ta kalle ta ba, ballantana ta faɗi marar daɗi, sai dai abin
yana damunta, haƙuri kawai take yi,
har abin ya zame wa Salma jiki.
Duk irin waɗannan abubuwa ba
su ishi Hajiya ba, sai da ta nemo wa Ishaƙ yarinya wai sai ya ƙara aure. A cewar Hajiyar, tana zargin matar ɗanta Salma da bin maza take yi a waje idan ta fita aiki. A
sanadiyyar wannan magana, Salma hawan jini ya kama ta, ta kwanta a asibiti na
tsawon watanni tana jinya. Kafin ta fito, sai da Hajiya ta saka Ishaƙ ya auri ‘yar ƙawarta, wai don dai ya wulanƙanta Salma. Da amarya Fati ta zo, sai ta riƙe Salma da ɗanta Mujahid
(wanda Hajiya ta tsanta) hannu biyu-biyu, kamar ita ta haife shi. Komai Mujahid
yake so, Fati ke yi masa. Hajiya ta hana ta, amma ta ƙi ji, ta ce ai duk ɗaya
ne. Da Hajiya ta ga haƙarta ba ta kai ga
gaci ba, sai Hajiya ta tafi gidan su Fati, ta gaya wa iyayenta cewa, su tashi
tsaye, domin Salma ta mallake miji ta kuma mallake musu ‘ya, sai abin da take
so ake yi a gidan, don haka su nemi magani. Duk da ta ga wannan bai yi mata ba
sai kuma ta faɗa neman magani. Har ta ci sa’ar nakasa Salma, a sanadiyyar
magani da Hajiya ta rinƙa zuba wa Salma
cikin abinci. A ƙarshe abin da ta
so ya faru ga Salma sai ya faɗa kanta, ta ɗimauce, daga ƙarshe ta mutu. Ita ma Fati ta ci maganin da Hajiya ta zuba
wa Salma a abinci, ta mutu.
A fim ɗin Butulci (1999) na kamfanin Danfodiyo Production Sokoto,
ya nuna yadda Maryam ta shiga halin ƙunci tun tana ƙarama. An nuna cewa suna cikin mota a hanyarsu ta zuwa ƙauye tare da iyayenta da ƙannenta, ɓarayi suka tare
su. A wurin nan ɓarayin suka kashe duk wanda ke cikin motar, sai ita kaɗai ta tsira. Maryam ta gudu cikin daji ta zauna, inda Allah
ya haɗata da Sadik wanda ya taimake ta ya kai ta gidansu wajen
mahaifiyarsa. Bayan ta huta, ta ba su labarin yadda aka yi ta zo daji. Sadik ya
ce, ta zauna tare da su, amma mahaifinsu ya rasu, shi kuma lebura ne, amma zai
yi bakin ƙoƙarinsa ya riƙe
ta.
Suna zaune a haka, har soyayya ta ƙullu tsakanin Maryam da Sadik, har ma da alƙawalin aure. Kwatsam sai Maryam ta haɗu da Alhaji Kabir ya hure mata kunne. Ga yadda tattaunawar
ta kasance:
Sadik: |
Yanzu mama, daidai ne a ce wai Maryam tana fita a motar
Alhaji Kabir, har sun fara yin magana. |
Maryam: |
Wai magana ake yi da ni ne? |
Sadik: |
I, maganarki ake yi.
Mene ne tsakaninki da Alhaji Kabir? |
Maryam: |
Wannan bai shafe ka ba. |
Mama: |
Ni ba wannan yake damuwata ba, yawace-yawacen da take yi
safe da yamma. |
Maryam: |
Ni ba inda nake zuwa. |
Sadik: |
Wato mama tana yi miki ƙarya ko? |
Maryam: |
I, ƙarya
ake yi mini, tunda ban yi ba. Zan tafi gidan Alhaji Kabir da yamma, |
Zan tura a kwasar mini kayana, saura kuma a yi mini sata.
Kwaɗayi mabuɗin wahala, Maryam
dai kwaɗayin abin duniya ya ruɗe ta
har ta ɓata da iyayen da ta samu suka rufa mata asiri, bayan da ta
rasa iyayen da na asali. Bayan ta koma gidan Alhaji kabir ba da daɗewa ba, sai ‘yan sanda, suka zo gidan bincike, ashe Alhaji
Kabir shugaban ‘yan fashi ne. Yaransa ne ma suka kashe mata iyaye ba ta sani
ba. Don haka, aka yi gaba da shi da duk abin da ya mallaka. Nan fa Maryam ido
ya raina fata. Ta rasa wurin zuwa, ta dawo gidan su Sadik amma suka ƙi karɓar ta. Sakamakon mugun halinta ya ci ta.
Sakamakon Bincike
Wannan takarda ta gano cewa akwai fina-finam Hausa waɗanda ke ɗauke da muhimman
abubuwa da suka shafi rayuwar al’umma. Takardar ta yi sharhi a kan fina-finan
da suke yi wa al’umma hannunka-mai-sanda, da su guji aikata munanan halaye irin
na Hajiya (a cikin fim ɗin Aljannar Mace) da kuma Maryam (a cikin fim ɗin Butulci). Hausawa na cewa, “Komai nisan dare, gari zai
waye.” Ma’ana, dukkan mai aikata munanan halaye ba zai ƙarshe mai kyau ba.
Kammalawa
Wannan maƙala
ta yi taƙaitaccen bayani a
kan fim, tun daga ma’anarsa da tarihin samuwarsa da kuma rawar da wasan
kwaikwayo ta taka wajen samuwar fim. Haka kuma, an kawo gabatar da bayani a kan
miyagun halaye da mummunan ƙarshe
tare da nazari da sharhi yadda waɗannan
abubuwa suke zuwa a cikin tsarin fina-finan Hausa. Bugu da ƙari, a cikin fina-finan an nuna yadda ƙarshen masu aikata miyagun halaye suka kasance a cikin
fina-finan. Wannan kuwa yakan zo ne a fina-finan domin tunatarwa da faɗakarwa da kuma hannunka-mai-sanda ga al’umma. A ƙarshe, wannan takarda tana kira da ɗalibai da manazarta da su shigo cikin finafinan Hausa don
tsamo irin albarkatun ilmuka da faɗakarwar
da ke ciki.
Manazarta
Abubakar, Y. (2012). “Keɓaɓɓun Kalmomin Fim da Sinima da Majigi.” Kundin digiri na ɗaya. Zariya: Jami’ar
Ahmadu Bello.
Adamu, N. M. (2002). ‘Mata Cikin
Fina-finan Hausa”. Kundin digiri na biyu. Kano: Jami’ar Bayero.
Ado, U. (1994). “Nason Adabin Baka
Cikin Rubutaccen Wasan Kwaikwayo”. Kundin Digiri na Biyu. Kano: Jami’ar Bayero.
Adesanya,A (2000). From film to ɓideo Nigerian ɓideo
films (Eds) Jonathan Hynes, center of international studies, ohco: Jos.
Ahmed U.B (1987). A critiƙueof an early (1902) Hausa Dramatic literature: A paper
presented at the 4th international ANNUAL Conference of Linguistics
at Bayero Uniɓersity, Kano
Aminu, H. (2012). “Raha a Wasan
Kwaikwayon Hausa: Kwatancin Wasannin Karambana da na Dan’ibro.” Kundin digirina
uku. Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.
Aristotle (1907). “Poetic” (Dramatic
theory) published in 1895. (Eds) sarmuel Butcher Books, Google.com
Crow B (1983). Studying Drama Nigerian
longman publishing L.t.d
Ɗangambo, A.
(1984). Rabe-raben Adabin Hausa Da Muhimmancinsa Ga Rayuwar Hausawa. Kano:
Triumph Publishers.
Ekwuazi, H. (1991). Film in Nigeria
Nijeria film: corporation Jos: Jos Nigeria.
East, R.M (1930). The Siɗ Hausa Plays. Zaria:
Hukumar Fassara.
Gummi, A. M. (1982) Alƙur’ani mai Girma Tarjamar ma’anoninsa. Beirut, Lndon: Daral
Arabiya.
Hassan, B. M. (2012). “Takaicin Mata a
Fina-finan Hausa.” Kundin digiri na biyu. Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.
Lawal, S. (2021). “Kwatancin Kishi a Fim Ɗin Ɗakin Amarya Da Na
Matar Mamman.” Zaria: Kundin Digiri na
Farko. Sashen Harsuna da Al’adun Afrika, Jami’ar Ahmadu Bello.
Lawuyi, B. O (1997), the political
economy of ɓideo marketing in ogmosho: Nigeria Africa 67:3 to.
Magaji, A. (1999). “Kunya da Mutunta
Mutane a Al’adar Bahaushe.” a cikin Hausa Studies, No. 1. Kano: Jami’ar Bayero.
Ogunleye. F, (2004). A report from the
front: the Nigerian ɓideo film. Ƙuartely
reɓiews of film and ɓideo
21 (Routledge).
Okome and Hynes, J, (1997) cinema and
social change in West Africa. Jos: Nigerian Film Corporation,Jos
Okome Hynes, J, (2000), Eɓolɓing popular media: the the Nigerian ɓideo film. Nigerain ɓideo
films Ohio: Ohio center for international studies Jos: Nigerian Film Institute
Jos.
Sa’id, B. da wasu (editoci). (2006). Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero. Kano: Jami’ar Bayero Kano.
Ugor, P (2007). Censorshipand the
content of Nigerian ɓideo films. More, postcolonial teɗt, Uniɓersity of Albata.
Ukadike, F. (2001)” first cinema and
manifestation of “first” cinema in Anglo phone Africa”.
Waya, Z. I. (2021). “Tsarin Jumla a Kalmomin ‘Yan Fim a
Hausa.” Kundin digiri na uku. Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.
Yahaya (1978) “Nazarin kan yanayin
wasan kwaikwayon Hausa, A cikin processing of the first international
conference on Hausa languge, literature and culture Kano: jami’ar bayero.
Yahaya, I.Y. (1988) Hausa a Rubuce:
Tarihin Rubuce-Rubuce cikin Hausa, Zaria: N.N.P.C Zaria.
‘Yar’aduwa, T.M (2007). Wasan
kwaikwayon Hausa Na’oinsa da sigoginsa. Kano: Benchmark published limited.
(Published by usman. Alamin publishing company Kano).
Zango, H. S. (2021). “Zamantakewarmu a
Yau: Nazari daga Fim ɗin Babban Gida.” Kundin digiri na ɗaya. Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.
[1] A
duba Tarken wasan kwaikwayo na 1902.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.