TAMBAYA (72)❓
Hadisi ya tabbata cewar duk sanda musulmi ya karanta Qulhuwallahu ahad sau 10 a jere za a gina masa gidan bene a Aljannah, idan kuma na dace da daren Laylatul Qadari, kenan Allah SWT zai ninninka min ginin gidaje a cikin Aljannah sannan kuma shin zan iya karanta sama da sau 10 don samun gidajen da yawa
AMSA❗
Alhamdulillah
Shahararren
Tabi'in nan Sa'id ibnul Musayyab (Rahimahullah) ya karbo hadisi mursal cewar
Annabi SAW ya ce: "Duk wanda ya karanta Qulhuwallahu ahad sau 10 a jere,
Allah SWT zai gina masa katafaren gidan bene a cikin Aljannah. Idan ka karanta
20, gidaje 2, ka karanta 30 gidaje 3
Sayyadina
Umar RA ya ce: "Na rantse da Allah ! In dai hakane to zamu samu gidajen
bene da yawa tunda zamu yawaita karantawa
Sai Annabi
SAW ya ce: "Fallahu akhsar" ma'ana: "Allah shi ne mai
yawaitawa"
Abin nufi shi
ne Allah SWT ba zai gaji da gina muku gidajen ba matuqar zaku yawaita karantawa
(Sunan
Darimi hadisi mai lambata 3429)
Hafizh Ibn
Khathir (Rahimahullah) ya ce: wannan hadisi ne mursalin jayyid (mai kyau)
(Duba
Suratul Ikhas a cikin Tafsir na Ibn Khathir)
(Muhammad
Abusoomar ya taba amsa makamanciyar wannan tambayar)
Haka kuma an
karbo hadisi daga Abu Hurairah RA ya ce: Annabi SAW yaji wani mutum yana
karanta Qulhuwallahu ahad sai ya ce: "gaskiyar sa ce"
Sahabbai
suka ce: Ya ma'aikin Allah, mene ne gaskiyar ta sa ?
Sai yace
(SAW): "Aljannah ce gaskiyar ta sa"
(Musnad Imam
Ahmad 7669)
Annabi SAW
ya ce: "Duk wanda ya karanta Qulhuwallahu ahad sau 10 a jere, Allah SWT
zai gina masa katafaren gidan bene a cikin Aljannah"
(Sahih
al-Jami' al-Saghir, 6472 na Muhammad Nasiriddin albany)
A shawarce,
duk wanda ya karanta wannan hadisi to ya dinga aiki dashi musamman ma a cikin
goman karshen nan don samun yawan dubunnan gidajen saboda daren Laylatul Qadari
- idan kai malami ne to sai ka tara dalibanka ka ce su dinga karantawa sau 10 a
jere, idan mahaifiyace to sai itama ta tara yayanta waje guda su karanta a tare
kuma a jere, hakama mahaifi. Gidan haya kuke zama a matsayin mata da miji to ku
lizamci wannan bonanza don samun babban rabo, kada ayi biyu babu
Wannan
bonanza za ta fara ne daga lokacin da rana ta fadi har zuwa ketowar alfijir din
daren LAYLATUL QADARI
Kuma duk
wanda ya koyawa wani to yana da ladan wani gidan daban ba tareda an tauyewa
wanda aka koyawa haqqinsa ba kamar yanda ya tabbata a cikin sahihin hadisi.
Allahu Akbar ! Wallahi babu wani Attajiri a duniyarnan da ya isa ya baka wani
abu kwatankwacin wannan
Aljannnah
gaskiya ce. Tananan yanzu haka, an tanade ta ga masu rabo. Mu'ujizozin Qur'ani
kadai sun isa sun tabbatar mana samuwar Aljannah
A shekarun
baya akwai wani lokacin da muna muna zaune tareda yan uwa a makarantar Nurul
Islam litahfizul Qur'an dake anguwanmu, ina cikin karatun Qur'ani ina karanta
daidai ayata 26 cikin Suratu Yunus inda Allah SWT yake cewa;
( لِّلَّذِينَ
أَحْسَنُوا الْحُسْنَىٰ وَزِيَادَةٌ ۖ وَلَا يَرْهَقُ وُجُوهَهُمْ قَتَرٌ وَلَا
ذِلَّةٌ ۚ أُولَٰئِكَ أَصْحَابُ الْجَنَّةِ ۖ هُمْ فِيهَا خَالِدُونَ )
يونس (26) Yunus
Waɗanda suka kyautata
yi, sunã da abu mai kyãwo kuma da ƙari, wata ƙũra bã ta rufe fuskõkinsu, kuma haka wani ƙasƙanci. waɗancan ne abokan
Aljanna, sunã madawwama a cikinta.
Anan take
sai qurar iska ta taso ta lullube fuskokinmu gaba daya, kasa ta shigarwa
wasunmu ido, masu furzar da kasar nayi, tuf ! tuf ! mutane na ta kakkabe
fuskokinsu
Nace Allahu
Akbar ! Sadaqallahul Azim
Anan naga
mu'ujizar Qur'ani qarara, na nunawa yan uwa da muke tare daidai wannan ayar,
mukaita fata da roqon Allah Azzawajallah ya sakamu cikin Aljannah gidan dawwama
inda qura bata rufe fuskoki wadda fadin Aljannar musulmi daya tak yakai girman
sammai bakwai da kassai bakwai kamar yanda Allah SWT ya fada;
( وَسَارِعُوا إِلَىٰ
مَغْفِرَةٍ مِّن رَّبِّكُمْ وَجَنَّةٍ عَرْضُهَا السَّمَاوَاتُ وَالْأَرْضُ
أُعِدَّتْ لِلْمُتَّقِينَ )
آل عمران (133)
Aal-Imran
Kuma ku yi
gaugawa zuwa ga nẽman gãfara daga Ubangijinku da wata
Aljanna wadda fãɗinta (dai dai da) sammai da ƙasa ne, an
yi tattalinta dõmin mãsu taƙawa.
Allahu Akbar
! A dan karamin sanin da Allah SWT ya ba ni na bangaren ilimin kimiyyar sararin
samaniya (Astronomy) wannan ayar ita ce tafi kowacce dauremin kai la'akari da
ana auna girman sama ne da gudun haske wanda a kowanne second daya haske yana
gudun kilometers 300,000 ne kuma akwai inda kafin haske yaje sai ya share sama
da shekaru trillions, quadrillions, octillions ko zillions ko ma sama da haka
kuma duk magana ake ta lebatun sama ta farko ballantana ta biyu har zuwa ta
bakwai. To in dai har fadin gidan mutum daya a Aljannah zaiyi daidai da sammai
bakwai da kassai bakwai to ina kuma ga tsayin gidan, tunda a al'adance tsayi
yafi fadi
Wallahu
ta'ala a'alam
Ya Allah ka
sakamu a cikin Aljannatil Firdous don rahamarka ba don halayenmu ba
Subhanakallahumma
wabi hamdika ash-hadu anla'ilaha illa anta, astaghfiruka wa'atubi ilayk
Amsawa;
Usman
Danliti Mato (Usmannoor_As-salafy)
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.