Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Shan Rubutun Mallakar Miji

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum warahmatullah. malam ina da tambaya, Muna dafa kaza da Tantabara da magani da rubutu muci saboda gyaran jikinmu, ita Tantabara muna rubuta yasin kafa 3 kasancewarta zuciyar Alqur'ani ne, mu haɗa da magani don samun soyayyar miji da kulawa ita kuma kaza Arrahman muke rubutawa kasancewarta Amaryar Alqur'ani ne, idan mun cinye sai mu binne kashin, bama sashi ashara to ya halatta ko ya saɓawa sunnah? Jazakumullahu bikhair.

Karin bayani akan hakan Malam shine ba waɗannan surorin ne kaɗai ake rubutuwa ba, akan rubuta waɗansu surorin daban sannan a buɗe minjaye a rubuta sunan mijin a haɗa da wani abun a sha. Allah ya saka da alkhairi.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Gaskiya ire-iren waɗannan abubuwan ba su halatta ba. Dalili kuwa shine :

- Shi Alqur'ani an saukar dashi ne domin mu yi riko dashi mu samu shiriya da kuma warakar chututtukanmu. Amma ba a saukar dashi don wasu Manufofi irin waɗannan naku ɗin ba.

- Koda Maluman da suke ganin halaccin shan rubutu, Wannan ya keɓanci marasa lafiya ne kaɗai.

- Bai halatta arika chakuda Alqur'ani da wasu abubuwan Kulumboto ba.

- Hakanan duk wani abu Kulumboto ko Surkulle da za a yi shi domin juyar da soyayya zuwa Qiyayya, ko Qiyayya zuwa Soyayya to wannan Sihiri sunanshi. Kuma haramun ne.

Masu yin irin waɗannan abubuwan ba su da wata Hujjar yin haka daga Alqur'ani ko Sunnah ko ayyukan magabata na kwarai.

Gyaran jiki wannan ba laifi bane. Amma duk abin da mutum zai yi don juyar da zuciyar wani, in dai ba addu'a bace to haramun ne.

Ya kamata Mata masu yin irin wannan suji tsoron Allah. Domin daga haka ne ake zarcewa zuwa ga bin bokaye da 'yan bori. (Allah shi kiyayemu ameeen).

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments