MUQABALAR ALKALI ABUBAKAR AL-BAQILLANIY A KAN ANNABI ISA (AS) A FADAR PAPAROMA
Paparoma ya ji Fada ya nuna akwai matsala a hanyar da aka ruwaito Mu'ujizar tsagewar wata ga Annabi Muhammad (saw), har ya ji dadi, ya samu kofar sukar Mu'ujizar ta Annabi (saw), shi ya sa ya tambayi Fadan, ta yaya za a soki maruwaita Mu'ujizar ta tsagewar wata?
Sai Fada ya
ce: Irin wadannan Mu'ujizozi in da a ce sun inganta, to dole a ce mutane masu
yawa ne suka ruwaito daga wasu mutanen masu yawa, haka har ya iso gare mu. Da a
ce an samu haka da dole mu san hakan ya faru. Amma tun da hakan bai faru ba, to
wannan yana nuna cewa; kawai karya ce aka kirkira.
Sai Paparoma
ya juya ya fiskanci Alkali Abubakar Al-Baqillaniy, ya ce: To kawo amsa.
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: To ai abin da kuka fada a kan tsagewar watan
irinsa zan fada a kan "Ma'ida" (teburin cin abinci) da aka saukar wa
Annabi Isa (as) daga sama. Sai a ce muku: Da a ce da gaske an saukar wa Annabi
Isa (as) "Ma'ida" (teburin cin abinci) daga sama to dole a ce mutane
masu yawa ne suka ruwaito daga wasu mutanen su ma masu yawa. Ta yadda ba zai
yiwu a samu wani Bayahude ko Kirista ko Bathanawe face ya tabbatar lallai hakan
ya faru. Amma tun da ba su tabbatar da hakan ba, hakan ya nuna labarin karya
ne.
Nan da nan
Paparoma da Fada da sauran faɗa wa a fadar suka rasa ta cewa.
Ai daga nan
sai taro ya watse.
Sai kuma aka
sake wata haduwar a zama na biyu. Sai Paparoma ya tambayi Alkali Abubakar
Al-Baqillaniy ya ce: Mecece Aqidarku game da Al-Masihu Dan Maryam (as)?
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: Shi ruhin Allah ne, kuma kalmarsa ce, bawansa,
Annabinsa kuma Manzonsa. Kamar Annabi Adam (as) yake, daga kasa Allah ya
halicce shi sai ya ce masa kasance, sai ya kasance. Sai ya karanto Ayar Suratu
Ali-Imran [Aya ta 59].
Sai Paparoma
ya ce: Ya kai Musulmi, Isa Al-Masihun ne kake ce masa bawa?!
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: Eh, haka muke fada, haka yake a Addininmu.
Paparoma ya
ce: Ba ku cewa; shi Dan Allah ne?
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: Allah ya tsare mu. {Allah bai riki wani d'a ba,
kuma babu wani abin bauta a tare da shi...} [Al-Muminun: 91]. Lallai kuna fadin
magana mai girman muni.
Idan kun ce:
Isa Al-Masihu (as) dan Allah ne, to waye Ubansa, waye dan uwansa, waye kakansa,
waye baffansa da kawunsa...?
Ya kirgo
adadi na dangi. Sai Paparoma ya rude.
Sai Paparoma
ya ce: Ya kai Musulmi, shin bawa yana halitta, yana rayarwa, yana kashewa, yana
warkas da makafi da kutare?
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: Bawa ba ya iya yin haka, duka wannan aiyukan
Allah ne.
Sai Paparoma
ya ce: To in ka san duka wadannan aiyukan Allah ne ba na bawa ba, ta yaya
Al-Masihu zai zama bawan Allah, daya daga cikin halittun Allah, alhali ya zo da
wadannan Mu'ujizozi, ya aikata duka wadannan abubuwan mamaki?
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: Allah ya tsare. Isa Al-Masihu (as) bai rayar da
matattu ba, kuma bai warkas da makafi da kutare ba.
Sai Paparoma
ya tunzura ya ce: Ya kai Musulmi, shin inkarin wadannan abubuwa kake yi, alhali
sun shahara kowa ya san hakan?!
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: Babu wani cikin ma'abota ilimi da sani da fahimta
da ya taba cewa; Annabawa su suke halittar Mu'ujizozi da kansu, kawai Allah ne
yake halittarsu, kuma yake aikata su, yake gudanar da su a hanayen Annabawan
don ya gaskata su a kan abin da suke kira gare shi. Mu'ujizozin kamar shaida ce
gare su.
Sai Paparoma
ya ce: To ai kuma an samu mutane da yawa sun tabbatar da cewa; duka wadannan
suna cikin littafinku.
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: Ya kai Paparoma, a cikin littafin namu cewa aka
yi duka abin da Annabi Isa (as) ya zo da shi na Mu'ujiza sun faru ne da iznin
Allah. Sai ya karanto masa Ayoyin daga Al-kur'ani, Ayar Suratul Ma'ida [110],
da Ayar Suratu Ali-Imrana [49].
Sai ya ce:
Duka Annabi Isa Al-Masihu ya aikata su ne da iznin Allah shi kadai ba shi da
abokin tarayya, ba -wai- Isa (as) din ne ya yi su da kansa kai tsaye ba.
Idan za a ce
Al-Masihu Isa (as) da kansa ya rayar da matattu, ya warkas da makafi da kutare,
to kenan sai a ce: Annabi Musa (as) ma da kansa ya tsaga kogi gida biyu, ya
mayar da hanunsa ya yi fari idan ya fitar daga hamatansa, kuma yake juya
sandarsa ta zama macijiya. Saboda haka Mu'ujizozin Annabawa ba aiyukansu ba ne
kai tsaye, Allah ne yake yinsu sai ya gudanar da su a hanunsu.
Saboda haka
idan ba zai yiwu a ce: Annabi Musa (as) shi yake yin Mu'ujizozinsa da kansa kai
tsaye ba, to haka na Annabi Isa (as) ma, ba zai yiwu a ce shi yake yi kai tsaye
ba.
Sai Paparoma
ya ce: To ai dukkan sauran Annabawa tun daga kan Annabi Adam (as) har na
bayansa suna kaskantar da kai ga Al-Masihu suna neman biyan bukata a wajensa.
Sai Alkali
Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: To su Yahudawa kashi ne a bakinsu da ba za su iya
cewa; Al-Masihu (as) yana kaskantar da kai ga Musa (as) yana neman biyan bukata
a wajensa ba?
Ai kowane
mabiyin wani Annabi zai iya cewa; Al-Masihu (as) yana kaskantar da kai ga
Annabinsa yana neman biyan bukata a wajensa. Don haka ba banbanci a wannan
ikirarin.
Can sai wani
Pastor ya daga hanu, sai ya jefo tambaya ga Alkali Abubakar Al-Baqillaniy ya
ce: Me za ka ce a kan abin kunyar da matar Annabinku ta yi, har ake tuhumarta
da aikata alfasha?
Za mu cigaba
insha Allahu.
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.