Citation: Lawal, G. (2024). Ɗarsashin Zuci a Cikin Wasu Waƙoƙin Aminu Ladan Abubakar (ALA). Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 415-422. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.052.
ƊARSASHIN
ZUCI A CIKIN WASU WAƘOƘIN AMINU LADAN ABUBAKAR (ALA)
Garba Lawal
Tsangayar Ilimi,
Jami’ar, Jihar Kaduna
Tsakure:
Wannan takarda ta ƙunshi
tsokaci ne, ko nazari kan yadda Aminu Ladan Abubakar ALA ya sarrafa wasu
zantuttuka da kalmomi masu alaƙa da ɗarsashin
zuci cikin wasu waƙoƙinsa. Mawaƙin ya sarrafa zantuttuka da dama, domin faɗakarwa da ilmantarwa ko
wa’azantarwa a kan wasu abubuwa da suka shafi rayuwar al’umma ta yau da kullum.
Batutuwa masu alaƙa da ɗarsashin
zuciya, batutuwa ne da suka faru ba wai shaci faɗi
ba, waɗanda suke sosa
zuciyar mawaƙin
a duk lokacin da suka faɗo
masa rai, ko suka motsa masa zuciya. Har wa yau kuma batutuwa ne da suke riƙe a
zuciyar mawaƙin
yake ganin ba zai iya mantawa da su ba a rayuwa. A taƙaice dai manufar wannan
nazari shi ne fito da tasiri da muhimmancin ire-iren waɗannan zantuttuka da kalmomi, waɗanda mawaƙin ya
sarrafa a cikin waƙoƙinsa. An yi amfani da ɗiyoyin
waƙoƙin
mawaƙin
a inda aka tattara bayani da suka shafi ɗarsuwan
zuci, wanda a ƙarshen binciken an gano cewa sarrafa ire-iren waɗannan zantattuka masu alaƙa da ɗarsashin zuci a waƙa,
suna da tasiri da muhimmanci domin kusan duk abubuwan da mawaƙin
yake ambatawa a waƙar, tabbatattu ne wato sun faru a zahirance, ba wani shaci faɗi ba ne.
Fitilun Kalmomi: Ɗarsashin
Zuci, Waƙoƙi,
Aminu Ladan Abubakar
Gabatarwa
Mawaƙan Hausa, ya’Allah na baka ko rubutacciya ko na zamani kan yi amfani da
wasu hanyoyi mabambanta ko wani irin salo saboda samun damar isar da saƙonnin dake ƙunshe a waƙoƙinsu, domin bayar da tasu gudummuwar wajen gina rayuwar al’umma. Aminu Ladan Abubakar (ALA) na ɗaya daga cikin shahararrun mawaƙan Hausa na zamani wanda ya rera
waƙoƙi da dama domin faɗakarwa da ilmantarwa ko
wa’azantarwa da kuma waɗanda suka shafi shugabanci ko
siyasa da dai sauransu. Haka kuma mawaƙin
ya yi amfani da basira da hikima wajen sarrafa wasu zantuttuka da kalmomi masu
jiɓi da sosuwar zuci a wasu waƙoƙinsa, a inda yake bayyana abubuwa da ke ƙunshe a zuciyarsa kuma suke
faranta masa rai ko akasin haka a duk lokacin da tunaninsu ya faɗo masa a zuciya. Akwai aikace-aikace da dama da suka gabata
game da waƙoƙin Aminu Ladan Abubakar ALA, waɗanda suka tattauna kan batutuwa daban- daban. Daga cikinsu
akwai Isa, (2009) da ta gudanar da nazari kan farfaganda a waƙoƙin ALA a inda ta kawo misalai a waƙar Bubbukuwa da waƙar bara a Kufai da sauransu. Har
wa yau kuma Yakasai da Abu-Ubaida (2021) sun gabatar da littafi dake ƙunshe da tarihi da kuma
aikace-aikacen fasaha a waƙoƙin ALA da dai sauransu.
Amma duk daga cikin waɗannan aikace-aikace da suka gabata babu wanda ya yi tsokaci
kan ɗarsashin zuciya a waƙoƙin ALA. Saboda haka, manufar wannan nazari shi ne, tsokci
kan wasu waƙoƙin ALA masu alaƙa da ɗarsashin zuciya, domin fito da tasiri da kuma muhimmancin waɗannan zantuttuka da kalmomin da mawaƙin ya sarrafa.
Taƙaitaccen Tarihin Aminu Ladan Abubakar (ALA)
Aminu Ladan abubakar (ALA) yana ɗaya daga cikin mawaƙan
Hausa na zamani wanda ya yi fice a fagen shriya waƙoƙin Hausa domin ilmantarwa, da faɗakarwa, ko wa’azantarwa, da kuma waɗanda suka shafi harkokin siyasa da soyayya da sarauta da dai
sauransu.
Imran (2008) da Umar (2011) da
Hamza (2011) da Isa (2013) da Muhammad (2014) da Yakasai da Sani (2021) sun
bayyana cewa an haifi Aminu Ladan Abubakar (ALA) a ranar talata 2 ga watan 10
shekara ta 1973 cikin shekarar hijira ta 1394 a unguwar Yakasai ƙaramar hukumar Birni da Kewaye,
jihar Kano. Sai dai kuma an yaye shi ne a wata unguwa ta daban, wato unguwar ƙofar Wambai a hannun kakanninsa.
Daga baya sai iyayensa suka yi ƙaura
zuwa ƙaramar hukumar da ake kira
Nasarawa inda suka zauna a unguwa mai suna Unguwar Tudun Murtala.
Karatunsa
Aminu Ladan Abubakar (ALA) ya
fara ne da koyan karatun addini a ƙarƙashin wani malami mai suna malam
Muhammad Sani wanda ake yi wa laƙabi
da malam ɗan- Sakkwato wanda a wurinsa ne
ALA ya haddace izufi biyar daga cikin Alƙur’ani mai girma. Baya ga haka kuma ALA ya yi karatu a wata
makarantar Islamiyya mai suna Zaharadden Islamiyya Tudun Murtala ƙarƙashin kulawar malam Usman Tudun Wada, inda ya fara tun daga
rabin aji har ya zuwa ya kai ga aji shida, wanda daga baya kuma ya zama ɗaya daga cikin
malaman makarantar Islamiyyar.
Aminu Ladan Abubakar (ALA) ya
fara karatun boko ne, a wata makarantar firamare mai suna Tudun Murtala Primary
School. Ya yi wannan karatu ne a tsakanin shekarar 1980 zuwa 1986. Daga nan
kuma sai ya halarci makarantar sakandire ta Dakata Kawaji wato (Government
Senior Secondary School Dakata Kawaji) daga shekara ta 1986 zuwa 1992.
Yakasai (2012) ya ƙara da cewa bayan kammala
karatun sakandaire. ALA ya dakatar da karatu na tsawon shekaru goma sha biyu
(12). Daga baya ya koma makaranta a shekara ta 2003, inda ya shiga makarantar
fasaha ta Kano wato (School of Technology, Kano) ya yi karatu a fannin zane-zane
wato (Department of Art and Industrial Design). A wannan makaranta ce ya samu
shedar Difiloma a shekarar 2007.
Sana’arsa
Aminu Ladan Abubakar (ALA) ya yi
sana’o’i da dama domin magance matsalolin rayuwa waɗanda suka haɗa da zane-zanen taswira da kuma
sana’ar aski ta zamani (Babin Saloon) gugan kayan sawa musamman na kwat-kwat a
‘yan gwanjo wanda ake ba shi yana gogewa idan an buɗe dilar gwanjo.
Rubuce-rubucensa
Aminu Ladan Abubakar ALA ya
wallafa littattafai da dama kafin ya fara sana’ar waƙa daga cikinsu akwai: jirgi ɗaya 1,2,3 da cin zarafi, 1,2 da baƙar aniya 1,2, da cin fuska 1
da rinjaye 1 da Tarzoma 1 da ƙawa zuci 1 da Suwaiba 1 da Ceto
ko Cuta? 1
Ƙungiyoyi
Aminu Ladan Abubakar (ALA) ya yi
rijista da ƙungiyoyi
da dama waɗanda suka haɗa da Association of Nigerian Authors (AMA) da Hausa Authors
Forum (HAF) da Ranar Mawaƙan
Hausa Foundation (RMHF) da Briget Writers Association (BWA) da Areas Films
Makers (AFM).
Iyalansa
Aminu Ladan Abubakar (ALA) yana
da matan aure guda huɗu waɗanda suka haɗa da Khadija Saleh wacce ita ce
matarsa ta farko wacce ya aure ta a ranar ta 4 – 10 – 1996. Sai kuma Alawiyya
Wada Isa ita ce matarsa ta biyu wacce ya aure ta a shekara ta 26 – 8 – 2006.
Sai kuma Adama Sani wacce take matarsa ta uku da ya aura a ranar ta 20-12-2009,
sai ta ƙarshe
wato Alawiyya Ahmad Na’Abba wacce aurenta a ranar ta
15-1-2011. Aminu Ladan abubakar (ALA) yana da ‘ya’ya goma sha huɗu (14) maza huɗu mata goma:
*Maza
Imamuzzabbi
Baƙir
Ahmad
Muhsin
*Mata
Bilkisu
Husna
Humaira
Amina
Nafisa
Husna
Fatima
Khadija
Hafsat
Hanan
Sani, (2021).
2.0 Ɗarsashin Zuci
Masana da manazarta da dama sun
tofa albarkacin bakinsu game da ma’anar kalmar ɗarsashi.
Daga cikinsu akwai Bargery (1934:234) wanda ya nuna cewa ɗarsashi kalma ce ta Hausa wadda aka samu daga kalmar “ɗarsu”. A luggance wannan kalma tana nufin fiɗar wani abu ɗigo-ɗigo, wanda a cikin zance a iya cewa “wannan abin ya ɗarsu a zuciya” (this occured in my mind).
Shi kuwa Izard (1977) ya bayyana
ɗarsashi da cewa, “ya kasance ɗabi’a ko halayyar mutum na yawaita zurfafa tunanin wani abu
na ƙauna ko tsoro ko ƙiyayya” da ka iya haifar da ɗarsuwa a zuciya”.
A cewar Daniel (1995) kuwa, ya
nuna cewa ɗarsashin zuci na nufin tsananta
ko yawaita tunanin wani abu da ake riƙe
da shi a zuciya, wato kamar soyayya ko tsoro”,
ya ƙara da da cewa “Akwai wasu hanyoyi manya-manya kuma mabambanta da ake
fahimtar ɗarsashin zuciya ga ɗan’Adam da kuma dabbobi. Daga cikinsu akwai tsoro da ɓacin rai da kishi ko jin daɗi
da sauransu”.
Gusau (2008) a tasa fahimtar ya
bayyana ɗarsashin zuci da cewa wani abu
ne kan ɗarsu a zuciyar mutum na jin daɗi ko ɓacin rai ko kuma wani abu da ka
iya rinjayar zuciyar mutum domin son wani abu ko kuma ƙiyayya ga wani abu”.
Satatima (2009:48) ya bayyana
sosuwar zuci da wani abu ne da yake cikin zurfin tunanin ɗan Adam. Wanda ƙwaƙwalwa ke sarrafawa sai ya motsa
zuciyar mutum na son wani abu, ko ƙin
wani abu.
Dangane da waɗannan ra’ayoyin masana da manazarta suka bayar, a iya cewa, ɗarsashin zuci kan samu ne sanadiyyar yawaita ko tsananta tunanin
wasu abubuwa da suka faru baya, waɗanda ake riƙe da su a cikin zuciya. Haka
kuma yawaita tunawa da ire-iren waɗannan abubuwa kan samar da jin
daɗi ko farin ciki da murna, ko
kuma akasin haka, wato ɓacin rai ko baƙin ciki da damuwa. A taƙaice
dai sosuwar zuci wani yanayi ne da ya shafi rayuwar ɗan’adam a sakamakon yawaita tunani kan soyayya ko ƙiyayya ko fushi ko raha da dai
sauransu. Wato dai duk waɗannan kan samu ne bayan zuciya
ta sosu.
Ra’in Bincike
Dangane da daddale bayani game
da wannan bincike da aka gudanar. An ɗora aikin ne bisa ra’in ilimin
mutuntaka (psychoanalysis theory) wanda bisa ra’in ne aka nazarci waƙoƙin da Aminu Ladan Abubakar (ALA) ya sarrafa zantuttuka masu
jiɓi da sosuwar zuci.
Henderson da Thompson (2011:28)
sun bayyana cewa Paul Dubious ne ya ƙirƙiri ra’in ilimin mutuntaka kasancewarsa wanda ya shahara a fagen
iya mu’amala tsakaninsa da masu fama da
cutar taɓin hankali da ta shafi ƙwaƙwalwa”. Sigmund Freud ya ɗabbaƙa
ra’in wanda shi masani ne a ɓangaren abubuwan da suka shafi ƙwaƙwalwa da kuma tunani.sigmund Freud ya gudanar da rayuwarsa a
farko-farkon shekaru tamanin da suka gabata a ƙasar ɓiena, wato dai an haife shi a
shekara ta 1956, a garin Freberg na ƙasar
Morabra, kuma ya mutu a ƙasar
London cikin shekara ta 1939.
A shekara ta 1909, Freud ya samu
goron gayyata daga Jami’ar Clerk Jane Worchester ta hannun malaminsa mai suna
Starnly Hall domin ya gabatar da lacca game da ilimin mutuntakar ɗan’Adam. A nan ne Freud ya bayyana cewa akwai ɓangarori guda huɗu da suka danganci mutuntakar ɗan’Adam, waɗanda suka haɗa da:
Id (Hayyaci/ɗimuwa)
Yanayi ne da mutum kan kasance
kodayaushe a ɗimauce ko kuma ba a cikin
hayyaci ba. Wato dai yanayi ne da ake alaƙanta
taɓuwar hankali ko wata matsala da
ta shafi ƙwaƙwalwa.
Ego (Ra’ayi)
wani yanayi ne da a kodayaushe
mutum kan kasance mai ra’ayi nasa na kansa.
Super Ego (ɗabi’a)
Yanayi ne da hankalin da mutum
ke da alaƙa da ɗabi’unsa kyawawa ko munana. Wato dai hankali da ɗabi’a da tunani suna tafiya ne a tare da juna.
Free – Association (‘Yancin
Zuciya)
Wannan wani ɓangare ne, da mutum ke bayyana zancen zuci, wato mutum ya
bayyana abin da ke cikin zuciyarsa ko suke sosa masa zuciya domin isar da wani
saƙo da ka iya zama izna ko nasiha ga jama’a, ko kuma domin mayar da martani a rubuce ko a magance.
Arlow (1984:18) ya ƙara da cewa ‘yancin zuci na nufin barin mutum ya bayyana abin da ke cikin
zuciyarsa, musamman ga wanda zuciyarsa ta sosu sakamakon aukuwar wasu abubuwa
na farin ciki ko na baƙin
ciki.
A taƙaice dai ra’in ilimin mutuntaka na da alaƙa ta kusa da tunani da hankali saboda duk abin da mutum zai
aiwatar sai ya yi tunani a kansa.
Ɗarsashin Zuci A Wasu Waƙoƙin ALA
Tsananta ko yawaita tunanin wasu
abubuwa da suka faru a baya ke haifar da soswar zuci ga ɗan’Adam, wacce kuma take samar da farin ciki da murna ko jin
daɗi da nishaɗi musamman idan abin da zuciyar ta sosu a kansa ya shafi
soyayya. Haka kuma sosuwar zuci kan
samar da baƙin ciki
ko ɓacin rai da nuna takaici ga abin
da ya shafi ƙiyyya.
Aminu Ladan Abubakar (ALA) ya sarrafa wasu zantuttuka masu jiɓi da sosuwar zuci a wasu waƙoƙinsa
domin nuna farin ciki da murna ko waɗanda ya nuna ɓacin rai da baƙin
ciki.
Ɗarsashin Zuci na Murna
Kalmar murna a Hausa tana nufin
nuna jin daɗi ko farin cikin samuwar wani
abu, ko aukuwar wani abu na alkhairi da mutum ya amfana da shi. Mawaƙin ya nuna farin cikinsa da
murna da jin daɗi game da wasu kyaututtuka na
lambobin yabo da karramawa daga makarantu da jami’o’i da kwalejojin ilimi,
kamar dai yadda yake ambatawa a waƙar
inda yake cewa:
Jagora: :F.C.E ta
Kanawa,
:Sun ɗabbaƙa
ayyukana,
:Satifiket sun ka
bani,
:Da allo na
gurina,
:Ƙungiyar ulama’u jimla,
:Na ƙasa ƙarƙaf garina,
:Ulama’un F.C.E.,
:Sun bincika
ayyukana,
:Har shaida sunka bani,
:Don tallata
addabina,
:Kumbotso kwalejin
Sa’ade,
:Sun shaidar
ayyukana,
:Ligal Islam
Study,
:Sun ban allo na
kaina,
:Kwalejin
Zazzagawa,
:Sun bani a kan
yabona,
:Science school ta
mata,
:Ta Garko suna yabona.
Amshi: Shahara ce
ussulibin,
:Ilimi yassamu tsantsa,
(ALA: Shahara Sanadin Sanina)
Haƙiƙa wannan
baiti da ya gabata na wannan waƙa,
ƙunshe yake da zantuttuka masu
alaƙa da sosuwar zuci, da ke nuna
murna da farin ciki tare da yabawa ko godiya, game da kyaututtuka na lambobin
girmamwa da karramawa, wanda mawaƙin
ya amfana da su, daga wasu ƙungiyoyi
da jami’o’i
da kwalejojin ilimi da sauransu. Tabbas wnnan babban lamari ne, da mutum ba zai
taɓa mantawa da shi ba a rayuwarsa.
Wato kamar dai yadda Aminu Ladan Abubakar (ALA) yake yawaita tunawa da ire-iren
waɗannan abubuwan alheri da ya samu
a rayuwa wanda yakan ji daɗi da murna da farin ciki a duk
lokacin da zuciyarsa ta sosu sakamakon tunawa da wannan abun alheri da ya samu.
Har wa yau kuma mawaƙin ya ci gaba da bayyana ko nuna
farin ciki da murna da jin daɗi ganin yadda ya zama sanadiyyar kuɓutar da wasu mutane daga gidan kurkuku, waɗanda aka tsare su kuma babu masu belinsu amma shi ya zama
silar kuɓutar da su kamar dai yadda yake
ambatawa a waƙar inda
yake cewa:
Jagora: Sabulun
wanka da omo,
Da ruwan wanke
jikina,
Sun mani karɓar karamci,
Sanadin ƙaunarsu guna,
Wanka sai nai sau
uku,
Duk wayewa ta
rana,
In gajarce makku
komai,
Wan shekara da
rana,
Aka mai she ni a
kotu,
Ta aminta da mai belina,
Aka ɗagga zama na kotu,
Muka je mu tsumayi
rana,
Sai na samu
ubangidana,
Sani Lawan
maigidana,
Na gaya masa can a
jarun,
Akwai sadaka mai
gudana,
Sadaƙatujjariyar nan,
Mai lada mai
gudana,
Wani yawon darre
yayyi,
Ya shekara gun da kwana.
Amshi: Shahara
sanadin bugawa,
Nasara ta samu guna.
Jagora: Wani
rikici na iyali,
Ya shekara da
kwana,
Wani matsala ce ta
aure,
Takkai shi wajen
da kwana,
Wasu ba hali na
biyan,
Tara ya saka su
kwana,
Wani five thousand
kaɗai ce,
Ta zaman shi gurin
ya kwana,
Wani ten thousand
kaɗai ce,
Ta zaman shi gurin
ya kwana,
Wani ko a jaka ɗari ne,
Ya gaza ya biya
ganina,
Sai Sani ya ce “A ƙirgo,
Adadin saba’in a
zana.”
Zai biya masu
dukka tara,
Su baro jarun da
kwana,
Haka ko an kai da
yardar,
Allah mai
taimakona,
Aka sayi
jallabiyoyi,
Aka babba su da rana.
Amshi: Shahara
sanadin bugawa,
Nasara ta samu guna.
(Waƙar Shahara: Rukuni na huɗu, rukunin nasara).
Duk waɗannan baitoci da suka gabata daga wannan waƙa ƙunshe suke da zantuttuka masu alaƙa da sosuwar zuci da ke nuna
murna da farin ciki ko jin daɗin wani babban aikin alheri da
ya taɓa yi a rayuwarsa. Wato yadda ya
zama silar kuɓutar da mutane saba’in daga
gidan kurkuku. Haƙiƙa wannan ba ƙaramin aikin alheri ba ne, kuma
abu ne da ba za a taɓa mantawa da shi ba a rayuwa.
Ɗarsashin Zuci Na Damuwa
Batutuwa ko zantuka masu alaƙa da ɓacin rai ko damuwa ko baƙin ciki kan zo ne a sakamakon faruwar wasu abubuwa marasa daɗin ji, ko gani da suka faru a baya. Idan aka tuna da faruwar
ire-iren waɗannan abubuwa akan samu damuwa
da ɓacin rai ko fushi da sauransu.
Aminu Ladan Abubakar (ALA) ya sarrafa ire-iren waɗannan
zantuttuka, da dama a wannan waƙa
ta shahara domin byyana wasu batutuwa, da suka
faru a baya wato dai wasu batutuwa ne marasa daɗin ji da mawaƙin
yake yawaita tunawa, da su kuma suke sosa masa zuciya lokaci bayan lokaci. Haka
kuma suke sanya masa baƙin
ciki ko ɓacin rai, da nuna damuwa da dai
sauransu. Mawaƙin ya
nuna ɓacin rai da takaici da nuna
damuwa kan yadda wasu ‘yan uwansa mawaƙa
suka ci amanarsa ta hanyar fitar da wata waƙa a kasuwa wacce take ƙunshe
da habaici da zambo ga wasu manyan jami’an
gwamnatin jihar Kano, kamar dai yadda yake ambatawa a waƙar inda yake cewa:
Jagora: Suka je
suka yanki waƙar,
Hasbunallahhu da
rana,
Suka kai gun ‘yan
wayoyi,
Aka watsa ko a
inna,
Suka ɓata shirin da mun kai,
Suka je censor da
sharri,
Wai mun yo soja na
gona,
Wai mun yi
infasineshan,
Mun cuci Halima
Gwamna,
A can ɓarayin Halima,
Ta ci alwashi da ƙuna,
Mun baɗeta ƙasa
a iddo,
Mun yi sulhu irin
na arna,
Mun yi alƙawari da kanmu,
Sidi da mu kai mu ɓanna,
Sai ta harsala tai
nifaƙa,
Ta kirayi Rabo na
Gwamna,
Ɓarayin Sani Lawan ma,
Aka kai masa tsegumina,
Amshi: Shahara ce ɗan mabuɗin,
Ilimi a ƙasan sanina.
(Waƙar Shahara, rukuni na uku)
Waɗannan
ɗiyoyi da suka gabata ƙunshe suke, da zantuttuka masu
alaƙa da sosuwar zuci mai nuna baƙin ciki ko ɓacin rai, da takaicin abin da ya faru ga shi mawaƙin. Wato yadda wasu ‘yan’uwansa mawaƙa suka ha’ince shi ta hanyar fitar da waƙar da suka rera,
domin raddi ga wasu jagororin hukumar tace fina-finan Hausa ta jihar
Kano. Aminu Ladan Abubakar (ALA) ya nuna takaicinsa ƙwarai, ganin yadda suka watsa
masa ƙasa a ido, suka zubar masa da
mutunci a wurin wasu manyan gwamnatin jihar Kano, musamman Sani Lawal ƙofar Mata da kuma Amaryar
Gwamnan Jihar Kano wato Hajiya Halima
Shekarau.
Haƙiƙa, wannan
wani babban lamari ne da yake sosa zuciyar mawaƙin, musamman a duk lokacin da ya tuno da faruwar al’amarin
sai ransa ya ɓaci. Wato dai kusan a iya cewa,
wani abu ne da ba zai taɓa mantawa da shi a rayuwarsa ba.
Ɗarsashin Zuci na Soyayya
Kalmar soyayya na nufin shaƙuwa ko ƙauna da take tsakanin wasu ɓangarori biyu, wato musamman a tsakanin mutum da mutum, ko a
tsakanin mutum da dabba ko tsakanin mutum da dabba ko tsakanin mutum da wani
abu na daban. Aminu Ladan Abubakar ALA ya sarrafa ire-iren waɗannan zantuttuka da kalmomi a waƙoƙinsa domin nuna muhimmancin soyayya ko dalilai na samar da
soyayya kamar dai yadda yake cewa a wƙarsa:
Jagora: Dalilin So
akwai yawan sabubbai,
Gurbin so akwai
yawa ya ɗibbai,
Ku bi ni a sannu
kar ku zo a baibai,
Zan zo da zuwa in fasale su dai
bai.
Amshi: Sannu
sannu-sannu dai ALA,
Sannu-sannu-sannu dai ALA,
Jagora: Abin ɗoki ya zam abin surewa,
Abin nema ya zam
abin gudewa,
Abin mamari ya zo
da gundurawa,
Da son kwaɗayi haka take zamowa.
Jagora: Abin
fahari ya zam abin kawarwa,
Abin ƙauna ya zam abu na yarwa,
Abin lale ya zam
abin kawarwa,
Da son shelawa haka take zamowa.
(Waƙar Fuju’a (Kalmar So) ta ALA).
Duk waɗannan ɗiyoyin waƙa da suka gabata na daga wannan
waƙa ƙunshe suke da bayanai masu nuna matsayin soyayya, a inda ya
nuna cea, soyayya ta gaskiya ita ce soyayya, ba wai so dan kwaɗayin wani abu na daban ba. Haka kuma soyayya ta sha’awa ita
ma takan zama abar ƙyama
domin soyayya ce ba ta haƙiƙa ba. Ita soyayya ta sha’awa ba ta ƙarko
kuma a ƙarshe
takan haifar da takaici da kuma ɓacin rai ga duk wanda ya tsinci
kansa a cikinta. Wato dai kamar yadda ya nuna cewa, “soyayyar kwaɗayi takan zama abar
surewa”.
“Soyayyar kwaɗayi takan zama abar gujewa” “Soyayyar kwaɗayi takan zama abar gundura”.
Duk waɗannan su ne makomar soyayya, da aka kalata saboda kwaɗayi ko sha’awa.
Ɗarsashin Zuci na Alhini
Kalmar alhini na nufin nuna
juyayi ko damuwa ga wani abu mai tayar da hankali ko firgitarwa, kuma nuna
tausayawa ga wani mutum ko wata al’umma game da faruwar wani lamari marar daɗin ji. Wato kamar yadda Aminu Ladan Abubakar ALA ya nuna
alhininsa ga al’ummar Arewacin Nijeriya dangane da kisar da aka yi wa Sardauna
inda yake cewa:
Jagora: Daga kashe
su Sardauna,
An ka yi Decreen ƙarya,
Sun ka yi thirty
four Decree,
Dokoki na hamayya,
An ka rugurguje
aikin,
Amadu babu
alkunya,
Northernisation
Policy,
An ka baje su ba kunya.
‘Y/Amshi: Gamji
Maza abin koyi,
Ahmadu Bello
Sardauna,
In na tuno
wafatinsa,
Sai ya sako ni in kuka.
Jagora: An izini a
ƙasar Hausa,
Hausa ta zam
harshen aiki,
Daga kashe su
Sardauna,
An ka ba je wannan
aiki,
Wani abu na ban
haushi,
Sanda akai kisan
haƙƙi,
Sai Ibo sun ka hau
fati,
Sun kashe Gamji Hamshaƙi.
(ALA: Waƙar Gamji Maza).
Haƙiƙa duk waɗannan baitoci da suka gabata na daga wannan waƙa, ƙunshe suke da batutuwa dake nuna
alhini ga al’ummar Arewacin Nijeriya, na
babban rashin da suka yi na jajirtaccen shugaba, kuma jarimi wato wanda ya kawo
wasu abubuwan ci gaba a yankin Arewa. Amma kuma yau an wayi gari babu shi,
sakamakon kisan da wasu suka yi masa. A
dalilin haka ya zama an rasa wasu daga cikin ire-iren ci gaban da ya kawo a
yankin na Arewacin Nijeriya. Da wannan
Aminu Ladan Abubakar ALA yake nuna alhininsa a wannan waƙa domin tausayawa ga al’ummar Arewacin Nijeriya
5.0 Kammalawa
Haƙiƙa sarrafa
ko amfani da zantuttuka ko kalmomi masu alaƙa da sosuwar zuci na da matuƙar tasiri da muhimmanci ga rayuwar al’umma. Saboda faɗakarwa ce ko ilmantarwa kai
tsaye domin kuwa abubuwa ne da suka faru a zahirance kuma ga shi kansa mawaƙin yake bayyanawa da nufin, su
zama izna ga mutane. Har wa yau kuma batutuwa ne da ake da tabbacin faruwarsu
ba wai shaci faɗi ba. Sa’annan kuma zantuttuka ne masu ratsa zuciyar mai sauraro
sakamakon yadda suke ƙunshe
da abubuwan tausayi ko alhini da ta’ajibi
da dai sauransu. A taƙaice
dai amfani ko sarrafa zantuttuka masu alaƙa
da sosuwar zuci a waƙoƙin Hausa na zamani, wata hanya
ce ta faɗakarwa da ilmantarwa, da
wa’azantarwa, ta hanyar bayyana wasu abubuwa da suka faru ga mawaƙi, ko ga wata al’umma da ya rayu a cikinta. Saboda haka suna da matuƙar muhimmanci da tasiri ga
rayuwar al’umma.
Sakamakon Bincike
Haƙiƙa yawaita
tunanin wasu abubuwa a ƙwaƙwalwa ke haifar da sosuwar zuci
ga ɗan’Adam. Wato mutum ya kasance
mai yawaita tunani game da wasu abubuwa da suka faru kuma ake riƙe da su a zuciya. Ire-iren waɗannan abubuwa sun danganci soyayya kan wani abu, ko ƙiyayya ga wani abu, ko kuma wata
hamayya da ta kasance a tsakanin wasu mutane ko al’umma. Da wannan ake ganin cewa, ɗarsashin zuci wani yanayi ne, da ya shafi rayuwar ɗan’Adam da ta ƙunshi
wasu abubuwa kamar tunani, ko juyayi ko alhini ko kuma ƙiyyya ga wani abu, ko soyayya
kan wani abu ko hamayya da dai sauransu. Duk waɗannan
wasu abubuwa ne da idan suka faru ba a taɓa mantawa da su a rayuwa. Saboda
abubuwa ne da za a riƙa
yawaita tunani game da faruwarsu musamman ga mutumin da ya tsinci kansa ga ɗaya daga cikinsu.
Aminu Ladan Abubakar (ALA) ya
sarrafa zantuttuka, masu jiɓi da sosuwar zuci a wasu waƙoƙinsa, domin faɗakarwa da ilmantarwa. Mawaƙin ya kawo batutuwa, da dama da
suka faru, masu daɗi da marasa daɗi waɗanda suka faru a kansa, musamman
ga abin da ya shafi sana’arsa ta waƙa.
Har wa yau kuma mawaƙin ya
sarrafa zantuttuka masu alaƙa
da sosuwar zuci a waƙoƙinsa, ta hanyar bayyana
gwagwarmaya da kuma ƙalubale
da ya fuskanta a rayuwa, duk a sanadiyyar rera waƙoƙin Hausa
na zamani, wanda har sai da waƙa
ta zama sanadiyyar zuwansa gidan kurkuku. Aminu Ladan Abubakar (ALA) ya bayyana
batutuwa da dama waɗanda suka faru a kansa masu kyau
da marasa kyau waɗanda suke faranta masa zuciya ko
ɓacin rai, a duk lokacin da
tunaninsu ya faɗo masa a zuciya.
Ire-iren waɗannan batutuwan sukan ɗarsa masa zuciya lokaci bayan
lokaci, tare da sanya masa farin ciki ko nishaɗi,
ko kuma akasin haka. Da wannan dalili ya sa mawaƙin yin amfani da waɗannan batutuwa domin nufin faɗakarwa da ilmantarwa ga jama’a. Duk batutuwan da mawaƙin ya ambata masu alaƙa da ɗarsuwan zuci, abubuwa ne da suka faru a zahirance ba wai
shaci faɗi yake furta wa ba. Da wannan
ake ganin cewa, ire-iren zantuttuka masu alaƙa da ɗarsuwan zuci waɗanda mawaƙin
ya sarrafa suna da tasiri da muhimmanci ga rayuwar al’umma, musamman idan aka
yi la’akari da ire-iren darussa da zantuttukan suka ƙunsa. Wato tun daga kan
gwagwarmaya da ƙalubale
da ya fuskanta a rayuwa dangane da sana’arsa
ta waƙa. Da kuma ire-iren nasarori da
kyaututtuka da kuma lambobin girmamawa da ya sam daga jami’o’i da kwalejojin
ilimi da ƙungiyoyi
daban-daban. Duk waɗannan suna da tasiri da
muhimmanci ga rayuwar jama’a. Wannan kuwa saboda batutuwa ne da suka ƙunshi haƙuri da jarunta da kuma dagewa
wajen neman na kai da riƙo
da gaskiya da rashin tsoro da haƙuri
da dai sauran su.
Manazarta
Barista, M.L. (2011). Waƙoƙin Aminu Ladan Abubakar ALA. Kano: Iya Ruwa Publishers.
Bashir, R. (2021). Hotoncin Zuci A Waƙoƙin Baka Na Hausa: Tsokaci A Kan
Wasu
Waƙoƙin Maza
Da Na Fada. Digiri Na Uku. Sashen Harsuna da Al’adun
Afirka. Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.
Daniel, G. (1995). Emotion
Intelligence. London: Bantom Books.
Gusau, S.M.
(2008). Waƙoƙin Baka A Ƙasar Hausa: Yanaye-Yanayensu Da
Sigoginsu Kano: Benchmark Publishers
Limited.
Hamza, M.K. (2011). Nazarin
Salon Sarrafa Harshe a waƙoƙin Aminuddeen Ladan Abubakar
(ALA). Kundin Digiri na Farko, Sashen Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu ɗanfodiyo.
Imran, A.L. (2008). Jigo da Salo
a waƙoƙin Aminu Ladan Abubakar (ALA). Kundin Digiri na Farko,
Sashen Harsuna da Al’adun Afirka. Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.
Isa, Z. (2013). Farfaganda a Waƙoƙin Fiyano na Hausa Daga 2003 –
2013. Kundin Digiri Na Biyu, Sashen Harsuna da Al’adun
Afirka. Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.
Izard, C.E. (1977). Human
Emotion. New York: Plenum.
Lawal, G. (2022). Sosuwar Zuci A
Waƙoƙin Hausa Na Zamani: Nazari A Wasu Waƙoƙin Aminu Ladan Abubakar (ALA). Digiri Na Uku. Sashen Harsuna
da Al’adun Afirka. Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.
Satatima, G.I. (2009). Waƙoƙin Ɗarsashin
Zuciya Na Makaɗan Husa. Kundin Digiri na Uku.
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya da Kimiyyar Harshe. Kano: Jami’ar Bayero.
Umar, R.A. (2011). Matsayin Uwa
a Bahaushiyar Al’ada: Nazarin Waƙar
Ummina ta Aminu Ladan Abubakar (ALA). Kundin Digiri na Farko, Sashen Harsunan
Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu ɗanfidiyo.
Yakasai, S.A. da Sani, A.
(2021). Diwanin Waƙoƙin Aminu Ladan Abubakar (ALA)
Amana Printing Press.
Yusuf, B. (2017). Zuciya A Tunanin Bahaushe: Nazari Daga Waƙar Baka. Kundin Digirin Farko,
Sashen Harsuna Da Al’adun Afirka. Zariya: Jami’ar Ahmadu Bello.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.