Citation: Sulaiman, M.S. (2024). Bayyanar Izzar So A Tarbi`in Waƙar, "Zuwana Jami`a."Ta Alƙali Halliru Wurno Sakkwato. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 423-431. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.053.
BAYYANAR IZZAR SO
A TARBI`IN WAƘAR, "ZUWANA JAMI`A."TA ALƘALI
HALLIRU WURNO SAKKWATO
Muhammad Salisu
Sulaiman
Sashen Harsunan
Nijeriya Da Kimiyyar Harshe, Tsangayar Fasaha Jami`ar Jihar Kaduna
Tsakure:
Wannan maƙala ƙunshe take da sharhin wata waƙa
wadda Alƙali
Halliru Wurno ya rubuta mana a lokacin muna ɗalibta
digirin farko a Jami`ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato, a shekarar 1994.
Halliru Wurno ya ziyarce mu ne sakamakon gayyatar da malaminmu Farfesa
Abdullahi Bayero Yahya ya yi masa. A yayin ziyarar ya gabatar mana da wasu daga
cikin waƙoƙinsa.
Bayan ya kammala gabatar da waƙoƙin, mun yi masa tambayoyi game da
rayuwarsa da waƙoƙin da ya gabatar. A lokacin da zai tafi, sai ya karɓi sunayen ɗaliban ajin domin ya rubuta
masu waƙa.
Sai aka yi rashin sa`a sunayen wasu ɗaliban
bai fito a cikin waƙar ba. Wannan ya kawo `yan gunaguni a tsakanin ɗalibai. Sannan a cikin waƙar sai
ɗaliban suka lura cewa
an fifita ambaton sunan wata ɗaliba
Binta. Saboda an ambaci sunayen ɗalibai
kowa sau ɗaya, ita
kuwa an ambace ta har waje takwas. Waɗannan
abubuwa guda biyu, su ne suka haifar da tambayoyi kamar haka: Me ya sa sunayen
wasu ɗaliban bai fito
ba? Sannan mece ce alaƙar Halliru Wurno da Binta? Waɗannan
tambayoyi su ne aka yi sharhi a kansu a cikin wannan maƙala.
Fitilun Kalmomi: Izzar So, Tarbi`i, Waƙa, Alƙali
Halliru Wurno
Gabatarwa
A lokacin muna ɗalibta
a matakin digirin farko a Jami`ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato, malaminmu Farfesa
Abdullahi Bayero Yahya, yana da wani tsari da yake gabatarwa ga ɗalibansa: "Waƙa A
Bakin Mai Ita." Yakan gayyaci marubuta waƙoƙi cikin aji, mawaƙi ya gabatar da waƙarsa, ɗalibai su yi masa
tambayoyi. A irin wannan tsari Malam ya taɓa
gayyato mana Malam Sambo Wali da Malam Garba Gwandu da Alhaji Alƙali
Halliru Wurno.
Maƙasudin wannan tsari shi ne domin ɗalibai su sami ƙaruwar ilimi daga bakin mawaƙa kai tsaye.
Game da gayyatar da ya yi wa Halliru Wurno, ga abin da Farfesa Abdullahi Bayaro
Yahya ya ce:
"Saduwar Halliru Wurno da ɗaliban aji uku na ALH. 312: Rubutattun Waƙoƙin
Hausa, na gayyaci Alhaji Halliru da ya zo cikin wannan aji a ranar 08-01-1994
domin ɗalibaina suna
buƙatar
su yi hira da shi. Ya kuwa karɓi
wannan gayyata. Mun yi hira da shi mai amfani kuma na naɗe hirar a cikin faifan rikoda."
Ina iya tunawa a cikin godiyar da Farfesa Abdullahi Bayaro
Yahya ya yi ga Halliru Wurno, bayan an gama hirar, ya yaba mana sosai, a taƙaice
ga abin da ya ce:
"Bisa al`ada ta zamantakewa, idan ɗalibanka suka yi abin yabo,
kakan jira ne wani ya yaba masu. To amma waɗannan
ɗalibai ba zan jira
yabon wani ba, ni da kaina zan yaba masu. Wato zan yi koyi da sunnar ƙadangare.
A lokacin da ya faɗo
daga sama, ya duba dama da hagu, ya ga ba wanda ya jinjina masa, sai ya jinjina
wa kansa. Alal haƙiƙa na yaye ɗalibai
da dama, amma waɗannan
ɗalibai na musamman
ne, ba zan taɓa
mantawa da su ba."
A lokacin da Halliru Wurno zai tafi, sai ya karɓi sunayen wasu daga cikin ɗaliban. An karɓi sunayen ne a gurguje,
saboda haka sunayen wasu bai fito a cikin waƙar ba.
Asalin waƙar ƙwar biyu ce, sai na yi mata tarbi`i, wato
na ƙara
ɗangwaye biyu a kan
kowane baiti. Saboda akwai ƙorafi na rashin fitowar sunayen wasu ɗaliban ajin, sai aka ƙoƙarta aka kawo su cikin waƙar. Waƙar
Halliru Wurno ta tsaya ne a baiti na 51. Daga nan sai na ɗora har zuwa baiti na 80,
wato kusan dukkan ɗalibai
na B.A.Hausa 1995 sun fito a cikin waƙar. Sannan aka yi godiya ga wasu daga
cikin malaman da suka koyar da mu a shekarar.
Ma`anar Waƙa
“Waƙa tsararriyar maganar hikima ce da ake rerawa ba faɗa kurum ba, wadda ke ƙunshe
da wani saƙo
a cikin zaɓaɓɓun kalmomi waɗanda aka auna domin
furucinsu ya yiwu ba tare da tuntuɓe
ba." (A.B.Yahya:199: 3)
"Rubutacciyar waƙa, aunanniyar maganar hikima ce wadda ake
rerawa a cikin tsarin daidaitattun ɗangwaye
da baitoci da tsayayyun ƙafiyoyi a rubuce ko a haddace ba tare da kiɗa ba." (Sulaiman S.M.
2019)
Zubi Da Tsarin Waƙar
Asalin wannan waƙa ta Halliru Wurno ya rubuta ta ne da
haruffan Ajami. Farfesa Abdullahi Bayero Yahya, ya juya ta zuwa haruffan
Ingilishi, sannan waƙar `yar tagwai ce, tana da ƙanana da babban amsa-amon (na)
Daga baya ɗaya
daga cikin ɗaliban
ajin Sulaiman Salisu Muhammad Mai Bazazzagiya ya yi mata tarbi`i. Wato ya ƙara ɗangwaye bibbiyu a bisa
kowane baitin waƙar. Sannan ya ƙara wasu baitoci a cikin waƙar,
domin sunayen duka ɗaliban
ajin ya fito. Halliru Wurno ya tsaya a baiti na 51, shi kuma Sulaiman ya ƙara
har zuwa baiti na 80.
Amsuwar Waƙar Ga Ɗalibai
Bayan Halliru Wurno ya kammala wallafa waƙar, an
gabatar da ita ga ɗalibai,
maimakon ɗaukacin ɗalibai su nuna gamsuwarsu
da waƙar,
sai wasu ɗalibai suka
fara gunaguni. A lokacin sai tunanin ɗalibai
ya kasu zuwa gida huɗu:
Waɗanda
sunayensu ya fito a cikin waƙar suna murna, saboda tarihi ba zai mance
da su ba. Wannan ya sa sun yaba sun yi godiya matuƙa ga Halliru Wurno.
Waɗanda
sunayensu bai fito ba, duk da cewa suna cikin ajin a lokacin da aka yi hirar,
suna gunaguni mene ne ya haifar da haka? Duk da yake a cikin waƙar
Halliru Wurno ya amsa wannan tambaya kamar haka:
Ina zuba godiyata na yaba ku,
Rashin sunanku shi at tarnaƙina.
Zama sunan waɗansu
da ban sani ba,
A nan su nis sani ga irin sanina.
Wasu daga cikin ɗalibai
mata sun nuna kishi, me ya sa aka ambaci sunan Binta fiye da su, tana ɗaliba suna ɗaliba, kuma haɗuwar farko a cikin aji?
A bisa al`adar zamantakewar ɗalibai
a cikin aji, za ka ga akwai ƙauna, ko so, ko soyayya da ke gudana a
tsakanin ɗalibai.
Akwai masu son Binta a cikin aji, wasu sun nuna jin daɗi wasu kuwa damuwa suka nuna.
2.1 Mece ce Izzar So?
2.1.1 Izza
Asalin kalmar izza Balarabiyar kalma ce. A cikin Alƙur`ani
mai girma Allah SWT ya ce: "Duk wanda ya kasance yana neman wata izza, to
Allah shi ne mai izza gaba ɗaya."
(Sura:
Faɗir, Aya ta 10 )
Bargery (1934) a cikin ƙamus ɗinsa
ya bayyana ma`anar izza da, 'Girman kai.'
Kalmar izza na iya ɗaukar
ma`anar ƙuwwa
ko shauƙi
ko ƙarfi
ko ɗaukaka, musamman
abin da ya shafi mulki.
2.1.2 Ma`anar So
So, shi ne sosuwar ko ƙawazucin zuciya na kusantar, ko mallakar,
ko ganin, ko jin labarin wani abu mai rai ko maras rai, da nufin biyan wata buƙata
domin sanyayar zuciya.
2.2. Yadda Ake Kamuwa Da So
Kamuwa da so wanda ya shafi mu`amala tsakanin mace da
namiji, ba abu ne wanda ake shirya masa ba. Haka kwatsam mutum kan sami kansa
cikin tarkon so, ya cukuikuye shi. Kamar yadda hatsarin mota kan zo ba shiri,
wani ya ji ciwo, wani ya fita lafiya, wani ma har ya mutu, to haka shi ma shiga
tarkon so yake. Babu wani wuri takamaimai inda so ke ɗana tarkonsa. Tarkon so na nan a kakkafe a
ko`ina, ana iya faɗa
masa ba dare ba rana. Mutum na iya aukawa a tarkon so a kasuwa ko a mota ko a
filin wasa ko a wurin biki ko asibiti ko makaranta da sauransu.
2.3. Mabuɗan
Kamuwa Da So
Mabuɗi
shi ne abin da ake amfani da shi wajen buɗe
rufaffiyar jaka ko akwati, ko ƙofa domin a samu a shiga ciki. Kamar
yadda kullalliyar ƙofa take, haka nan zuciyar ɗan
Adam ke a kulle. Akwai mabuɗai
guda uku waɗanda ke buɗe zuciyar ɗan Adam. Da zarar sun buɗe ta, sai so ya sami damar
cusa kansa ciki. Wani kan tsaya a bakin ƙofa, wani kan tsaya a tsakiya, wani kan
kai ƙarshen
zuciyar wanda ya kamu da shi. Waɗannan
mabuɗai na so ga su
kamar haka:
2.3.1 Gani: Yana ɗaya
daga cikin abubuwan da ke haifar da kamuwa da so a tsakanin `yan Adam. Namiji
na iya kamuwa da so, da zarar ya ga wata mace, ba sai ya yi magana da ita ba,
haka nan abin yake ga mace. Wannan ganin na iya kasancewa ganin fuska da fuska,
ko gani a hoto, ko kuma gani ta talbijin. Sannan mutum na iya kamuwa da son
wani ko wata da zarar ya gan shi, ko bai san shi ba.
3.1.2 Magana: Magana kan taka muhimmiyar rawa a wajen buɗe ƙofar so a cikin zukata.
Wani da ya ji maganar mace zai kamu da son ta. Haka ita ma wata macen da ta ji
maganar wani, sai ta kamu da son sa. Wannan maganar tana iya kasancewa ta baka
da baka ce ta gudana a tsakanin mai son da wadda ake son. Ko kuma ta kafafen yaɗa labarai kamar: Rediyo ko
Talbijin ko Jarida. Wani kuma ta jin waƙa ko kuma karatun Al`ƙur`ani
ko wa`azi. So na iya sarƙuwa ta kowanne ɗaya
daga cikin waɗannan
nau`o`in magana.
3.1.3 Labari: Jin labari na ɗaya
daga cikin hanyoyin da kan sa mutum ya kamu da son wani ko wata ko wani abu ba
tare da ya gan shi ba, bai kuma ji maganarsa ko maganarta ba. Sai dai kawai ya
ji labarinsa ko labarinta ne. Tana iya kasancewa wannan labarin an ji shi baki
da baki ne, ko a gidan Radiyo, ko a Talbijin. Ko kuma a rubuce a Mujalla ko a
Jarida. Labarin da aka ji yana iya kasancewa ta wata jarumta ce, a fannin
sana`arsa, ko a makaranta, ko dukiyarsa ko ɗabi`unsa
da sauransu.
3.2 So Ba Shi Da Bare
Ɗabi`ar so, kamar jini ne a jikin ɗan Adam, ba wanda ba shi da shi. Ko kuma kamar
iska ce, ba wani abu mai rai wanda ba ya shaƙar sa. Ba wani abu mai rai, mutum ne ko
dabba ce, tsuntsu ne ko ƙwaro ne, ko shuka da zai ce ba ya shaƙar iska. To haka shi ma
so yake, duk wata halitta mai rai tana da nata hanyoyin aiwatar da so. Mutum ba
ya gushewa da son wani abu, sai ranar da aka ce ya bar duniya.
Sai dai ɗabi`ar
so, kowace ƙwarya
akwai abokiyar burminta. Yara da matasa, da tsofaffi, malamai da ɗalibai, masu arziki da
talakawa duk suna da shi a cikin zukatansu. Haka dabbobi da tsuntsaye da ƙwari
da shukoki, duk akwai irin nasu nau`in son.
3.3. Wace ce Binta?
Asalin Binta Bakatsiniya ce tana cikin ɗalibai waɗanda ba su yi aure ba a
lokacin, wato budurwa ce. kamar yadda Alƙali Hilliru ya kawo bayaninta a cikin waƙar.
6. Garinta na Dikko can Katsinanssu,
Haƙiƙan Binta ta tsere ka juna.
Akwai baitoci guda takwas da aka ambaci Binta, waɗannan baitoci ga su kamar
haka: 6, 8, 9, 17, 19, 23, 27, 47. Haka nan akwai wata Binta Chinoko, wadda aka
ambata sau ɗaya. A
gaskiya an shaidi Binta da kyawawan ɗabi`u.
Hannayenta a buɗe suke
ga duk wani ɗalibi da
ya nemi agajinta, musamman kuɗi
ko abinci idan ALUTA ta ratsa.
A wajen siffar jiki ba a bar ta a baya ba, irin siffar
Katsinawa ke gare ta. Ita ba ƙatuwa ba, ba kuma lange-lange ba. Ita ba
fara ba ce, amma kuma ba baƙa ba. Wato siffar wankan tarwaɗa
ke gare ta. Ga ta kyakkyawa ga fuska da sauran sassan jikinta. Duk wanda ya yi
wata hulɗa da Binta,
tabbas zai ce ta cancanci wancan yabo da Halliru Wurno ya yi mata. Gamayyar
kyawawan ɗabi`u na iya
mu`amala, da kyawun siffar diri, da iya magana, waɗannan su ne tarkon da ke ribatar zukatan masu
mu`amala da Binta har su ƙaunace ta.
3.4. Bayyanar Izzar So
A sakamakon gabatar da waƙar da Halliru Wurno ya yi Izzar So ta
bayyana a waɗannan a tsakanin
waɗannan kason mutane:
Yawaita ambaton sunan Binta a cikin waƙar,
akwai alamun Halliru Wurno ya kamu da son Binta. Ba komi ya haifar da haka ba
illa Izzar so. Ƙila ita ce ta ingiza shi ya yi wannan yabo, ba tare da
la`akari da me zai biyo baya ba.
ii. Halliru Wurno a matsayinsa na babban malami, Alƙali,
mawaƙi,
ba zai rasa wasu daga cikin ɗalibai
mata masu son sa ba. Tunda kowa yana son nagari. To sai ga shi ƙarara
ya karkata yabonsa zuwa ga Binta. Wannan ya haifar da kishin so a tsakanin wasu
ɗaliban masu ƙauna
ko son Halliru Wurno. Misali dubi yadda yake umurtar sauran matan da su kai
caffa zuwa ga Binta.
Garinta na Dikko can Katsinanssu,
Haƙiƙan Binta ta tsere ku juna.
Ku saurara ɗiya
mata ku ji ni,
Ku kai caffa ga Binta tana da rana.
Halinta kama da Binta ta Dikko waccan,
Da nic ce tai kama da wata da rana.
Waɗannan
baitoci sun fifita Binta a kan sauran ɗalibai
mata. Abu ne sananne ga mata cewa ba kasafai mata ke yarda wata ta fi su ba.
Wannan ya haifar da kushewa da tsangwama a tsakanin Binta da sauran ƙawayenta.
Ba komi ya haifar da haka ba, illa izzar so da ke cikin zukatansu.
Waɗanda
ke son Binta izzar so ta bayyana a gare su ta fuska biyu:
Kaso na farko, suna jin daɗi
an kwarzanta masoyiyarsu. Saboda haka zaɓinsu
ga Binta ba su yi zaɓin
tumun dare ba. Saboda haka sonsu zuwa ga Binta ya ƙaru matuƙa,
haka nan ƙaunarsu
ga Halliru Wurno ta ƙaru, saboda ya yabi tasu.
Kaso na biyu, suna ganin wannan yawan yabo, da walakin, goro
a cikin miya. Sawun giwa ne ke son take na raƙumi. Misali a baiti na 11 ga abin da ya
ce:
Karatu tat taho ba son maza ba,
Akwai su garinsu mai wargi ka daina.
Wannan baitin kamar yana yi wa masoyan Binta shaguɓe ne, cewa su daina damun
ta da batun neman soyayya. Ba abin da ya kawo ta Jami`a ke nan ba, karatu ta zo
yi. Idan maza take so, ai akwai su a garinsu. Wannan ya sa izzar so da ke cikin
zuciyarsu ya sa sun ƙara ƙaunatar Binta saboda a bisa alamu ana so a ture su gefe. A
gefe ɗaya kuma, a
dalilin izzar so, suna yi wa Halliru Wurno kallon hadarin kaji, saboda abin da
ya faɗi gare su, kamar
yana kashe masu kasuwa ne.
4.1 Kammalawa
A bisa bayanai da suka gabata, an yi bayani game So da yadda
ake kamuwa da So. Sannan mun ga bayyanar izzar So daga ɓangarori mabambanta. Wadda izzar So ta ja
Halliru Wurno yawaita yabon Binta a cikin waƙarsa, ba tare da la`akari da me haka zai
haifar ba, a tsakanin ɗaliabai.
Izzar So ce ta haifar da kishi a tsakanin ƙawayen Binta, saboda an fifita ta a
kansu. Haka nan izzar So ta sake bayyana a tsakanin masoyan Binta maza, wasu na
yabon Halliru Wurno saboda ya wasa gwanarsu. Wasu kuwa na kushe masa saboda
suna da tunanin cewa, in ka ga kare yana sunsunar takalmi, ƙila ɗauka zai yi.
Daga ƙarshe a cikin wannan maƙala an kawo tarbi`in 'Waƙar
Zuwana Jami`a,' sannan an ga yadda aka ƙara sunayen ɗaliban da Halliru Wurno bai sanya su a cikin
waƙarsa
ba. Aka rufe waƙar da godiya ga wasu malamai da suka koyar da ɗaliban shekarar 1995.
TARBI`IN WAƘAR ZUWANA JAMI`A TA ALƘALI
HALLIRU WURNO
Sulaiman Salisu Muhammad (Mai Bazazzagiya)
08067917740 30-08-2023
Zuwana Jami`a nis san ka Dabo,
Zuwana Jami`a dai mun yi sabo,
Zuwana Jami`a na sami tarbo,
Ga manyan ɗalibai
manyan ɗiyana.
Maza mata ina ƙaunar ku sosai,
Maza mata fa ga tsaraba ta ƙosai,
Maza mata fa na same su sosai,
Akwai ladabi gare su suna da rana.
Da duba na ga fuskokin ƙawaye,
Da ƙauna tas shige ni ina hawaye,
Da duba na ga fuskokin su waye,
Kamar dai safiyar sallah ganina.
Da mata har mazansu nake ta ƙauna,
Da mata har mazansu irin ganina,
Da mata har mazan nan salihina,
Sakin fuska mutumci sun yi suna.
Akwai wata malama ba ta bilayi,
Akwai ladabi na ce ba kauce layi,
Akwai wata malama dubin da na yi,
Akwai natsuwa ga Binta irin ganina.
Garinta na Dikko ga kara gare su,
Garinta na Dikko kunya ce gare su,
Garinta na Dikko can Katsinanssu,
Haƙiƙan Binta ta tsere ku juna.
Akwai kyawo akwai natsuwa gare ta,
Akwai kyawon ɗabi`a
ba mugunta,
Akwai ladabi akwai hange gare ta,
Daɗai
ba ta ya da kai ba ku ɗau
batuna.
Kwaɗai
ke sa ake dai raina mata,
Kwaɗai
sam babu shi a wajenta Binta,
Kwaɗai
dai ba ta yi ta kama kanta,
Faɗin
baba ga Binta abin musu na.
Ɗiyata tabbaci kin zarce mata,
Ɗiyata kin yi tsatsa zuciyata,
Ɗiyata na jiya kumya ke gare ta,
Yawan ladabi ga Binta abin yabo na.
Da ɗai
ba a ce taho domin kira ba,
Da ɗai
ba a ce taho ba ta sunkuya ba,
Da ɗai
ba a ce taho ki jiya ta zo ba,
Ajin nan dole dai taka amsa suna.
Karatu tat taho ba shirbici ba,
Karatu tat taho ba gulmace ba,
Karatu tat taho ba son maza ba,
Akwai su garinsu mai wargi ka daina.
Zama ba don ana ce ɗaliba
ba,
Zama ba don ina guje kuskure ba,
Zama ba don ganin ta cikin aji ba,
Walicci zan kirai mata ni ganina.
Zama Binta a ilmi zaruma ta,
Zama azumi da salllah ta naƙalta,
Zama ita saliha ta mumina ta,
Na Allah ɗai
take shagali mu`ina.
Akwai wata salaha yanzun tana nan,
Akwai wata mai himma tana nan,
Akwai wata Hanne `yar Kawoje na nan,
Akwai lura da himma lalabena.
Haƙiƙa zubinta yai siffar madubi,
Haƙiƙa halinta kullum kama carbi,
Haƙiƙa halinta Hannatu ko ga dubi,
Fulanin Yamma kumya sun yi suna.
Ɗiyar nan yanzu kaya za ni sauke,
Ɗiyar ɗakinta
kullum ga shi wanke,
Ɗiyar Kangiwa na ga Amina yanke,
Ga boko ko gurama ta yi suna.
Halinsu guda da manya masu ilmi,
Halinsu guda da waye mai muƙami?
Halinsu guda da Binta zuwa ga ilmi,
Ta Birnin Dikko ƙusa ba ta kwana.
Da himma tat tafo kwa daina ƙyashi,
Da himma tat tafo hannu da mashi,
Da himma tat tafo digiri ta yo shi,
Garat `yan si, e, wannan ƙanƙane na.
Ba`a kam Binta sam ba ta kula sa,
Ba`a kam Binta ba mata na gasa,
Ba`a kam Binta ba ta kula da wasa,
Sani taz zo biɗa
wasa buzaina.
Ba`a ab ba ta yi ko ɗai
ƙazamat,
Ba`a sai sokuwa waina ku sammat,
Ba`a ab ba ta yi don kar a rammat,
A maisat shawarakanya faɗina.
Da Maryam Tambuwal kar dai ku manta,
Da Maryam tabbaci ta ɗarma
mata,
Da Mairamu Tambuwal huska akwai ta,
Mutunci ta fake ni kam ganina.
Da mata masu halaye karimi,
Da matayen Riɓa
mata na Zurmi,
Da Binta Chinoko mata masu ilmi,
Gurama Ingilishi godabe na.
Halinta muna yabawa ni da waccan,
Halinta ku tabbata ta zarce waccan,
Halinta kama da Binta ta Dikko waccan,
Da nic ce tai kama da wata da rana.
Da kamun kai na ce maku ta yi suna,
Da yin ladabi biyayya ba hiyana,
Da kamun kai da ɗa`a
ga amana,
Da tsoron Jalla ba su kama da arna.
Da mataye karimai kun ga na san,
Da kyau Safiya ɗiyar
Kyaftin ku dai san,
Da kyau Safiya ɗiyar
Abdallah na san,
Da alhairinsu sun wanke zufana.
Hijabi sun ka sa sun kauce jifa,
Hijabi kariya tamkar fa rumfa,
Hijabi sunka sa sun ɓoye
siffa,
Kamar Jarwal da Hausawan Madina.
Ku dai kula yanzu dai zan gargaɗe ku,
Ku gane Yarima bai daidai da Kuku,
Ku dai kula kar ku sa haɗama
a ranku,
Kamar wada Binta taz zama ni ganina.
Ana ƙamfarku can daji su ƙwanso,
Ana wanka da kyau an sanya soso,
Ana ƙamfarku har ku ma kuna so,
Katangar hanƙuri ku yi an nufina.
Maza gumba ta dutse zan faɗe
ku,
Maza zan waiwaye ku ina tuna ku,
Maza zan waiwayo ku ina yaba ku,
Yawan ladabinku tare da tanadina.
Sulaiman yanzu kai ne zan wa ƙaimi,
Sulaiman nai du`a`i sam muƙami,
Sulaiman bin Bawa Digi Karimi,
Kwaleji idekeshi mai murnar ganina.
Da Adamu Ila yau zan je gare shi,
Da Adamu Ila tilas zan kire shi,
Da Adamu Ila na Tsafe fa sa shi,
Hussaini Umar Ruwan-daɗi
Aminna.
Uzairu Haruna wa yas san ƙasarsu,
Uzairu na ce Bayajidda ƙasarsu,
Uzairu Haruna Daura ak ƙasarsu,
Biɗar
digirinsa yaz zaka mahiri na.
Da kau Idrisu yanzu ku zam tunawa,
Da kau noma gari nasu ba gazawa,
Da kau Idrisu Yusufu ɗan
Jigawa,
Sa`idu na Bangi Ali muzakkari na.
Mu zo wani jarumi zan ambace shi,
Mu zo mu gani a yau dai zan yabe shi,
Mu zo Ɗangulbi Ali muna ishe shi,
Da Ibrahim na es-es zarumi na.
Mutanen Kwantagora irin ganina,
Mutane ne na Gwamatse zarumai na,
Mutanen Kwantagora akwai amana,
Dalilin Abdu nis san ɗalibina.
Aminu karamci kun ga ya min,
Aminu garinsu ku zan tuna min,
Aminun Es Fada ba zai ɓace
min,
Dalilin Abdu Bayaro ɗan
uwana.
Ina zuba godiya domin tuna ku,
Ina waƙe ɗiyana
malamanku,
Ina zuba godiyata na yaba ku,
Rashin sunanku shi at tarnaƙina.
Zama sunan wasunku da ban gani ba,
Zama tilas na bar wasu ban faɗi
ba,
Zama sunan waɗansu
da ban sani ba,
A nan su nis sani ga irin sanina.
Akwai Sarki na Hausa na ce Kabiru,
Akwai zikiri akwai natsuwa Kabiru,
Akwai Abdulkarim Kano Kabiru,
Fasaha ag garai da mutumta juna.
Ga fuska sai ka ce Hillo na Mubi,
Ga fuska in yana duban madubi,
Ga fuska sai ka ce Liman ga dubi,
Wurin cika alƙawal shi yai suna.
Da Ya`u na Shehu tabbas na gidan nan,
Da Ya`u na Shehu Zariya jarumi nan.
Da Ya`u na Shaihu Zariya wa mutum nan,
Shi far mai kan sani faɗi
ɗalibina.
Da wannan ɗalibin
bai son husuma,
Da Adam Zariya zan sa shi, shi ma,
Da Adamu wanga Abdullahi shi ma,
Tsayayye na ga ilmin zamanina.
Abubakari na ce maku ɗan
ina ne,
Abubakari ganina salihi ne,
Abubakari na Ummaru Dange ɗa
ne,
Da yas san Jabru babban haziƙi na.
Sulaiman Zariya yau zo mu gaisa,
Sulaiman Salihu ilimi gare sa,
Sulaiman Salihu shi bai da wasa,
Wurin tsare gaskiya in dai faɗi
na.
Aliyu Kajuru ya zarce wa sako,
Aliyu Kajuru Sadauki na kadarko,
Aliyu Kajuru ɗan
Abdallah shi ko,
Halinsa ga ƙoƙari babban mutum na.
Zuwana Jami`a Allah Tabara,
Zuwana Jami`a na sami kara,
Zuwana Jami`a na iske yara,
Ɗiyan manyan mutane ɗalibaina.
Ku saurara maza mata ku ji ni,
Ku saurara aron kunne ku ba ni,
Ku saurara ɗiya
mata ku ji ni,
Ku kai caffa ga Binta tana da rana.
Kwaɗai
ab ta yi nono ga rugga,
Kwaɗai
ab ta yi gun ɗinka
riga,
Kwaɗai
ab ba ta yi ba ƙalla yanga,
Da jin izza gare ta abin gudu na.
Kamar wada an ka ce in Binta na nan,
Kamar wata Gimbiyar Sarki tana nan,
Kamar wada an ka ce kul Binta na nan,
Ga kamun kanta wane fasiƙina.
Ku bi ta a sannu ƙawaye kui abota,
Ku bi ta ku ɗauki
halayenta mata,
Ku bi ta ku ɗauki
halayenta kyauta,
Da sakarci da roƙo tasari na.
Ji Alhaji Haliru yau dai nai batuna,
Ji Alƙali ina yaba ɗalibaina,
Ji Alhaji Wurno Alƙali Halir na,
A can dai dauri yau kam mallamina.
Waɗanda
Alƙali
Hilliru Wurno Bai Ambace Su A Cikin Waƙar ba.
Sulaiman yanzu lissafo wasunsu,
Sulaiman yunƙura don ambato su,
Sulaiman gaisuwa kai ta gare su,
Dalili yanzu ai ba ni da suna.
Muna yin godiya Allah ya saka,
Muna yin godiya Allah ji ƙan ka,
Muna murna dalilin wagga waƙa,
Na Wurno karimi malamina.
Da juyawa a yanzu na ga waye,
Da waigawa a baya fa na kiyaye?
Abokai ne a can gefe ƙawaye,
Suna nan jere dukkan `yan ajina.
Na Katurunmu na ce Adamu Sani,
Na Katuru biɗo
mani ka ji Mani,
Na yo masa gaisuwa ya zam kula ni,
Mutum mai dariya mai kama kaina.
Sa`idu na Bangi yau na waiwaye ka,
Sa`idu na Bangi Allah dai ya saka,
Sa`idu na Bangi dole in yabe ka,
Mutum ne kamili tabbas in nuna.
Ina Bello na Bandiya yau ka gane,
Ina Bello na Bandi na ce mutum ne,
Ina Bello na Bandi muzakkari ne,
Mutum ne salihi a irin ganina.
Ina Sani na Yakubu ɗan
Bicin nan,
Ina Sani na Yakubu jarumin nan,
Ina Sani ku nemo min garin nan,
Farar fuska iwa huda ta rana.
Mu dai gaisa Muhammadu Namadina,
Mu je Anka mu gaisai ɗalibina,
Mu dai koyi ga Manzo ɗan
Amina,
Mutum ne salihi tabbas ganina.
Ina Yarawal fa Umaru dai karimi,
Ina roƙo ga Rabbi ka sam muƙami,
Ina ƙaunar sa tabbas bai da ɗumi,
Mutum ne kamili na so da ƙauna.
Muhammadu Altine na Maru Sahihi,
Muhammadu Altine jika ga Shehi,
Muhammadu tabbaci shi kam madihi,
Akwai ladabi akwai natsuwa ganina.
A ƙofar mata nemo Mustafa ne,
A ƙofar mata can ne za mu zaune,
A can ne Mustafa ya tafo ku gane,
Kanawan Dabo mun sabo da juna.
Akwai Bello na Wamba muzakkari ne,
Akwai Bello na Wamba yana ina ne?
Akwai shi ajin ga saurara ka gane,
Akwai ƙwazo karamci ɗalibi
na.
A Bakori Abubakari na san shi,
A nan ya taho fa ilmi zai biɗe
shi,
A can Katsina yake zaune gidanshi,
Ina Umar mutumin can Katsina.
Abubakari Mafara kana ina ne?
Abubakari fa babban ɗalibi
ne,
Abubakari cikakken ɗalibi
ne,
Ku nemo min Sama`ila jarumina.
Mutanen Zuru nai cigiya gare ku,
Mutanen Zuru ga saƙo gare ku,
Mutanen Zuru wa gwarzon cikin ku,
Ina Umar fa Yakubu sahibina.
Madomawa Ƙwazo ina ka je ne?
Madomawa garinsu fa jarimi ne,
Madomawa Muhammadu ɗalibi
ne,
Na ce Sani karimin jarimina.
Sulaimanu na Kumbashi karimi,
Sulaimanu mutum ne mai muƙami,
Sulaimanu mutum ne shi salami,
Akwai haƙuri da dattaku ganina.
Abubakari na Rabi`u ba ya wasa,
Abubakari a yanzu ina biɗar
sa,
Abubakari mu bi shi zuwa gidansa,
Garinsu ka bincika can ne Gumina.
Ina Mai Shehi Gayari kana ina ne?
Ina kake ne mu zauna salihi ne,
Ina Mai Shehi babban ɗalibi
ne,
Abubakari a yau ga gaisuwana.
Ina tuna Malami Sani na Jega,
Ina kake ɗalibi
mai kyau da riga,
Ina kai gaisuwa can ne fa Jega,
Ina yin godiya kai malamina.
Ina Lamiɗo
Dada na can Kanon nan?
Ina ne zan gano shi cikin ajin nan?
Ina adu`a da yaz zam ba shi dai nan,
Mutum ne haziƙi shi ɗalibina.
A ƙarshe Ummaru namu na Bunza,
A ƙarshe dole mai tauna ya furza,
A ƙarshe Umaru ya kai ga mazza,
Mutum ne jarimi a irin ganina.
Sulaiman na yi tarbi`i na waƙa,
Sulaiman na yi ƙari baiti waƙa,
Sulaiman Halliru Wurno na saƙa,
Muna yin godiya Hallir gwanina.
Muna yin godiya gun malaminmu,
Na Bayero Abdu Farfesa a ilmu,
Yahya tabbaci ya taimake mu,
Asiri gun salon waƙa gwanina.
Akwai wasu malamanmu ina yabawa,
Akwai Dunfawa malam bai gazawa,
Akwai malam fa Yakasan Kanawa,
Akwai Amfani Farfesan garina.
Akwai Iron Malumfashi ku duba,
Akwai Sa`adiyya Umar can ka duba,
Akwai Muhabub fa Alƙali na duba,
Gafuru ka gafarta masa nai addu`ana.
Akwai Ɗantumbushi zan so ganin ka,
Akwai ma Ɗahiru Arugungu naka,
Akwai saƙo na ce Allah ya saka,
Gare ku muna yin godiya duk malamaina.
Muna roƙon ka ya Allah ji ƙan mu,
Muna roƙon ka Aljanna ka ba mu,
Muna roƙo maza mata ɗiyanmu,
Mu san tsira Gafuru Ubangijina.
A yau dai sha tara na kammala ta,
A wanga wata na ce maku dai Agusta,
A yau dai shekara ta dubu biyunta,
A sa ashirin da ukku shekara na.
Manazarta
Abdullahi, B. (1983) “A Critical Anthology Of The Ɓerse
Of Alhaji Bello Giɗaɗawa.” Kano: Department Of
Nigerian Languages, Bayero Uniɓersity.
Unpublished M.A.Thesis.
Adamu A.U. (2007) Manuscript Learning Ability And Indegenous
Knowledge For Deɓt.
Hausa Ajami In Historical Conteɗt.
Nigerian Interlectual Heritage Proceeding Of An Internal Conference On Preserɓing Nigerian Scholar And
Literary Traditional And Arabic Ajami Manuscript Heritage. Arewa House, Ahmadu
Bello Uniɓersity,
Kaduna. Kaduna: Prime Publicity Nig. Ltd
Bargery, G.P (1934) A Hausa-English Dictionary And
English-Hausa Ɓocabulary. Zaria: Jami`ar Ahmadu Bello Press Ltd
Bello, G. (1993) “Baje Kolin Hajar Tunani.” Sokoto: Giɗaɗawa Press.
Bello, S. (2002) Rubutattun Waƙoƙin Hausa Na Ƙarni Na Ashirin A Jihohin
Sokoto Da Zamfara Da Kabi. Unpublished Ph.D Bayero Uniɓersity Kano
Bosso, M.A. (2010) Nazarin Ajami Cikin Hausa Don Makarantu
Manya Da Ƙanana.
Minna: Hasbunallah Printers
Birniwa, A.H. (1981) “The Imfiraji 1 And 4 Of Aliyu
Namangi.” London: Soas. Uniɓersity
Of London. Unpublished M.A Thesis.
Bugaje, M.H. (2011) Wa`Azi A Rubutattun Waƙoƙin
Mata Na Ƙarni
Na Ashirin. Zariya: Sashen Harsuna Da Al`Adun Afrika Tsangayar Fasaha Jami`Ar
Ahmadu Bello: M.A. Thesis
Bunza A.M. (2002) Rubutun Hausa Yadda Yake Da Yadda Ake
Yinsa. Lagos: Ibrash Islamic Publication Centre Ltd
Dangambo, A. (2007 ) Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa. Zaria: Amana Publishers.
Garba, S. (2011) Salon Sarrafa Harshe A Waƙoƙin Aƙilu
Aliyu: Zariya: Sashen Harsuna Da Al`Adun Afrika Tsangayar Fasaha Jami`Ar Ahmadu
Bello: Ph.D Thesis
Idris Y. (2016) Bijirewa A Waƙoƙin Siyasa: Bincike Kan Waƙoƙin
1903-2015: Zariya: Sashen Harsunan Afrika Da Al`Adu Jami`Ar Ahmadu Bello.
Malumfashi, A.I. (2010) Wa`azi A Rubutattun Waƙoƙin Ƙarni
Na Ashirin. Harshe 4 Jounal Of African Languages Sashen Koyar Da Harsunan
Nijeriya Da Na Afrika Jami`Ar Ahmadu Bello, Zariya
Malumfashi, A.I. (2019) Ɗanbuzuwar Akuya, Ko Bai Yi Gashin Ko`ina
Ba, Ya Yin A Katara: Aƙilu Aliyu Da Waƙoƙin Bijirewa Sashen Harsuna Da Al`Adun
Afrika Tsangayar Fasaha Jami`ar Ahmadu Bello Zariya
Malumfashi, I. (2019) Labarin Hausa A Rubuce: Zaria: Ahmadu
Bello Uniɓersity Press
Maniya, M.S. (2004) “Tarihin Sahabban Shehu. Sokoto: Al-Amen
Printing Press
Muhammad, D. (1985) “Ɓisual Imagery In Blind Poetry
Illustration From Namangi`s Imfiraji And Audu Makaho`s Tabuka.” Lagos: Nigeria
Magazine
Muhammad S.S (2011) Kwatancin Waƙar Jiddul Ajizi Ta Shitu Ɗan
Abdurra`uf Da Kanzil Azimi Ta Aliyu Namangi. .”Zariya: Department Of African
And Nigerian Languages. Unpublished M.A. Thesis
Muhammad, S.S (2018) Gudummuwar Marubuta Waƙoƙi
Wajen Yaƙar
Talauci A Ƙasa.
Nazari Daga Waƙar Gangar Wa`Azu Ta Malam Muhammadu Na Birnin Gwari. First
International Conference, Faculty Of Arts Kaduna State Uniɓersity, Nigeria
Mukhtar, I. ( 2005 ) Bayanin Rubutacciyar Waƙar
Hausa. Abuja: Countryside Publishers
Namangi, A. (1972) Waƙoƙin Imfiraji Juzu`I 1-4 Zaria:Northern
Nigeria Publ. Company.
Sarɓi
A.S. (2007) Nazarin Waƙen Hausa. Kano: Samarib Publishers.
Skinner, A.N. (1969 ) “A Hausa Poet In Lighter Ɓein’
African Language.” African: Language Reɓiew,
Ɓol.
8.
Sulaiman, S.M. ( 2010) Bazazzagiya. Zaria: Maigwado
Multi-Media
Sulaiman S.M. (2019) Matakan Nazarin Rubutacciyar Waƙa. Zariya:
Ahmadu Uniɓersity.
Press Limited
Tahir R.M. (2012) Ajamin Hausa. Don Ƙananan Makarantu. Zariya:
Yahaya Ɓentures
General Printers And Publishers
Yakawada, M.T (1983) “Waƙeƙeniya” Zaria: Department Of Nigerian And
African Languages, Ahmadu Bello Uniɓersity.
Unpublished B.A. Project.
Yakawada, M.T. (1987). “Tarkakken Matanin Waƙar
Kanzil Azimi Ta Aliyu Namangi.”
Zariya: Dept. Of Nigerian And African Languages, Ahmadu
Bello University.
Unpublished M.A. Thesis
Yahaya. I.Y ( 1988 ) Hausa A Rubuce. Zariya: Northern
Nigeria Publishing Company.
Yahya.A.B. (2016 ) Salo Asirin Waƙa. Sokoto: Guaranty
Printers Sokoto
Zaruk, R.M. Da Wasu (2006) ‘Sabuwar Hanyar Nazarin Hausa’
University Preess
PLC, Ibadan.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.