Ticker

6/recent/ticker-posts

Duk Yaran Da Muke Haifa Da Mijina Sikila Ne, Zan Iya Neman Ya Sake Ni Na Auri Wani?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum dafatan anwuni lafiya malam, dan Allah malam ina neman shawara ina da aure 'ya'yana ukku, na farko yana da shekaru bakwai (7 years) kuma yana da sikila na biyun yana da shekaru biyar (5 years) sai ta ukkun nada Shekarau biyu (2 years) itama tanada sikila watanta biyar yanzu da rasuwa, sai ɗayan Wanda baida sikilar ya fara ceman kafarshi na ciwo ba ayi awaba kuma hannunwanshi suma suka fara ciwo, sai duka jikin shima ya ɗauki ciwo, shima mai sikilar sai ya fara ciwan, muna zuwa asibiti aka basu gado muka kwanta sun tambaye mu Wanda bai da sikilar mun yi mashi awo ne mukace a'a, saboda tunda akai haifeshi bai taɓa ciwo ba sai mura da ɗan zazzaɓi shima na rana ɗaya ne yawarke to sunyi mana bayanin cewa wata sikilar na daɗewa kafin ta bayyana to sai ya rasu, shima ɗayan kwana ɗaya da rasuwar wancen sai ya rasu kuma kanwarsu wata biyar tsakaninsu hankalina ya tashi yanzu banda 'ya'ya kuma ni kaɗai ce wajen mijina, shi ya kuma faɗi mani dole yakara aure ni kuma ya ce sai nan da shekara goma yake san in haihu ni kuma inasan 'ya'ya kuma ina san mijina amma ban san in haihu da shi saboda na sha wahalar yara kuma jinin mune ɗaya kaga dole tinani ya dame ni, shin zan iya cewa mijina ya sauwake mani inje insamu wani Wanda zan iya haihuwa yara ba sikila ba?? dan ALLAH inasan Karin bayani nagode

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikum assalam, Tabbas Kina cikin damuwa da tashin hankali, Tun da kin zama Mai wabi. Allah ya shar'anta saki ne Domin tunkuɗe cuta daga ɗaya daga cikin ma'aurata Ko dukansu Kamar yadda ayar Suratun Nisa'i ta tabbatar da hakan. Mutukar kin ga a cigaban zamanku akwai cutarwa kina iya neman rabuwa da shi Ko ta hanyar saki Ko fansar kai. Yana daga cikin manufofin aure samun zuriyya waɗanda za su ɗebe kewa. Idan Kuka rabu Allah zai iya azurta kowa daga falalarsa, ya ba ki miji ya kuma ba shi matar da in sun haɗu ba za su haifi Sikila ba.

Allah ne mafi sani

Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments