𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum warahmatullah.
Malam barka da yamma, so nake don Allah malam a qara mana bayani kan qabli da
ba'adi, da kuma dalilan da ke sa a yi su. Allah ya saka wa malam da alkhairi.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salamu.
SUJJADA QABLIYYA: ita ce sujjada
guda biyu da ake yi kafin a yi sallama ta dalilin rage wani aiki daga cikin
ayyukan sallah da mantuwa.
Sujjada qabliyya sunnah ce ba
farilla ba. Ana yin sujjada qabliyya ce bayan mai sallah ya kammala karatun
tahiya, kafin ya yi sallama sai yayi kabbara ya yi sujjadu guda biyu, daga nan
sai ya sake yin tahiya ya yi sallama. Wasu malaman kuma suka ce ko bai sake yin
tahiya ba, zai iya yana gama sujjadan ya yi sallama.
Idan kuma mai sallar da sujjada
qabliyya ta same shi ya mance bai yi ta ba har sai bayan ya yi sallama, to babu
laifi, sai ya yi sujja ba'adiyya (sujjada bayan sallama) a madadinta.
Amma ba duk ayyukan sallah ne
idan aka mance aka rage su ba ne sujjada qabliyya take isar masu ba, sujjada
qabliyya tana isarwa ne kawai a lokacin da mai sallah ya mance da sunnah ɗaya ko biyu ko fiye daga
cikin sunnonin sallah, misali mutum yana sallah sai ya mance da kabbarori biyu,
ko ya mance da faɗin
'Sami'allahu liman hamidahu' sau biyu, ko ya mance da zaman tahiya ta farko a
sallah mai raka'a uku ko mai raka'a huɗu,
to a irin nan ne sujjada kafin sallama (Sujjada qabliyya) take isarwa.
Wato kenan sujjada qabliyya ba ta
isarwa ga mai sallar da ya mance da wani farali daga cikin farillan sallah.
Wannan na nufin idan mai sallah ya mance da wani farali daga cikin farillan
sallah dole ne sai ya koma ya yi wannan farali da ya mance da shi, misali
mutumin da ke sallah, a maimakon ya yi sujjada guda biyu kamar yadda aka saba
kawai sai ya yi sujja ɗaya,
ya mance ya miqe zuwa raka'a ta biyu, to a nan hukuncinsa dole ne ya dawo ya yi
wannan cikon sujjada ɗaya
da ya mance da ita, sannan ya miqe ya ci gaba da yin raka'a ta gaba, bayan kuma
ya idar da sallarsa sai ya yi sujjada ba'adiyya.
Wannan misali kenan a sujjada,
haka hukuncin yake a sauran farillan sallah, kamar karatun Fatiha, da ruku'u,
da ɗagowa daga ruku'u,
da sauransu. Duka waɗannan
idan mutum ya mance da su a cikin sallah, to dole ne sai mutum ya koma ya kawo
su, sannan kuma bayan ya kawo su, idan ya idar da sallarsa ya sallame zai yi
sujja bayan sallama wato (sujjada ba'adiyya)
Wato kenan dai a taqaice, sujjada
kafin sallama ba ta isarwa ga gyara sallar da aka mance da farilla daga cikin
farillan sallah har sai an koma an yi wannan farillan da aka mance da ita kamar
yadda malaman Fiqhu suka ayyana.
SUJJADA BA'ADIYYA: ita ma sunnah
ce. ita ce sujjads guda biyu da ake yin su bayan an sallame sallah ta dalilin
wani qari da aka yi a cikin sallah da mantuwa. Misali mai sallah ya mance ya
qara raka'a ɗaya ko
biyu ko uku a sallar Azahur ko La'asar ko Isha'i, ko ya mance ya qara raka'a
biyu a sallar Magriba, ko ya mance ya qara raka'a ɗaya a sallar Asubahi, to duk wanda ya sami
kansa a ɗaya daga
cikin irin wannan hali, zai yi sujjada biyu ne bayan ya yi sallama, wato
sujjada ba'adiyya kenan.
Amma malaman Fiqhu sun ce: Duk
wanda ya qara yawan adadin raka'o'in sallah, to sallarsa ta ɓaci. Misali mai sallar
Asubahi ya mance ya qara raka'a biyu suka zama raka'o'i huɗu, ko kuma mai sallar
Azuhur ko La'asar ko Isha'i ya mance ya yi raka'a takwas, ko mai sallar Magriba
ya mance ya yi raka'a shida, to duka waɗannan
sallarsu ta ɓaci kamar
yadda Malam Abdurrahman mai littafin Ahdhari ya ambata.
Har-ila-yau, wanda ya mance ya
qara sujjada ta uku a wata raka'a daga cikin raka'o'in sallarsa, ko ya mance ya
yi ruku'u sau biyu a cikin wata raka'a daga cikin raka'o'in sallarsa, ko ya
mance ya yi zaman tahiya a raka'a ta farko a cikin sallarsa, ko ya mance ya
qara yin zaman tahiya a raka'a ta uku a sallah mai raka'a huɗu, to duka hukuncin wannan
shi ne yin sujjada bayan sallama, wato sujjada ba'adiyya. Wannan dai a taqaice
kenan.
WATA FA'IDA: Malaman Fiqhu sun
ce: Duk wanda ya yi ragi ya kuma yi qari a cikin sallarsa zai yi sujjada kafin
sallama ne, wato sujjada qabliyya, saboda ana rinjayar da ɓangaren ragi ne a kan ɓangaren qari. Misali mutum
yana sallah, sai ya mance ya qara sujjada ɗaya
a ɗaya daga cikin
raka'o'in sallarsa a maimakon biyu sai suka zama uku, sannan da ya matsa gaba
sai ya mance da faɗin
'sami'allahu liman hamidahu' da kuma wata kabbara guda ɗaya, to a nan hukuncinsa zai yi sujjada ne
kafin sallama, domin ɓangaren
ragi yana rinjayar ɓangaren
qari ne.
Allah ne mafi sani.
Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
HUKUNCIN WANDA YA MANTA DA
SUJJADA KABLI KO BA'ADI
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Tambayata itace
shin menene hukuncin wanda yamance sujada kabli ko ba'adi yayinda ta kama shi?.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam Warahmatullahi
Wabarkatuhu.
Imam Mardaawi (Rahimahullah) yace
acikin Al-musannaf (2/154) na Ibn Qudamah: A rankon sajadar mantuwa Akwai
sharadi guda biyu.
1. Ya kasance cikin masallaci.
2. Ya kasance aikin baiyi tsawo
ba.
Ma'ana ba'a samu tazarar lokacin
yin mantuwar da tinawa ba.
Wannan shine ra'ayi mai kyau
kamar yadda Al-Mardaawi yace. Imam Ahmad (rahimahullah) yace; Zaiyi sajadar ne
idan ya tina anan kusa. Koda kuwa ya fita daga masallacin ne. Kuma yace zaiyi
sajadar koda bayan lokaci mai tsawo ne ya tina, ko kuma yayi magana, ko kuma
har bayan ya fita masallaci ne. Wannan shine ra'ayin da Shaykhul Islam Ibn
Taymiyyah ya zaba.
Al-Ikhtiyaaraat al-Fiqhiyyah,
Shafi na 94).
Idan mutum ya manta sujudar
mantuwa wacce zaiyi kafin sallama (Sajadar Qabli kenan), har ya sallame bai
tina ba, toh zaiyi sujudar qablin ne anan take kuma wajibi ne yinta (idan ya
tina anan kusa).
Amma idan kuma ya sallame kuma
Bai tina ba har sai bayan an ɗauki
lokaci mai tsawo, ko ya fita daga masallaci, ko alwalarsa ta warware. Toh anan
babu bukatar yin sajadar mantuwa, kuma sallasa ta inganta. Al-Rawd al-Murabba’
Sharh Zaadal Mustaqna’ (2/461)
MISALI: Idan mutum ya manta
tahiyar farko, anan sajadar qabli ta kamashi, toh sai ya manta ya sallame
batareda yayi qabli ba, toh zaiyi qablin ne idan ya tina nan take.
Amma idan bai tina ba anan kusa
har sai bayan wani lokaci mai tsawo ko ya fita masallaci, toh anan bazai yi
sajadar qablin ba kuma sallarsa tayi.
Shaykhul Islam Ibn Taymiyyah yace
zaiyi sajadar ne idan ya tina, koda ya tina ne bayan lokacin mai tsawo. Saboda
hakan zai zama cikon abinda ya bari ne a sallarsa.
Amma Ra'ayin da yafi kyau shine
ra'ayin Mawallafin (rahimahullah) Wanda shine idan bai tina ba sai bayan lokaci
mai tsawo, toh bazai rama sajadar ba kuma sallarsa tayi. Idan kuma ya tina anan
kusa zaiyi sajadar.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.