Ticker

6/recent/ticker-posts

Neman Gafara Kafin Ramadan

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum. Saƙonnin da ake turawa ta social media na neman gafara daga mutane kafin shigowan Ramadan, da gaske wai hakan Sunnah ne? Akwai wani hadisi ne a kan hakan?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah.

Ni dai ban san wani hadisi da ya kwaɗaitar da cewa kafin shigowar watan Ramadan mai albarka a nemi jama’a gafara a kan zunuban da aka aikata musu ba. Haka kuma ban san wani hadisi da ya nuna akwai wata falala ga wanda ya sanar da jama’a ranar da watan Ramadan zai kama ba.

Muna tsoron duk waɗannan su zama daga cikin ƙarairayi ne da ake ƙirƙirawa ana jinginawa ga Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam). Wannan kuwa kowa ya san haram ne, saboda hadisai sahihai masu yawa da suka zo a kan haka, kamar abin da Al-Imaam Muslim ya riwaito a Muqaddimar littafinsa As-Saheeh, a babin (Wajibcin Riwaya Daga Amintattu Da Barin Riwayar Maƙaryata), daga Samurah Bn Jundub da Al-Mugheerah Bn Shuubah (Radiyal Laahu Anhumaa) cewa: Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce

« مَنْ حَدَّثَ عَنِّى بِحَدِيثٍ يُرَى أَنَّهُ كَذِبٌ فَهُوَ أَحَدُ الْكَاذِبِينَ »

Duk wanda ya bayar da wani hadisi daga gare ni wanda kuma ake tsammanin shi ƙarya ne, to shi (mutumin) ɗaya daga cikin maƙaryata ne. (Sahih Muslim: 1)

Haka kuma Al-Imaam Al-Bukhaariy a cikin Kitaab: Al-Ilm, Baab: Ithmu Man Kazzaba Alan Nabiy (Sallal laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya riwaito da isnadinsa sahihi har zuwa daga Anas (Radiyal Laahu Anhu) cewa: Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce

« مَنْ تَعَمَّدَ عَلَىَّ كَذِبًا فَلْيَتَبَوَّأْ مَقْعَدَهُ مِنَ النَّارِ »

Duk wanda da gangar ya ƙaga mini ƙarya, to ya nemi mazauninsa a cikin Wuta. (Sahih Al-Bukhaariy: 108)

Wannan hadisi ne mutawaatir, domin sahabbai sama da sittin suka riwaito shi daga Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam), kamar yadda malamai suka faɗa. (Dubi: Sahih Al-Jaami’: 2837).

Don haka dai wajibi ne musulmi su yi taka-tsantsan a kan yaɗa duk abubuwan da suke ji da gani musamman a cikin kafafen yaɗa bayanai na zamani irin su: Twitter da Facebook da Whatsapp da Telegram da sauransu. Kafin mutum ya tura wani abu ya yi ƙoƙarin tabbatarwa ko samun marinjayin zato a kan sahihancinsa daga malamai a kusa ko a nesa da shi tukun, don kar ya shigar da kansa a cikin waɗannan da hadisai suka yi magana a kansu.

Amma fa neman gafara da neman yafiya daga ’yan uwa, da ƙoƙarin samu ƙarin aminci da fahimtar juna a tsakanin musulmi kyakkyawan abu ne da ake nemansa a koyaushe ba sai a watan Ramadan kaɗai ba. Keɓance watan Ramadan da yin hakan har da cewa wai ma Sunnah ce ta Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ne, shi ne muke cewa ba mu san hakan ba. Janyo gamammun ayoyi ko hadisai a kan kyautatawa ko yawaita ayyukan alkhairi a cikin Ramadan a nan ba su isa dalilai ba. Sai a kiyaye.

Allaah ya ƙara mana fahimta da shiriya gaba-ɗaya.

WALLAHU A'ALAM

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/J1hm5Tw12uYBqfaiPwf28l

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments