𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salamu Alaikum, ina da ƙaramin
ciki wanda bai kai wata uku ba, kuma ga shi ina fama da matsalar jin yunwa.
Domin daga safe zuwa dare nakan ci abinci aƙalla sau bakwai (7). Idan kuma ban ci ba,
ina wahala sosai. Wani zubin ma ko tashi ba na iyawa. Don Allaah! Yaya zan yi?
Ga kuma Ramadan?!
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul
Laah.
Da farko dai ina ga zai yi kyau
ki tuntuɓi likitoci
da sauran masana harkar lafiyan masu ciki, domin ki samu tabbacin ko wannan
matsalar ta yawan ci babba ce ko kuma ba wata babbar matsala ce abin tsoro ba a
gare ki. Domin cin abinci har sau bakwai a yini guda a cikin halin rayuwar yau
ba ƙaramar
magana ba ce, musamman ga talaka mai ƙaramin ƙarfi.
Allaah ya sa dai lafiya.
Dangane da hukuncin azuminki
kuwa, wannan malamai sun sha bamban a cikinsa. Amma dai abin da muka fi natsuwa
da shi, shi ne ra’ayin waɗanda
suka ce: Matar da ta kasa yin azumin Ramadan saboda matsalar ciki ko matsalar
shayarwa, to sai ta bayar da abinci ga matalauci a maimakon duk wani yinin da
ba ta yi azumin ba.
Dalili kuwa: Allaah Maɗaukakin Sarki ne ya ce
وَعَلَى ٱلَّذِینَ یُطِیقُونَهُۥ
فِدۡیَةࣱ طَعَامُ مِسۡكِینࣲ
Kuma abin da yake a kan waɗanda suke ɗaukarsa da wahala shi ne
fansa: Ciyar da abinci ga musakai. (Suratul Baƙarah: 184.)
Game da wannan ayar, Abdullahi
Bn. Abbas (Radiyal Laahu Anhumaa) ya ce: 'A kan wannan: An yi wa tsoho da
tsohuwa ne sassauci, waɗanda
suke ɗaukar azumin
da wahala cewa: Su ajiye azumin in sun ga dama, kuma su ciyar da abinci ga
matalauci a maimakon duk yinin da ba su yi azumin ba, kuma babu ramuko a
kansu.’
Har zuwa inda ya ce: ‘Ya tabbata
a kan tsoho da tsohuwa idan ba za su iya yin azumin ba, haka kuma mai ciki da
mai shayarwa idan suka ji tsoro: Sai su ajiye azumin kuma su ciyar da abinci ga
musakai a maimakon duk yinin da suka sha azumin.’
(Sahih Al-Bukhaariy: 4505).
Sannan kuma Anas Bn Maalik
Al-Ka’abiy (Radiyal Laahu Anhu) ya riwaito daga Annabi (Sallal Laahu Alaihi wa
Alihi wa Sallam) ya ce
إِنَّ اللهَ تَبَارَكَ وَتَعَالَى وَضَعَ عَنِ
الْمُسَافِرِ شَطْرَ الصَّلَاةِ ، وَعَنِ الْحَامِلِ وِالْمُرْضِعِ الصَّوْمَ
Lallai Allaah mai Albarka da Ɗaukaka
ya yafe wa matafiyi rabin sallah, kuma ya yafe wa mai ciki da mai shayarwa
azumi.
(Abu-Daawud, An-Nasaa’iy, da At-Tirmiziy, da
Ibn Maajah suka riwaito shi)
Yafe musu azumin yana nufin za su
bayar da fansar abinci ne. Haka manyan malamai guda biyu daga cikin sahabbai:
Ibn Umar da Ibn Abbaas (Radiyal Laahu Anhumaa) suka bayar da fatawa:
Ad-Daaraqutniy ya riwaito da wani
isnadin da Al-Albaaniy a cikin Al-Irwaa’u: 4/19 ya ce: Nagartacce ne, daga Ibn
Abbaas (Radiyal Laahu Anhumaa) cewa: Shi ya ga wata baiwarsa mai ciki ko mai
shayarwa, sai ya ce: Ke kina matsayin wanda ba zai iya ba ne. Wajibinki shi ne:
Ciyar da abinci ga talaka a maimakon duk yinin da ba ki yi ba, kuma babu ramuko
a kanki.
Haka nan dai ya sake riwaitowa
daga Ibn Umar (Radiyal Laahu Anhumaa) cewa: Wata matarsa ta tambaye shi alhalin
tana da ciki, sai ya ce: Ki ajiye azumin, ki ciyar da abincin talaka a maimakon
duk yinin da kika ajiyen, kuma kar ki rama.
(Dubi: Irwaa’ul Ghaleel: 4/19-20).
Sannan kuma a cikin Sahabbai ba a
samu wanda ya saɓa
musu ba. Sannan kuma ayar (waɗanda
suke ɗaukarsa da
wahala) ta haɗe duk
da su, kuma a cikinta ba ambaci komai ba sai dai ciyarwa kawai. Haka Ibn
Qudaamah ya ambato a cikin Al-Mughnee: 4/395, kamar yadda ya kawo a cikin
Tamaamul Minnah: 2/166.
Kuma yadda ake ciyarwar shi ne
kamar yadda Sahabi: Anas Bn Maalik Al-Ansaariy (Radiyal Laahu Anhu) ya nuna ne
أَنَّهُ ضَعُفَ عَنِ الصِّوْمِ عَامًا فَصَنَعَ
جَفْنَةَ ثَرِيدٍ ، وَدَعَا ثَلَاثِينَ مِسْكِينًا فَأَشْبَعَهُمْ
Lokacin da ya kasa yin azumi a
wata shekara, sai ya shirya abinci masaki guda, ya gayyaci musakai talatin, ya ƙosar
da su.
(Ad-Daaraƙutniy ya riwaito shi, kuma isnaadinsa
sahihi ne, in ji mai littafin: Irwaa’ul
Ghaleel: 4/21).
WALLAHU A'ALAM
Sheikh Muhammad Abdullaahi
Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.