Ticker

6/recent/ticker-posts

Miyar Gauta Ko Data Ko Dwata

Gauta ɗaya ne daga cikin ’ya’yan tsiro da ake samu a ƙasar Hausa. Ƙanana ne masu siffar attaruhu. Sai dai a maimakon zafi da attaruhu ke da shi, gautaytana da ɗanɗano ne mai ɗaci-ɗaci. Baya ga haka, akwai nau’in gauta da ke da matsakaicin girma. Irin waɗannan ba su fiye ɗanɗanon ɗaci ba, sai dai ɗanɗano main zaƙi-zaƙi kaɗan.

Mahaɗin Miyar Gauta (Ɗwata)

Akwai abubbuwan da za a tanada, idan za a haɗa miyar ɗwata.

i. Albasa         

ii. Daddawa   

iii. Gishiri        

iv. Kayan yaji

v. Mai              

vi. Ruwa        

vii. Tarugu      

viii. Tattasai

ix. Wake          

x. Ɗwata

Yadda Ake Miyar Gauta (Ɗwata)

Ita ma miyar gauta idan za a yi ta, akan jajjaga tattasai da tarugu da albasa a daka kayan yaji da daddawa da tafarnuwa. Bayan haka, sai a surfe wake a kuma wanke sannan a aje gefe. Daga nan za a soya jajjage tare da mai. Idan ya soyu, sai a saka daddawa a zuba wake a ciki, sannan a ɗan ƙara soyawa kaɗan. Bayan sun soyu tsaf, sai a saka gishiri a zuba ruwa, wato dai a yi sanwa. Daga zarar sanwa ta tafasa, za a matso da gautan da aka riga aka yanka sannan aka wanke.[1] Yayin da miyar gauta ta dafu takan warwatse ne tamkar guro. Abin da ya rage shi ne saka maburkaki a kaɗa, sai kuma sauke tukunya. Kusan akan ci miyar gauta da kowane irin tuwo.

Tsokaci 

Mutanen Burma suna daga cikin masu yawaita amfani da wannan nau’in miya. Sannan yawanci mata sun fi maza shan miyar gauta. Wannan bai rasa nasaba da tasirin da miyar take da shi wajen ƙara wa mai jego ruwan nono. A dalilin haka ne ma ake nuna buƙatar yin amfani da wannan miya ga mai jego, musamman ga yankunan da ake amfani da miyar sosai. Yara ba su fiye son wannan nau’in miyar ba, wanda hakan na faruwa ne a dalilin ɗan ɗaci-ɗaci da kuma bauri-bauri da take tattare da shi. Daga cikin garuruwan Hausawa da suke amfani da ita sosai akwai, Kano da Zazzau da Niger da Katsina da Zamfara da kuma Kabi da sauransu.



[1] Wani lokaci akan sanya gautar ba tare da an yanka ba. A irin waɗannan lokuta, da kansa gautan yake warwatsewa a cikin miyar. 

The book “Cimakar Bahaushe” (Diets of the Hausa People) is a collection of 293 traditional and modern diets of the Hausa people. Detailed explanations of the recipes and ingredients are provided. Comments are provided on the areas of the Hausa land where specific diets are mostly found, the age categories of people that usually use it, as well as the scientific impact of some of the diets to human biology.  Data is collected from interviews with different categories of people including:  i.                    Food sellers within the Hausa land: Mainly to have an idea of recipes on the diets.  ii.                  People of older age: Mainly to have insights on traditional diets of the Hausas.  iii.               Hausa scholars: Mainly to verify and justify the validity of the information obtained as well as provide further expert explanations on the diets.  Moreover, over two hundred (200) pieces of literature were reviewed to have better insight on the topic in question as well as get scientific and professional clarifications on some key concepts relevant to the research. The pieces of literature cover major relevant phenomena such as diet and hunger. Others are on the Hausa land and the Hausas.  The book contains thirty-three (33) chapters. Chapter one is the main introduction in which a concise explanation is provided on the Hausas, their history, their land, social life, and transformations due to globalization, acculturation, and modernity. Chapter two detailly discusses the concepts of diet and food from the Hausa point of view. That includes the meaning and the usage of diets in some Hausa works of literature both verbal and written (i.e. prose, poetry, proverbs, etc.).  Chapters three and four discuss the sources of Hausa diets and their forms accordingly. Chapters five to seventeen discuss some traditional Hausa diets including hard and soft ones. Chapter eighteen concentrates on the influence of modernity and globalization on Hausa diets. It has been discovered that there have been some significant changes in the Hausa diets ranging from recipes to kitchenettes.  Chapters nineteen to thirty-two discuss modern Hausa diets. Some traditional diets are still retained with little modifications, while on the other hand, there are a lot of new ones. Chapter thirty-three discusses “hunger” from the Hausa point of view. The relationship between hunger and food is examined. Additionally, the use of hunger in various Hausa literary works is studied. It is concluded that hunger is like a disease whereby its cure is food.  7th November 2022
Citation: Sani, A-U. & Umar, H.A. (2022). Cimakar Hausawa. Kano: WT Press. ISBN: 978-978-984-562-9.

Get a copy:
To obtain a copy of this book, kindly send a WhatsApp message to:
+2348133529736

You can also write an email to:

Post a Comment

0 Comments