𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Akkaramakallahu barka da war haka. Allah
ya qara basira da nisan kwana. Malam ina da wata tambaya ne wacce wani ya
tambayeni ita, Haqiqa tambayar tafi qarfina shine Nace masa ya bari zan tambayo
masa nima. Malam Yana tambayar Halaccin Auren wata yarinya da yake nema ne,
Amman abin cikensa ya gano Cewa Ya taɓa
soyayya da uwar yarinyar a Wani gari can shekarun baya da suka wuce Har sun
ta6a Zina da uwar. Yanzu Kuma ya tsinchi kansa a wannan yanayin, A cewarsa
Yanzu sun shaqu da yarinyar har sun fara maganar Aure, Amman fa yarinyar Bata
San wannan labarin ba. To shine yake tambayar Ya halatta ya cigaba da neman
auren yarinyar ko Kuma Aure ya haramta a tsakanisu Saboda wannan dalilin? Allah
ya taimaki Malam wannan ita ce tambayar.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Ita zina haramun ce. Kuma babu saɓani atsakanin malamai game da girman laifin
dake cikinta, Amma duk da haka bata haramta abinda aure ke haramtawa.
Don haka ya halatta ka auri ita wannan yarinyar mutukar dai
ba kaine kayi sanadiyyar zuwanta duniya a wannan zinar da kayi da mahaifiyarta
ba.
Ibnu AbdilBarri acikin littafinsa Al Istizkar (Juz'i na 5
shafi na 463) ya ce "Malamai sunyi saɓani
game da shin idan mutum yayi zina da wata mata, shin ya halatta gareshi ya auri
'yarta ko mahaifiyarta? Ko kuma idan ya taɓa
aikata zina da wata mace, shin ya halatta Ɗansa ko mahaifinsa ya aureta? Shin zina
tana haramta abinda aure ke haramtawa?
Malik ya faɗa
acikin Muwatta cewa "Yin zina da mace ba zai sanya mutumin da yayi zinar
da ita ɗin ya
haramta ga 'Yarta ko mahaifiyarta ba. Amma idan mutum ya aikata zina da
mahaifiyar matar da yake aure, to wannan bazai sanya matarsa ta haramta gareshi
ba, sai dai za'a yanke masa hukuncin kisa ne (ta hanyar jefewa) zina bata
haramta abinda halastaccen aure ke haramtawa.
Wannan shine fatawar Ibnu Shihab Azzuhriy da Rabee'ah, kuma
ita ce fatawar Laythu bn Sa'ad da Shafi'iy da Abu Thaur da Dawuduz Zahiriy kuma
ita ce fatawar Abdullahi dan Abbas (ra).
Karshen abinda na cirato daga chan ɗin kenan. Amma wasu malaman suna bada
shawarar cewa kada mutum ya auri 'yar matar da ya taɓa zina da mahaifiyarta saboda yin hakan zai
Qara sanya yawan haɗuwa
ko chudanya tsakaninsa da waccen matar (wato uwar matarsa) saboda gudun kada
shaiɗan ya sake rinjayarsu
zuwa ga komawa cikin laifin nan da suka taɓa
aikatawa.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.