𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamualaikum dafatan malam yana cikin koshin lafiy Amin. malam ni tambayata ita ce yana da kyau mutum yayi sallar Tahajjud a masallaci?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam Warahmatullahi
Wabarkatuhu.
Annabi Sallallahu alaihi Wasallam
yace “Mafificiyar sallarku (tahajjud) wacce kuka yita a gidane sai dai sallar
farilla kawai ”(Dubi Tirmizi Bisharhil Ahuz 2\00).
An ruwaito acikin Bukhari
mafificiyin sallar mutum a gidansane sai dai sallar Farilla kawai.
(Dubi Fathul Bary 3\0 ko Umdatul
Qary.
Acikin Hadisin Abdullahi bn Sa,ad
yace “Na tambayi Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam akan sallar mutum
tahajjud a gidansa dayinta a masallaci wanne yafi? sai Annabi Sallallahu alaihi
Wasallam yace “shin baka ganin gidana ba wanda yafi shi kusa da masallaci, amma
nayi sallah a gidana (tahajjud ) yafi nayi sallah amasallaci sai dai sallar
farilla” (Dubi Ibn Majah 1\39).
An karbo daga Zaidu bn Sabit (RA)
daga Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam yana cewa “Sallar mutum agidansa
tafi sallarsa a masallacina. (wato masallacin Annabi). sai dai sallar
farilla”(Dubi Abu Dawud 1\9, taglikutta aliq 1/ 239 Nailal Audar 3\5 ko Ash
shama,il 150).
Don haka yin nafilar tahajjud a
gida yafi yinta akowani masallaci falala. tunda Annabi Sallallahu alaihi
Wasallam yafifita nafila agidage a bisa masallacinsa.
Ananne Hafizu bn hajar yake cewa:
yin tahajjud agida lallai shiyafi falala ga al’umma gaba ɗaya, domin shine amsar da
Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya baiwa mai tambaya, fatahul bary juzu’I na
3 shafi na 25\6 Abu daud juzu’I na1 shafi na 69 Tajujjami’u juzu’I na 1 shafi
na 332 Nailul Audhar juzu’Ina 3 shafi na 95 Tagliqutta’aliq juzu’I na 1 shafi
239 Ashshama’il shafi na 157
Amma duk da haka rafkanannu
acikin garuruwan kasannan (Nigeria) suna karfafa mata akan fitowa masallaci da
tsakar dare domin yin sallar Tahajjud. Alhali Annabi Sallallahu alaihi Wasallam
yace da ummu Humaidu Allah ya yarda da ita, yayin da tazo gurin Manzon Allah
Sallallahu alaihi Wasallam tace “ Ya Rasulullahi inaso nayi sallah tare da kai”
sai yace “Na sani kinaso kiyi sallah tare dani, amma kiyi sallah a’yar kurin ɗakinki yafi kiyi sallah a
falonki, kiyi sallah a tsakar gidanki yafi kiyi sallah a masallacin mutanenki,
kuma kiyi sallah a masallacin mutanenki yafi kiyi sallah a masallacina
wannan”.(Ahmad ne ya ruwaito 6\71 da Ibn Khuzaima acikin sahihinsa 3\5 da Ibn Abdul
Barri acikin Tamhid 23\98).
Wannan yana nuna sallar mace ta
farillah a cikin gidanta yafi tayi a masallaci to yaya kuma Nafila. Donhaka yin
tahajjud a gida yafi yinta a masallaci a wajen mace ko namiji.
WALLAHU A'ALAM
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.