𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Wanda yake cikin azumi sai kuma ya suma, daga baya kuma sai ya farfaɗo. Shi ne ake tambaya: Azuminsa na nan ko ya karye?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul
Laah.
Kamar yadda shari’ar Manzon
Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ce take da ikon bayani a kan
yadda ake yin kowane aikin ibada har da Azumi, to ita ce dai take da ikon
bayanin abubuwan da suke karya Azumin.
A cikin duk abubuwan da suka zo a
cikin Al-Kitaab Was Sunnah game da masu ɓata
azumi, babu ɗaya da ke
nuna cewa gushewar hankalin mai azumi ta hanyar suma yana ɓata azumin!
Don haka dai, gushewar hankali ta
hanyar barci ko suma ko farfaɗiya
ma, ba su ɓata azumi.
Idan ya farfaɗo sai
kawai ya yi alwala, ko kuma wanka ya cigaba da sallah da azuminsa.
Allaah ya warkar da duk marasa
lafiyan cikinmu, ya sa larurarsu ta zama kaffara ga laifukansu.
WALLAHU A'ALAM
Sheikh Muhammad Abdullaah
Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.