Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Farin Ruwa Ko Wani Danshi-Danshi Dake Fitowa Ta Gaban Mace

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Menene hukuncin wani farin ruwa ko wani danshi-danshi dake fitowa Mace ta gabanta (farji), Shin idan ta ganshi a pant ɗinta lokacin da zatayi Sallah dolene saita cire pant ɗin kokuma zata iyayin Sallah dashi ahaka?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Dangane da Magana akan Farin-Ruwan dake fito daga farjin Mace Mālamai sunyi Saɓāni akansa

1. Qauli nafarko shine Mazhabin SHĀFI'IYYA dakuma HANĀBILA Suntafine akancewa ruwan dake fitowa daga Farjin-Mace mai tsarkine danhaka koda yātaɓa tufāfinta to zata iyayin Sallah dashi ahaka bāsai tā wankeba, sukace bābu wani dalilin dayazo yanuna cewa wannan ruwan ba mai tsarki bane, kuma dama a Asali komai amatsayin mai tsarki yake sai in ansāmu wani dalilin da yazo yace abu Kazā-da-Kazā bā mai tsarki bane

2. Qauli nabiyu kuma shine Mazhabin MĀLIKIYYA da HANAFIYYA Suntafi akan cewa ruwan dake fita daga farjin Mace najasāne, danhaka idan yataɓa tufāfi to dolene sai anwankeshi sannan ayi Sallah dashi, to amma Maganar datafi INGANCI acikin Zantukan da Mālamai sukayi itace, Alal-HaQiQā wannan ruwa kokuma danshin dake fita daga Farjin-Mace ba najasa bane, Saboda ba'asamu wani dalili dayanuna cewa najasa neba.

Bāya gahaka kuma Sai Mālamai suka sākeyin wani Sabānin akancewa Shin ko fitar wannan ruwan yana'iya warware Alwala kokuma ā'ā?

Mafi rinjayen Mālamai sukace fitarsa yana warware alwala, domin sunaganin cewa ruwan dakefita daga Farjin-Mace hukuncinsa daidai yake da hukuncin Mace Mai jinin Istahāra, shiyasa suka kafa hujja dacewa Mαиzoи Aʟʟαн (Sallallahu alaihi Wasallam) Yā umarci Mai jinin Istahāra dacewa tariƙayin alwala akowacce Sallah, danhaka sukace shima wannan Danshin ko ruwan dake fita daga farji za'a riskar da hukuncinsane da na mai Istahāra

Amma agefe ɗaya akwai Mālaman dasuke ganin cewa fitar wannan ruwa baya warware alwala kamar yadda (Ibn-Hazm) Yakāwo acikin littafinsa maisuna: (Al-Muhallā-Bil-Āsār) to saidai Mālamai dayawā sukace wannan Maganar tasa bashida wani ingantaccen dalili akanta

Danhaka kenan Maganā mafi inganci acikin zantukan da Mālamai sukayi akan wannan Mas'ala itace, cewa ruwan dake fitowa daga Farjin-Mace idan yakasance yāfitone daga cikin asalin mahaifā (wanda kuma dāmā gālibi ta mahaifar yake fitowa) sukace to ruwane mai tsarki danhaka koda yātaba tufafi ko Pant to za'a iyayin Sallah dashi bātare da an wankeba, amma idan wannan ruwa yāfitone daga ƙofar da fitsāri yake fitowa to najasane, sannan kuma idan Mace tanada alwala sai taga wannan ruwan yāfito mata to alwalarta tā warware danhaka dole sai tasake wata

Allah ta'ala yasa mudace

AMSAWA: Mυѕтαρнα Uѕмαи

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments