𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Shin ko ya halatta ga mace yayinda mai nemanta da aure yazo
wajenta ta je wajensa ba tare da tasa hijab ba?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Asali dai shari'a ta umarci Maza da Mata su rintse idanunsu
ga barin yiwa junansu kallo irin na sha'awa kamar yadda Allah(ﷻ) ya fada
قُل لِّلْمُؤْمِنِينَ
يَغُضُّوا مِنْ أَبْصَارِهِمْ وَيَحْفَظُوا فُرُوجَهُمْ ذَلِكَ أَزْكَى لَهُمْ....
MA'ANA
(Ya Muhammad(ﷺ)
ka gayawa Muminai (Maza) su rintse idanunsu kuma su kiyaye farjinsu, hakan shi
ne yafi tsarkaka a garesu.... (Suratul Nūr aya 30).
To amma shari'a ta yi izini ga mai neman aure ya kalli matar
da ya ke so ya aura, to sai dai kuma Malamai sunyi saɓani dangane da cewa ina ne iyakar gwargwadon
inda ya kamata maneminta ya kalla a jikinta? Wasu daga cikin Malamai sai suka
tsananta da yawa sukace bai halatta a ga komai a jikintaba, wasu Malaman kuma
sai suka sassauta da yawa, sukace ya halatta a ga komai a jikinta amma banda
tsiraicinta kaɗai,
daga cikin hujjarsu akwai wannan Hadisi na Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallama) da ya ke cewa
إذاخطب
أحدكم المرأة فإن استطاع أن ينظر إلي ما يدعوه إلي نكاحها فليفعل،
Ma'ana
Idan dayanku yana neman mace da aure, to idan ya samu ikon
ya kalli abinda zai ja hankalinsa ya aureta to ya aikata (ya kalla)
Sannan kuma akwai Malaman da suka tsaya a tsakiya, wato ba
su tsananta da yawa ba kuma ba su sassauta da yawa ba, wanda ko shakka babu
mafi yawa daga cikin Malamai sun tafi ne a kan wannan ra'ayi na tsaka-tsakiya,
daga cikin hujjarsu akwai wannan aya da Allah(ﷻ)
ya ke cewa
وَلَا
يُبْدِينَ زِينَتَهُنَّ إِلَّا مَا ظَهَرَ مِنْهَا
Ma'ana
Ka da Mata su bayyana adonsu sai dai abinda ya ke bayyanan
ne daga ciki. (Fuska da tafin Hannu) (suratul Nūr aya 31)
Danhaka Malaman da ke Mazhabobin Malikiyya, Shafi'iyya, da
kuma Hanafiyya. sukace iyakar fuska da tafukan hannu kaɗai ya halatta manemin aure ya gani, su kuma
Mazhabin Hanabila sukace ya halatta a kalli dukkan gurinda a bisa ga al'ada
yakan bayyan a ganshi a jikinta, wato kamar wuyanta, hannayenta, kafafuwanta,
da kuma gashin kanta. Musamman ma yayinda mace ta ke cikin gida tana yin wasu
'yan aikace-aikace irin na cikin gida.
To amma maganar da tafi inganci kuma tafi dalilai masu Ƙarfi
kamar yadda mafi yawan Malamai suka rinjayar itace, ya halatta mai neman aure
ya kalli fuskarta da tafukan hannayenta da wuyanta, da duga-duganta, da kuma
gashin kanta in buƙatar hakan ta kama, sai dai wasu Malaman sukace idan ya kalla
sau ɗaya shike nan
ya wadatar daga nan bai halatta ba ya sake kallo. amma wasu Malamam sukace ya
halatta ya mai-maita kallonta idan buƙatar hakan ta kama, ko da kuwa ba tare da
tasan yana kallonta ɗin
ba, sai dai bai halatta yayi mata kallo irin na sha'awa ba wanda zai sa shi
yaji daɗi a ransa.
Sannan wannan hukuncin yana tabbatuwa ne a kan Mutumin da yazo neman aure
tsakaninsa da Allah da gaske yakeyi ba wai da wasa ko yaudara ya ke yi ba,
sannan yana da tabbas ko kuma zato mai rinjaye na cewa idan ya nema za a karɓeshi a yarda da da shi.
Sannan da sharaɗin
ya kasance babu wani wanda yake nemanta a baya da har suka riga amince da shi a
kan ya nemeta, saboda Manzon Aʟʟāн(
Sallallahu alaihi Wasallam) ya hana wani ya nemi aure a kan neman wani
шαʟʟαнυ-тα'αʟα α'αʟαмυ
Mυѕтαρнα Uѕмαи
08032531505
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BXjuXb1WxX99NV3OsXPnLV
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.