Ticker

6/recent/ticker-posts

Menene Asalin Izala (Tarihin Izala)

TAMBAYA (99)

Mal usman wai Dan ALLAH da gske yan izala ne suka kawo rabuwar kawanan musulmi a Nigeria???

AMSA

Alhamdulillah

Amsar nan zata fito ne idan aka duba menene asalin ita kanta Izalar

Izala kalmace ta larabci da take nufin "kawar da" kuma cikakken sunanta shine "Izalatil Bidi'ah wa iqamatis Sunnah" ma'ana "Kungiyar kawar da Bidi'ah da tsayar da Sunnah", kenan kamata yayi kowa ya zamo dan Izala tunda ai duk musulmi na kwarai zai so ya kawar da Bidi'ah kuma ya tsayarda Sunnar Annabi Sallallahu alaihi wasallam, kungiya ce da marigayi Isma'ila Idris bin Zakariyya ya kafa ta a shekarar 1978 a jihar Plateau Jos, sakamakon hana shi yada Da'awah da gwamnatin zamaninsa tayi ba tare da qungiya ba, a lokacin da ya ajiye aikin soja

Dalilin da yasa ya kirkiri Jama'atu Izalatul Bidi'ah kenan, ya nemi shawarar Sarkin Musulmi na lokacin amman yace masa yan Bidi'ah fa zasu kashe ka, yace na amince indai har za'a yaqi Bidi'ah. Yace masa to ai bazai yiwu ka kawar da Bidi'ah ba tare da tsayar da Sunnah ba, sai yace ka cike sunan da "Wa iqamatus Sunnah" ma'ana "Da tsayar da Sunnah"

An haifi Malam Ismaila Idris a kauyen Goskorom dake garin Plateau, Jos, a shekarar 1937. Mahaifinsa ya koyar dashi har zuwa lokacin da yakai shekaru 15, daganan ya koma Bauchi inda yayi karatun soro a hannun: Shaikh Magaji, Shaikh Kansurawa, Shaikh Mahmud Bello (Limamin babban masallachin Bauchi), daganan ya koma Kano inda yayi degree a bangaren Islamic Studies. Daganan ya sake komawa Bauchi ya fara aiki a primary school. A 1969 ne, ya koma Kaduna, yayi shekaru 5 a matsayin Murshid (Mai bada shawara a kungiyar Jama'at Nasr al-Islam) inda ya fara da'awah yana sukar sufaye, saboda kausasawa a maganganunsa aka cire shi aka maida shi gidan Yarin Kakurdi dake Kaduna

Daga nan kuma ya shiga soja (Nigerian Army) inda aka nadashi Imam bayan yabar kungiyar Jama'at Nasr al-Islam a shekarar 1974. Lokacin da yana soja ne ya kara samun damar isar da da'awah ka'in da na'in hakan kuma ya zame masa qalubale, har aka yi masa tranfer zuwa Ibadan, inda yayi watanni 3 kacal saboda hatsaniya da ya samu tsakaninsa da Divisional Imam/Lt. Colonel akan bayar da Zakka. Daganan aka kara maidashi Kontagora. A Kontagora mutane suka fara halartar masallachin sojoji na Juma'ah la'akari da limamin sufi ne. Anan ma dai suka kara samun sa'insa silar yanda yake da'awah, aka kara yi masa transfer zuwa tsohon wajensa, Jos. Anan aka bashi Imam, ya ci gaba da yada da'awar sa tare da caccakar sufaye

Salon da'awarsa a ja hankalin al'ummah da yawa, kuma har gayyatar sa ake garuruwa don yada da'awah. Kungiyar Sufaye sun gaji da jin suka, nan da nan suka kai karar Shaikh Ismaila zuwa ga Ministry of Defence. Duk da cewar ya samo goyon bayan Major Alhassan amman an umarce shi da ya daina wannan da'awar da yake yi. Saboda yawan karya wannan dokar da aka saka masa ne aka kore shi daga aikin soja a shekarar 1978. A haka ya ci gaba samun magoya baya musamman daga Tijaniyya wanda silar wannan daukakar ne ya kafa kungiyar Izala

Sannan kuma Shaikh Ismaila Idris ya qalubalanci Sadaqat al-yawm al-thalit (sadakar 3) da Sufaye suke yi idan mutum ya rasu. Da kuma addu'o'in da sufaye suke taruwa suyi kwana 7 da kuma addu'ar 40 da ake yi. Da kuma lazimi da Tijaniyya suke da carbi, wasu suna 100 a kullum wasu kuma har 1,000. Da kuma irinsu ziyarar maqabartun shaihunnansu da sufaye domin neman tabarraki, da khalwa (wanda suke cewa suna kebewa ne da Allah) duk Shaikh Ismaila ya qalubalanci wannan ayyukan na bidi'ah

Haka kuma Izala ta tabbatar da cewar Allah Azzawajallah ne kadai yasan ilimin gaibu, kuma Annabi Sallallahu alaihi wasallam ne kadai yake iya bayyana mu'ujiza, kuma duk musulmai daya ne (sai wanda yafi wani tsoron Allah), kuma sufanci shirka ne, kuma ba'a ganin Allah a mafarki ko a zahiri (Saidai a Aljannah). Aqidar Izala shine duk wani sabon abin da aka sako a addini to wannan bidi'ah ne, amman kofar ilimi da ijtihadi a bude suke amman da hujja qwaqqwara

Izala ba da iya littafin "Kitab al-tawhid" wallafar Shaikh Muhammad b. Abd al-Wahab (1703 - 1792) take amfani ba, saidai kungiyar tana amfani da littattafan magabata irinsu: Ibn Taimiyya, Ibn al-Qayyim, Ibn Khathir, Ibn Abi Zayd al-Qayrawani da wasu manyan malaman Ahlus Sunnah. Izala na bin mazhabin Malikiyya ne

Idan kuma muka koma tarihi zamu tarar da cewar;

Daya daga cikin muhawarar da aka tafka a 10 ga watan April na shekarar 1978, shine akan maganar Federal Shari'ah Court of Appeal (FSCA) wato Kotun Shari'ar Musulunci ta Tarayya. A lokacin da shugaban committe na majalissar zartarwa ya kawo muhawarar (debate) akan shari'ah har aka buqaci za'a goge Section 180 (1) C - da suka saka masa "Shari'ah Paragraph daga Tsarin Constitution" (wanda kamata yayi shari'ar musulunci ace tana sama da constitution), wakilan musulmai suka harzuqa suka fita daga majalisar

Tsohon shugaban kasa (Head of State), Olusegun Obasanjo, ya buqaci duk wadanda suka tafi dinnan su dawo a ci gaba da muhawarar. Bayan sati biyu, majalisa ta ci gaba da zartar da wancan qudurin a 24 ga watan August, 1978. An qaddamar da sabon constitution zuwa ga shugaban kasa ba tare da sashin shari'ah ba (FSCA) wanda daga baya aka shigar dashi a 1 ga October, 1979

A karkashin sashi na: 240 (1), doka tace: "Kowacce jiha dake karkashin gwamnatin tarayya akan ta zartar da Shari'ah Court of Appeal

A wannan lokacin da Izala ta kafu ne al'ummar musulmai suka kula da ci gaban daukakar Shaikh Abubakar Mahmud Gumi (1922 - 2992), wanda manufarsa shine dirkake tare da shafe aqidar sufanci. Ba wai a iya rubuce-rubucen sa na Hausa ya qalubalanci sufaye ba, har ma da Tafsiransa da yake gabatarwa a gidan Radio na Kaduna, tsakanin 1970 zuwa 1974

Wallafar littafin sa mai suna "al-aqida as-sahiha bi muwafaqat ash-shari'a (Imani a mahangar shari'ah) ya janyo yaqi akan yan Bidi'ah, a shekarar 1972. Da kuma yan Tijaniyya da Qadiriyya. Shaikh Nasiru Kabara (1925 - 1996), shugaban Qadiriyya a Nigeria, wanda daga baya ya zama shugaban kungiyar na Africa, a wannan shekarar ne shima yayi raddi ta hanyar wallafa littafinsa "kitab al-nasiha al-sahiha fi'l-radd 'ala al-aqida al-sahiha" (Shawarar gaskiya akan sahihiyar aqida)

Haka shima batijjane Sani Kafinga ya wallafa nashi: "al-Minah al-hamida fil-radd ala-fasid al-aqida" (Kyaututtukan yabo zuwa ga wanda yake da naqasu a imaninsa)

Shaikh Gumi, bai rubuta wancan littafin don kowa ya karanta ba saboda a ganinsa fassara shi zuwa harshen hausa zai zama wani baqon abu a wancan lokacin. A lokacin da dalibinsa, Mallam Isma'ila Idris (1937 - 2000), wanda malamin makaranta ne a da can, mai karantarwa a masallachin Sultan Bello dake Kaduna, ya dinga debo hujjoji daga cikin littafin Shaikh Gumi ya fara sukar sufaye, silar haka aka fara muhawara mai zafi a yankunan da ake musulunci a kasa baki daya

Banbancin dake tsakanin Shaikh Gumi da dalibinsa Malam Ismaila Idris shine, shi Shaikh Gumi ba ya kama sunan kungiya kai tsaye saidai yayi jirwaye mai kamar wanka, yayin da shi kuma Ismaila Idris kai tsaye yake cewa: Abu kaza haramun ne, wannan yayi karo da sunnah, wane kafiri ne

(Duba Ostien, 2006 page 240)

Domin wasu karin bayanan game da rayuwar Shaikh Gumi, duba: Loimeier, Roman, Islamic Reform da kuma Political Change in Northern Nigeria, Evanston-Illinois: Northwestern University Press, 1997, pages na 148–171; da kuma tarihinsa, Sheikh Abubakar Gumi tare da Ismaila. Tsiga, Where I stand, Ibadan: Spectrum Books Limited, 1992. Da kuma Loimeier, 1997, page na 163

An tursasa Malam Ismaila Idris ya daina koyarwa, a lokacin Shaikh Gumi yana Saudiyya, har ya dawo Kaduna ana ci gaba da wannan taqaddama, Malam Ismaila yayi retire amman ya ci gaba da yada da'awar: "al-aqida al-sahiha"

A takaice Izala ta kawo hadin kai ga musulmi saboda an fahimci Sunnar Annabi Sallallahu alaihi wasallam sakamakon kafata kuma kungiyar ita ce irinta ta farko a tarihin yada addinin musulunci a Najeriya, hadi da harkar ilmantarwa

A yanzu haka, Dr. Abdallah Bala lau shine shugaban ta na kasa baki daya

A karshe ina son mu tuna cewar, su fa Mala'iku zasu tambayi mutum menene addininsa bawai minhaj dinsa ba

Muna roqon Allah ya rabamu da bidi'ah ya tabbatar damu akan bin sunnar Annabi Sallallahu alaihi wasallam bisa fahimtar magabatan farko (Salaf)

Wallahu ta'ala a'alam

Amsawa

Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments