𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Allah gafarta menene hukuncin Wanda sha'awa
tama yawa kuma bayason kallon batsa amma zuciyarsa ta kasa masa sai da ya kalla
yake samun sukuni bayan kuma daga baya yazo yai nadama. Sannan wace addu'a
yakama ta ya ringa karantawa.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Na farko dai wannan alama ce dake nuna Qarancin tsoron Allah
azuciyar masu yin haka. Sannan kuma da alamar cewa Zuciyarta tafi Qarfinta.
Allah Maɗaukakin
Sarki ya gaya ma Annabinsa Dawud (alaihis salam) cewa: "... Kuma kada kabi
son zuciya balle ta ɓatar
dakai kan hanyar ALLAH. Hakika waɗannan
da suke ɓatarwa daga
kan hanyar ALLAH, garesu akwai azaba mai tsanani saboda abinda suka manta na
ranar hisabi".
Kuma acikin suratu Yusuf (alaihis salam) Allah ya ce:
"hakika ita zuciya lallai mai yin umurni ce ga mummunan abu".
Allah shi ne ya halicci Ɗan Adam kuma ya sanya sha'awa ajikinmu
domin ya jarrabemu ya bayyanar da bayinsa masu tsoronsa da kuma waɗanda suka karkace daga
kan hanyarsa. Kuma ya kafa mana dokokin da zamu bi domin mu rabauta anan duniya
da kuma ranar Qiyamah. Don haka Allah yace ma Annabinsa (sallal Laahu alaihi wa
aalihi wa sallam)
وَقُلْ
لِلْمُؤْمِنَاتِ يَغْضُضْنَ مِنْ أَبْصَارِهِنَّ وَيَحْفَظْنَ فُرُوجَهُنَّ
...
"ka gaya ma muminai mata su runtse daga idanuwansu kuma
su kiyaye farjojinsu". (Suratul Nūr aya 32)
Wannan umurni ne daga Allah (SWT) zuwa ga Matayen Muminai,
bayan kuma ya gargadi Mazaje Muminai. Kuma Sayyiduna Abdullahi bn Mas'ud (rta)
Yace Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya ce: "HAKIKA
SHI KALLO, WANI KIBIYA NE MAI DAFI DAGA CIKIN KIBIYOYIN IBLIS. DUK WANDA YA
BARI DON TSORONA, ZAN CHANZA MASA DA WANI HASKE (WATO HASKEN IMANI) WANDA ZAI
JI DANDANONSA ACIKIN ZUCIYARSA".
(Mu'ujamul Kabeer na Tabaraniy juzu'i na 10 hadisi na
10,362).
Kallon batsa bai halatta ba. Kuma cewa wai sha'awa ce ta yi miki
yawa ba zai zama uzuri karɓaɓɓe agun Allah ba. Don
haka kiji tsoron Allah ki rika tuna ranar gamuwarki dashi. Ki kiyaye dukkan
gabobin jikinki daga saɓa
masa.
Allah Maɗaukakin
Sarki yana bada labarin ranar Alkiyamah. Ya ce: "AWANNAN RANAR DA ZAMU
YUMQE (SANYA RUFI) BISA BAKUNANSU, KUMA HANNAYENSU NE ZASU ZANYAR DAMU, KUMA
QAFAFUWANSU SUNA SHAIDARWA BISA ABINDA SUKA KASANCE SUNA TATTATAWA (NA
LAIFUKA)".
Kiji tsoron ranar tonon asirai, ranar da Allah zai nunoki
(kamar a vedio) gaki nan sanda kike aikata ayyukan sharrin da kika aikata.
Idan za ki tuba kiyi cikakkiyar tuba irin wacce Allah yake
so. Ba wai tubar Mayaudara ba.
Addu'ar neman shiriya kuwa babu kamar fatiha. Ki rika
karantawa tare da halarto girman Ubangiji. Allah mai gafara ne mai rahama. Shi
keda ikon shiriya da kuma yin gafara ga bayinsa.
Allah ya gafarta mana baki ɗaya,
Aameen.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.