Ticker

6/recent/ticker-posts

Yau Ka Gina Gidan Bene A Cikin Aljannah

Tambaya (72)

Duk sanda na karanta Qulhuwallahu ahad sau 10 a jere, Allah SWT zai gina min gida a cikin Aljannah ko zan iya karanta sama da sau 10 don samun gidajen da yawa

AMSA

Alhamdulillah

Shahararren Tabi'in nan Sa'id ibnul Musayyab (Rahimahullah) ya karbo hadisi mursal cewar Annabi SAW yace: "Duk wanda ya karanta Qulhuwallahu ahad sau 10 a jere, Allah SWT zai gina masa katafaren gidan bene a cikin Aljannah. Idan ka karanta 20, gidaje 2, ka karanta 30 gidaje 3

Sayyadina Umar RA yace: "Na rantse da Allah! Indai hakane to zamu samu gidajen bene da yawa tunda zamu yawaita karantawa

Sai Annabi SAW yace: "Fallahu akhsar" ma'ana: "Allah shi ne mai yawaitawa"

Abin nufi shi ne Allah SWT bazai gaji da gina muku gidajen ba matuqar zaku yawaita karantawa

(Sunan Darimi hadisi mai lambata 3429)

Hafizh Ibn Khathir (Rahimahullah) yace: wannan hadisi ne mursalin jayyid (mai kyau)

(Duba Suratul Ikhas a cikin Tafsir na Ibn Khathir)

(Muhammad Abusoomar ya taba amsa makamanciyar wannan tambayar)

Haka kuma an karbo hadisi daga Abu Hurairah RA yace: Annabi SAW yaji wani mutum yana karanta Qulhuwallahu ahad sai yace: "gaskiyar sa ce"

Sahabbai suka ce: Ya ma'aikin Allah, mene ne gaskiyar ta sa ?

Sai yace (SAW): "Aljannah ce gaskiyar ta sa"

(Musnad Imam Ahmad 7669)

Annabi SAW yace: "Duk wanda ya karanta Qulhuwallahu ahad sau 10 a jere, Allah SWT zai gina masa katafaren gidan bene a cikin Aljannah"

(Sahih al-Jami' al-Saghir, 6472 na Muhammad Nasiriddin albany)

A shawarce, duk wanda ya karanta wannan hadisi to ya dinga aiki dashi - idan kai malami ne to sai ka tara dalibanka ka ce su dinga karantawa sau 10 a jere, idan mahaifiyace to sai itama ta tara yayanta waje guda su karanta a tare kuma a jere, hakama mahaifi. Gidan haya kuke zama a matsayin mata da miji to ku lizamci wannan bonanza don samun babban rabo, kada ayi biyu babu

Kuma duk wanda ya koyawa wani to yana da ladan wani gidan daban ba tare da an tauyewa wanda aka koyawa haqqinsa ba kamar yanda ya tabbata a cikin sahihin hadisi. Allahu Akbar! Wallahi babu wani Attajiri a duniyarnan da ya isa ya baka wani abu kwatankwacin wannan

Aljannnah gaskiya ce. Tananan yanzu haka, an tanade ta ga masu rabo. Mu'ujizozin Qur'ani kadai sun isa sun tabbatar mana samuwar Aljannah

A shekarun baya akwai wani lokacin damuna muna zaune tare da yan uwa a makarantar Nurul Hayat Islamiyya dake anguwanmu, ina cikin karatun Qur'ani ina karanta daidai ayata 26 cikin Suratu Yunus inda Allah SWT yake cewa;

( لِّلَّذِينَ أَحْسَنُوا الْحُسْنَىٰ وَزِيَادَةٌ ۖ وَلَا يَرْهَقُ وُجُوهَهُمْ قَتَرٌ وَلَا ذِلَّةٌ ۚ أُولَٰئِكَ أَصْحَابُ الْجَنَّةِ ۖ هُمْ فِيهَا خَالِدُونَ )

يونس (26) Yunus

Waɗanda suka kyautata yi, suna da abu mai kyawo kuma da ƙari, wata ƙura ba ta rufe fuskokinsu, kuma haka wani ƙasƙanci. waɗancan ne abokan Aljanna, suna madawwama a cikinta.

Anan take sai qurar iska ta taso ta lullube fuskokinmu gaba daya, kasa ta shigarwa wasunmu ido, masu furzar da kasar nayi, tuf! tuf! mutane na ta kakkabe fuskokinsu

Nace Allahu Akbar! Sadaqallahul Azim

Anan naga mu'ujizar Qur'ani qarara, na nunawa yan uwa da muke tare daidai wannan ayar, mukaita fata da roqon Allah Azzawajallah ya sakamu cikin Aljannah gidan dawwama inda qura ba ta rufe fuskoki wadda fadin Aljannar musulmi daya tak yakai girman sammai bakwai da kassai bakwai kamar yanda Allah SWT ya fada;

( وَسَارِعُوا إِلَىٰ مَغْفِرَةٍ مِّن رَّبِّكُمْ وَجَنَّةٍ عَرْضُهَا السَّمَاوَاتُ وَالْأَرْضُ أُعِدَّتْ لِلْمُتَّقِينَ )

آل عمران (133) Aal-Imran

Kuma ku yi gaugawa zuwa ga neman gafara daga Ubangijinku da wata Aljanna wadda faɗinta (dai dai da) sammai da ƙasa ne, an yi tattalinta domin masu taƙawa.

Allahu Akbar! A dan karamin sanin da Allah SWT ya bani na bangaren ilimin kimiyyar sararin samaniya (Astronomy) wannan ayar ita ce tafi kowacce dauremin kai la'akari da ana auna girman sama ne da gudun haske wanda a kowanne second daya haske yana gudun kilometers 300,000 ne kuma akwai inda kafin haske ya je sai ya share sama da shekaru trillions, quadrillions, octillions ko zillions ko ma sama da haka kuma duk magana ake ta lebatun sama ta farko ballantana ta biyu har zuwa ta bakwai. To indai har fadin gidan mutum daya a Aljannah zai yi daidai da sammai bakwai da kassai bakwai to ina kuma ga tsayin gidan, tunda a al'adance tsayi yafi fadi

Wallahu ta'ala a'alam

Ya Allah ka sakamu a cikin Aljannatil Firdous don rahamarka ba don halayenmu ba

Subhanakallahumma wabi hamdika ash-hadu anla'ilaha illa anta, astaghfiruka wa'atubi ilayk

Amsawa;

Usman Danliti Mato (Usmannoor_As-salafy)

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/FBuwMyVjc2sGOEGLm0W7ed

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments