𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Menene Hukuncin Wasa Da Azzakari Harya Kai Ga Fitar Da
Maniyyi?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد
لله
Wannan al'ada ita ce malamai suke kira istimna'i wato mutum
yaiwasa da gabansa har maniyyi yafita mace ko namiji.
Wanda haramunne a alqur'ani da hadisi
Ibnu kaseer rahimahullah yace : Imamu shafi'i da wadanda
suka goyi bayansa yakafa hujja da haramcin wasa da gaba da faɗin Allah madaukakin sarki
وَالَّذِينَ
هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَافِظُونَ ٥ إِلَّا عَلَىٰ أَزْوَاجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُهُمْ
فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ ٦ فَمَنِ ابْتَغَىٰ وَرَاءَ ذَٰلِكَ فَأُولَٰئِكَ هُمُ
الْعَادُونَ ٧
Bayin Allah nagari Sune waɗanda
dangane da farjinsu suke kiyayeshi. Face a kan matan aurensu, ko kuwa abin da
hannayen damansu suka mallaka (kuyanginsu) to lalle su ba waɗanda ake zargi ba ne. Saboda
haka wanda ya nemi abin da ke bayan wancan, to, waɗancan su ne masu ƙetarewar haddi.
(Suratul Muminun 5-7)
Imamu shafi'i acikin littafin Aure yace sai ya kasance Allah
yabayyana kiyaye farjinsu saifa akan matayensu ko abinda damarsu tamallaka, sai
yazama haramun idan ba matarka bace ko kuyangarka sai Allah ya karfafi maganar
dacewa " wanda ya nemi koma bayan hakan yana cikin masu taka dokokin
Allah"
Bai halatta amfani da azzakari ba sai akan matarka ko
baiwarka, bai halatta jin-daɗi
dashi da hannu ba wallahu A'alamu kitabul ummu na imamu shafi'i.
Wasu malaman sun kafa hujja taharamcin istimna'i da faɗin Allah madaukakin sarki
وَلْيَسْتَعْفِفِ
الَّذِينَ لَا يَجِدُونَ نِكَاحًا حَتَّىٰ يُغْنِيَهُمُ اللَّهُ مِن فَضْلِهِ
Wadanda ba su samu damar aure ba sukame har sai Allah ya
wadata su daka falalarsa. (Suratul Nur aya 33)
Sukace: umarni da kamewa yana nuna hakuri da rashin samun
yin auren ko kuyangar.
A sunnah kuwa sunkafa hujja da hadisin Abdullahi dan mas'ud
Yardar Allah takara tabbata a gareshi ya ce: Mun kasance tare da Annabi
sallallahu Alaihi wasallam muna samari bamu samu komai ba sai Annabi sallallahu
Alaihi wasallam yace damu "ya ku taran samari duk wanda yasamu halin
daukar dawainiyar iyali yayi aure, domin yanasa kamewa daka gani, yana kuma
tsare farji, wanda kuma bai samu dama ba to nahore shi dayin azumi domin azumi
yana kariya daka fadawa haram. Bukhari 5066.
Sai shari'a ta shiryar lokacin da mutum ya gajiya wajen yin
aure sai ya dunga azumi tare da wahalarsa, shari'a bata shiryar zuwa wasa da
farji ba, tare da saukinsa akan azumi tare da haka ba'a halatta shiba.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.