Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Wasa Da Azzakari Har Ya Kai Ga Fitar Da Maniyyi

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Menene Hukuncin Wasa Da Azzakari Harya Kai Ga Fitar Da Maniyyi?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

الحمد لله

Wannan al'ada ita ce malamai suke kira istimna'i wato mutum yaiwasa da gabansa har maniyyi yafita mace ko namiji.

Wanda haramunne a alqur'ani da hadisi

Ibnu kaseer rahimahullah yace : Imamu shafi'i da wadanda suka goyi bayansa yakafa hujja da haramcin wasa da gaba da faɗin Allah madaukakin sarki

وَالَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَافِظُونَ ٥۝ إِلَّا عَلَىٰ أَزْوَاجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ ٦۝ فَمَنِ ابْتَغَىٰ وَرَاءَ ذَٰلِكَ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الْعَادُونَ ٧۝

Bayin Allah nagari Sune waɗanda dangane da farjinsu suke kiyayeshi. Face a kan matan aurensu, ko kuwa abin da hannayen damansu suka mallaka (kuyanginsu) to lalle su ba waɗanda ake zargi ba ne. Saboda haka wanda ya nemi abin da ke bayan wancan, to, waɗancan su ne masu ƙetarewar haddi. (Suratul Muminun 5-7)

Imamu shafi'i acikin littafin Aure yace sai ya kasance Allah yabayyana kiyaye farjinsu saifa akan matayensu ko abinda damarsu tamallaka, sai yazama haramun idan ba matarka bace ko kuyangarka sai Allah ya karfafi maganar dacewa " wanda ya nemi koma bayan hakan yana cikin masu taka dokokin Allah"

Bai halatta amfani da azzakari ba sai akan matarka ko baiwarka, bai halatta jin-daɗi dashi da hannu ba wallahu A'alamu kitabul ummu na imamu shafi'i.

Wasu malaman sun kafa hujja taharamcin istimna'i da faɗin Allah madaukakin sarki

وَلْيَسْتَعْفِفِ الَّذِينَ لَا يَجِدُونَ نِكَاحًا حَتَّىٰ يُغْنِيَهُمُ اللَّهُ مِن فَضْلِهِ

Wadanda ba su samu damar aure ba sukame har sai Allah ya wadata su daka falalarsa. (Suratul Nur aya 33)

Sukace: umarni da kamewa yana nuna hakuri da rashin samun yin auren ko kuyangar.

A sunnah kuwa sunkafa hujja da hadisin Abdullahi dan mas'ud Yardar Allah takara tabbata a gareshi ya ce: Mun kasance tare da Annabi sallallahu Alaihi wasallam muna samari bamu samu komai ba sai Annabi sallallahu Alaihi wasallam yace damu "ya ku taran samari duk wanda yasamu halin daukar dawainiyar iyali yayi aure, domin yanasa kamewa daka gani, yana kuma tsare farji, wanda kuma bai samu dama ba to nahore shi dayin azumi domin azumi yana kariya daka fadawa haram. Bukhari 5066.

Sai shari'a ta shiryar lokacin da mutum ya gajiya wajen yin aure sai ya dunga azumi tare da wahalarsa, shari'a bata shiryar zuwa wasa da farji ba, tare da saukinsa akan azumi tare da haka ba'a halatta shiba.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

NA KASA DAINA ISTIMNA’I

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Shin ko wanda yake yin istimna’i, idan ta tuba Allaah zai yafe ma shi? Kuma na yi na yi in daina amma na kasa. Ko akwai wata shawara da malam zai ba ni?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.

Ma’anar Istimna’i shi ne: Namiji ko mace ya riƙa wasa da gabansa har sai ya gamsar da kansu kamar ta hanyar fitar da maniyyi. A wurin malamai wannan aikin haram ne, domin ya saba wa siffan muminai bayin Allaah na-gari wadanda ya yabe su da cewa:

{وَالَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَافِظُونَ . إِلَّا عَلَى أَزْوَاجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ . فَمَنِ ابْتَغَى وَرَاءَ ذَلِكَ فَأُولَئِكَ هُمُ الْعَادُونَ}

Waɗanda kuma su ne masu kiyayewa ga farjojinsu. Sai dai ga matan aurensu ko kuwa abin da damansu suka mallaka, to lallai su a hakan ba abaiban zargi ba ne. Amma duk wanda ya nemi hanyar da ba wannan ba, to waɗannan su ne cikakkun ’yan ta’adda. (Surah Al-Muminuun: 5-7; Surah Al-Ma’aarij: 29-31).

A fili kuwa aikata istimna’i ya shiga cikin ‘wanda ya nemi hanyar da ba wannan ba’.

Wanda ya tuba daga aikata wannan mummunan aikin, ana fata Allaah Ta’aala ya yafe masa, domin abin da ya faɗa cewa:

{قُلْ يَاعِبَادِيَ الَّذِينَ أَسْرَفُوا عَلَى أَنْفُسِهِمْ لَا تَقْنَطُوا مِنْ رَحْمَةِ اللَّهِ إِنَّ اللَّهَ يَغْفِرُ الذُّنُوبَ جَمِيعًا إِنَّهُ هُوَ الْغَفُورُ الرَّحِيمُ} [الزمر: 53]

Ka ce: Ya ku bayina waɗanda suka yi ɓarna ga rayukansu! Kar ku ɗebe tsammani daga Rahamar Allaah. Haƙiƙa! Allaah yana gafarar zunubai gaba-ɗaya. Lallai ne shi, shi ne Mai gafara Mai Rahama. (Surah Az-Zumar: 53).

Amma matakan da mutum zai iya ɗauka domin barin komawa ga aikata irin waɗannan laifuffukan akwai cewa:

1. Ya riƙa tuna cewa, Allaah yana ganin sa a duk inda ya ke, kuma yana iya kama shi da azabtar da shi a kan wannan laifin a duk sadda da ya so.

2. Ya riƙa ɗaukan matakan da za su nisanta shi daga sheɗan, kamar zama a cikin alwala da yawaita zikirin Ubangiji a kowane hali, gwargwadon iko.

3. Ya nisanci kasantuwa shi kaɗai a wuraren da ya san yana samun daman yin wannan aikin, kamar a lokacin kwanciya ya riƙa kwana tare da wani a ɗaki ɗaya.

4. Ya san cewa ban-ɗaki matattarar sheɗanu ne, shiyasa yake yin addu’o’in neman tsari daga sheɗanun maza da mata a lokacin shiga.

5. Wannan kuma ke sanya shi yin gaggawan fita daga wurin, ta yadda ba zai daɗe a cikin sa har ya samu daman yin wannan mummunan aikin ba.

Ina roƙon Allaah ya ƙara kare ka daga sharrin sheɗanu da kuma sharrin zuciya mai yawan umurni da saɓon Ubangiji Ta’aala.

Wal Laahu A’lam.

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments