𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu
Alaikum. A halin da ake ciki yanzu yadda kafirai kamar a Jihar Filato da
Kudancin Jihar Kaduna suke ta yunƙurin karkashe musulmi da tarwatsa su da
raba su da garuruwansu, to idan waɗansu
musulmi suka tsaya suka tunkari waɗannan
kafiran har kuma suka rasa rayukansu a kan haka, za a iya cewa sun yi mutuwar
shahada irin na jihadin musulunci?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus
Salaam Wa Rahmatul Laah.
Sahihin
Jihadin Musulunci yana da sharuɗɗa
da ƙa’idoji da dokokinsa, kamar
yadda malamai masana suka yi bayani musamman a cikin littaffan Fiqhu.
Amma haƙƙi
ne na wajibi a kan musulmi a duk inda su ke su kare addininsu da rayukansu da
iyalansu da dukiyoyinsu da gwargwadon ƙarfi da ikonsu ko iyawarsu.
Idan musulmin
da su ke zaune a wani wurin da aka fi ƙarfinsu suka kasa kare kansu daga masu yi
musu ta’addanci, to
wajibi ne a kan sauran musulmin da su ke kusa dasu su taimaka musu.
Bai halatta ba
musulmi su bari ana zaluntar sashensu, ko kuma a riƙa amfani da su wurin
zaluncin, balle kuma su da kansu su zama masu shiryawa ko zartar da zaluncin.
Ya halatta ga
musulmin da ake ƙuntata musu su yi hijira zuwa inda za su iya yin addininsu ba
da takurawa ba, har zuwa lokacin da za su samu iko da ƙarfin tsayawa da ƙafafuwansu
a garuruwansu.
Duk lokacin da
wani musulmi ya rasa ransa a wurin ƙoƙarin kare addininsa ko rayuwarsa ko
iyalinsa ko dukiyarsa, ko kuma wurin hana a zalunce shi, to yana da hukuncin
wanda ya yi mutuwar shahada.
Bai halatta ba
musulmin da su ke a cikin rauni da rashin ƙarfin tattali su bari a yi amfani da su
wurin tayar da wata fitinar da za ta janyo a yi ta kashe su ko ’yan uwansu ko da kuwa da
suna jihadi ne.
Domin manufa
mafi girma na halittar mutane da aljanu shi ne su tsayu da bautar Allaah shi kaɗai, amma ba wai su yi ta
mutuwa suna barin duniya haka nan ba tare da ilimi da ilmantarwa ba.
Shi Jihadin
Musulunci Allaah Ta’aala ne yake kawo shi a lokacin sa. Abin da yake a kan
musulmi dai kawai shi ne yin tattali da shirin ko-ta-kwana, kar su yi sakaci
har arna su murƙushe su gaba-ɗaya.
Kuma ko da a
lokacin da musulmi su ke da ƙarfin iya tunkarar kafirai, ba a yarda su
yi fata ko burin hakan ba sai ya zama tilas. Domin zaman lafiya da aminci a
rayuwa shi ya fi komai.
Al-Bukhaariy
(2965-2966) da Muslim (4640) sun riwaito hadisin Sahabi Abdullaah Bn Abi-Aufaa
(Radiyal Laahu Anhu) cewa: Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa
Sallam) ya miƙe a cikin Sahabansa da yamma a wani yaƙin da ya fita, ya ce
« أَيُّهَا النَّاسُ ، لاَ تَتَمَنَّوْا
لِقَاءَ الْعَدُوِّ ، وَسَلُوا اللَّهَ
الْعَافِيَةَ ، فَإِذَا لَقِيتُمُوهُمْ
فَاصْبِرُوا ، وَاعْلَمُوا أَنَّ
الْجَنَّةَ تَحْتَ ظِلاَلِ السُّيُوفِ »
Ya ku mutane!
Kar ku yi burin haɗuwa
da maƙiya.
Ku roki Allaah kariya da lafiya. Idan kuma kuka haɗu da su to sai ku jajirce. Kuma ku san cewa:
Aljannah dai a ƙarƙashi inuwar takubba su ke.
Daga nan sai
kuma ya ce
« اللَّهُمَّ مُنْزِلَ الْكِتَابِ ، وَمُجْرِىَ السَّحَابِ
، وَهَازِمَ الأَحْزَابِ ، اهْزِمْهُمْ وَانْصُرْنَا
عَلَيْهِمْ »
Ya Allaah! Ya
Masaukin Littafi, kuma Mai gudanar da giragizai, kuma Mai ruguje rundunoni! Ka
rushe su, kuma ka ba mu nasara a kansu.
Hanyoyin samun
shahada suna da yawa a cikin sahihin musulunci, kamar yadda hadisai sahihai
daga Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) suka nuna
1. Mutuwa a
wurin yaƙi
da kafirai a jihadin ɗaukaka
Kalmar Allaah.
2. Mutuwa a
kan hanyar tafiya jihadin ɗaukaka
hanyar Allaah.
3. Mutuwa a
cikin annoba.
4. Mutuwa da
matsalar ciwon ciki.
5. Mutuwa ta
hanyar nutsewa a cikin ruwa.
6. Mutuwa a
cikin girgizar ƙasa ko rushewar gini.
7. Mutuwar
mace mai naƙuda ko mai ciki.
8. Mutuwa a
cikin gobara.
9. Mutuwa ta
dalilin tarin huka.
10. Mutuwa ta
dalilin cutar bulala.
11. Mutuwa
wurin kare addini ko rai ko iyali ko dukiya.
(Dubi dalilan
waɗannan a cikin:
Ahkaamul Janaa’iz, shafi: 35-41)
Manzon Allaah
(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce
« مَنْ قُتِلَ دُونَ مَالِهِ فَهُوَ شَهِيدٌ ، وَمَنْ قُتِلَ
دُونَ أَهْلِهِ ، أَوْ دُونَ
دَمِهِ ، أَوْ دُونَ
دِينِهِ فَهُوَ شَهِيدٌ »
Duk wanda aka
kashe shi yana kare dukiyarsa to shi shahidi ne. Kuma duk wanda aka kashe shi
yana kare iyalinsa, ko yana kare jininsa, ko yana kare addininsa, to shi
shahidi ne. (Abu-Daawud: 4774, kuma Al-Albaaniy a cikin Ahkaamul Janaa’iz,
shafi: 42 ya ce: Sanadinsa Sahihi ne).
Haka kuma ya
ce
« كُلُّ مَيِّتٍ يُخْتَمُ عَلَى عَمَلِهِ ، إِلاَّ الَّذِى
مَاتَ مُرَابِطًا فِى سَبِيلِ اللَّهِ ، فَإِنَّهُ يُنْمَى
لَهُ عَمَلُهُ إِلَى يَوْمِ الْقِيَامَةِ ، وَيَأْمَنُ مِنْ
فِتْنَةِ الْقَبْرِ »
Kowane mamaci
ana rufewa a kan aikinsa, sai dai wanda ya mutu a kan ribaɗi a cikin hanyar Allaah.
Shi kam ana yi masa renon aikinsa har zuwa Ranar Ƙiyama, kuma ana amintar da shi daga
fitinar ƙabari.
(As-Saheehah: 549, Sahih Abi-Daawud: 1258)
Kuma ko da
musulmi bai samu mutuwar shahada a filin jihadin ɗaukaka
Kalmar Allaah ba, wannan ba ya hana shi samun matsayin masu shahadar
Al-Imaam
Muslim (5039) da wasu As-Haabus Sunnan sun riwaito maganar Annabi (Sallal Laahu
Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) cewa
« مَنْ
سَأَلَ اللَّهَ الشَّهَادَةَ بِصِدْقٍ ، بَلَّغَهُ اللَّهُ
مَنَازِلَ الشُّهَدَاءِ ، وَإِنْ مَاتَ
عَلَى فِرَاشِهِ »
Duk wanda ya
roƙi
Allaah mutuwar shahada da gaskiya, Allaah zai kai shi masaukin masu mutuwar
shahada, ko da kuwa a kan gadonsa ya rasu.
Kar wani ya ɗauki waɗannan bayanan kamar kashe
gwiwa ko karya zuciya, amma dai ƙarin faɗakarwa
ko zaburarwa ne ga fahimtar haƙiƙanin yadda al’amura su ke, tare da samu kyakkyawar hanyar zartar da
su bisa dacewa da shari’a.
Sannan kuma tare da sanin cewa shi musulmi mabiyin shari’a ba ya yin asara a cikin komai a duk inda ya ke, in shà Allâh.
Allaah ya yi mana
maganin dukkan fitintinu, da dukkan masu tayar da su. Kuma ya zaunar da mu a
cikin ƙasashenmu
lafiya.
WALLAHU A'ALAM
Sheikh
Muhammad Abdullaah Assalafiy
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.