𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum mallam, ina da
tambaya akan ko ya halatta mata su ziyarci makabarta, don suyi addu’a ga
magabatansu ??
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikum assalam. Ya halatta
mata su ziyarci Makabarta, amma kar su yawaita, saboda Annabi Sallallahu alaihi
Wasallam ya la’anci mata masu yawan ziyarar Makabarta, kamar yadda Tirmizi ya
rawaito kuma ya inganta shi !!
Annabi Sallallahu alaihi Wasallam
ya wuce wata mace tana kuka a jikin Kabari, sai ya ce mata “Ki ji tsoran Allah,
ki yi hakuri” kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta: (1283), a
cikin hadisin Manzon Allah bai hana ta ziyarar Kabari ba, kawai ya yi mata
WA’AZI ne akan ruri da koke-koken da take yi, sannan Nana A’isha ta tambayi
Annabi Sallallahu alaihi Wasallam game da addu’ar da za ta yi in ta je
Makabarta sai ya koya mata, kamar yadda ya zo a Sahihi Muslim a hadisi mai
lamba ta (974), hakan sai ya nuna mustahabbancin zuwan mata Makabarta ba tare
da yawaitawa ba.
Addu’ar ita ce kamar haka
اَلسَّلامُ عَلَيْكُمْ
أَهْلَ الدِّيَارِ مِنَ المؤْمِنِينَ وَالْمُسْلِمِينَ، وَإِنّا إِنْ شَاءَ اللهُ بِكُمْ لاَحِقُونَ، وَيَرْحَمُ اللهُ الْمُسْتَقْدِمِينَ مِنَّا وَالْمُسْتَأْخِرِينَ أَسْأَلُ اللهَ لَنَا وَلَكُمْ الْعَافِيَةَ.
Aminci ya tabbata a gare ku, ya
ku ma'abota waɗannan
gidaje daga muminai da musulmi, kuma mu in Allah ya so masu riskuwa ne da ku.
Kuma Allah ya ji kan waɗanda
suka gabata daga cikinmu da waɗanda
suka yi saura. Ina rokon Allah aminci daga bala'i gare mu da gare ku.
Hadisin da aka rawaito cewa
Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ya la’anci mata masu ziyartar Makabarta
bai inganta ba, saboda a cikin sanadinsa akwai Salih Baazaam, shi kuma yana da
rauni a wajan malaman Hadisi, kamar yadda Ibnu Abdulbarr ya ambata a Tamheed
3/234.
Don haka ya halatta mata su
ziyarci Makabarta, saidai su kiyayi yawaitawa, saboda hadisin Farko da na
ambata, da kuma ruri da koke-koke, saboda hadisin Bukhari da ya gabata
Don neman karin bayani duba:
Almuhallaa 3/388 da kuma Almajmu’u 5/310.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BXjuXb1WxX99NV3OsXPnLV
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.