𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salamu
Alaikum. Malam, matar da mijinta ya sake ta kuma ta dawo gidan iyayenta, wai haƙƙin
ciyar da ita a kan wanene ya ke? Domin wasu iyaye sai ka ji suna cewa, yanzu
ciyar da ita ba shi ne a gabansu ba! Suna ganin ƙannenta sun fi ta daraja a wurinsu. Wai
ita bazawara ba ta da daraja ne?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah.
To, da farko
dai ma’anar ciyarwa shi ne abin da malaman Fiqhu suke kira: An-Nafaqah , watau
abin da mutum yake bayarwa domin amfanin kansa ko waninsa, na abinci ko abin
sha ko tufafi ko sauran abubuwan buƙata, kamar wurin zama da magunguna a
lokacin rashin lafiya.
Ciyarwa
wajibin abu ne da Allaah ya ɗora
ta a kan muminai a cikin ayoyi da hadisai ingantattu.
يٰۤـاَيُّهَا الَّذِيْنَ اٰمَنُوْۤا اَنْفِقُوْا مِمَّا رَزَقْنٰكُمْ مِّنْ قَبْلِ اَنْ يَّأْتِىَ يَوْمٌ لَّا بَيْعٌ فِيْهِ وَلَا خُلَّةٌ وَّلَا شَفَاعَةٌۗوَالْكٰفِرُوْنَ هُمُ الظّٰلِمُوْنَ
Ya ku waɗanda suka yi Imani! Ku
ciyar daga abin da Allaah ya azurta ku da shi, tun kafin wani yini ya zo muku,
wanda babu ciniki a cikinsa, babu abota kuma babu ceto. Kuma kafirai sune
azzalumai. (Surah Al-Baqarah: 254)
Shari’ar
musulunci ta ɗora wa
musulmi nauyin ciyar da matan aurensu da ’ya’yansu da iyayensu da danginsu mabuƙata
da barorinsu masu yi musu hidima, da kuma dabbobin da suke ƙarƙashin
ikonsu da kulawarsu. (Al-Wajeez, shafi: 394-400)
Haƙƙin
ciyar da mace a bayan aure yana kan mijinta ne. Allaah Ta’aala ya ce
لِيُنْفِقْ ذُوْ سَعَةٍ مِّنْ سَعَتِهٖۗ وَمَنْ قُدِرَ عَلَيْهِ رِزْقُهٗ فَلْيُنْفِقْ مِمَّاۤ اٰتٰٮهُ اللّٰهُۗ لَا يُكَلِّفُ اللّٰهُ نَفْسًا اِلَّا مَاۤ اٰتٰٮهَاۗسَيَجْعَلُ اللّٰهُ بَعْدَ عُسْرٍ يُّسْرًا
Sai mawadãci
ya ciyar daga wadãtarsa kuma wanda aka ƙuntata masa arzikinsa, to, sai ya ciyar
daga abin da Allah Ya bã
shi. Allah bã Ya
kallafa wa wani rai fãce
abin da Ya bã shi.
Allah zai sanya sauƙi a bãyan
tsanani. (Surah At-Talaaq: 7)
Kuma da aka
tambayi Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) a kan haƙƙin
matar ɗayanmu a
kansa, sai ya ce: ‘Shi ne ka ci da ita idan ka ci, kuma tufatas da ita idan ka
tufatu, kuma kar ka bugi fuska, kuma kar ka munana, kuma kar ka ƙaurace
sai dai a cikin ɗaki.’
(Abu-Daawud; Ibn Maajah)
Wannan haƙƙin
yana nan a kan mijin har a bayan ya saki matar har zuwa lokacin gama iddarta,
matuƙar
dai sakin raja’i ne
wanda akwai kome a cikinsa. Allaah Ta’aala
ya ce
وَالْوَالِدٰتُ يُرْضِعْنَ اَوْلَادَهُنَّ حَوْلَيْنِ كَامِلَيْنِ لِمَنْ اَرَادَ اَنْ يُّتِمَّ الرَّضَاعَةَۗوَعَلَى الْمَوْلُوْدِ لَهٗ رِزْقُهُنَّ وَكِسْوَتُهُنَّ بِالْمَعْرُوْفِۗ لَا تُكَلَّفُ نَفْسٌ اِلَّا وُسْعَهَاۚلَا تُضَاۤرَّ وَالِدَةٌ بِۢوَلَدِهَا وَلَا مَوْلُوْدٌ لَّهٗ بِوَلَدِهٖ وَعَلَى الْوَارِثِ مِثْلُ ذٰلِكَۚ فَاِنْ اَرَادَا فِصَالًا عَنْ تَرَاضٍ مِّنْهُمَا وَتَشَاوُرٍ فَلَا جُنَاحَ عَلَيْهِمَاۗوَاِنْ اَرَدْتُّمْ اَنْ تَسْتَرْضِعُوْۤا اَوْلَادَكُمْ فَلَا جُنَاحَ عَلَيْكُمْ اِذَا سَلَّمْتُمْ مَّاۤ اٰتَيْتُمْ بِالْمَعْرُوْفِۗ وَاتَّقُوا اللّٰهَ وَاعْلَمُوْۤا اَنَّ اللّٰهَ بِمَا تَعْمَلُوْنَ بَصِيْرٌ
Kuma mãsu
haifuwa (sakakku) suna shãyar da abin haifuwarsu shẽkara biyu cikakku ga
wanda ya yi nufin ya cika shãyarwa. Kuma ciyar da su da tufãtar da su yana a
kan wanda aka haifar masa da alhẽri. Bã a kallafa wa rai fãce iyãwarsa. Bã
a cũtar da uwa game da ɗanta,
kuma bã a cũtar da uba game da ɗansa,
kuma a kan magãji akwai misãlin wancan. To, idan suka yi nufin yãye, a kan
yardatayya daga gare su, da shãwartar jũna, to bãbu laifi a kansu. Kuma idan,
kun yi nufin ku bãyar da ɗiyanku
shãyarwa, to, bãbu laifi a kanku idan kun mĩƙa abin da kukazo da shi bisa al'ãda. Kuma ku bi Allah da taƙawa.
Kuma ku sani cẽwa lalle ne Allah, ga abin da kuke aikatawa, Mai gani ne.
(Surah: Al-Baqara, Ayat: 233)
Amma idan
sakin baa’in ne wanda babu kome a cikinsa, kamar wanda ya auku a matsayin na
cikon uku ko ta hanyar khul’i ko Li’aani , to a nan babu sauran ciyarwa a kan
mijin. Haka Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya faɗa wa Faatimah Bint Qais
(Radiyal Laahu Anhaa) a lokacin da mijinta ya sake ta na ƙarshen
uku: ‘Ba ki da wani
abu na ciyarwa ko mazauni a kansa.’
(Muslim)
Sai dai ko in
ya sake ta alhali tana da ciki ne. A nan wajibi ne ya cigaba da ciyar da ita
har sai ta haihu. Allaah Ta’aala ya ce:
اَسْكِنُوْهُنَّ مِنْ حَيْثُ سَكَنْـتُمْ مِّنْ وُّجْدِكُمْ وَلَا تُضَاۤرُّوْهُنَّ لِتُضَيِّقُوْا عَلَيْهِنَّۗ وَاِنْ كُنَّ اُولَاتِ حَمْلٍ فَاَنْفِقُوا عَلَيْهِنَّ حَتّٰى يَضَعْنَ حَمْلَهُنَّۚ فَاِنْ اَرْضَعْنَ لَـكُمْ فَاٰ تُوْهُنَّ اُجُوْرَهُنَّۚ وَأْتَمِرُوْا بَيْنَكُمْ بِمَعْرُوْفٍۚ وَاِنْ تَعَاسَرْتُمْ فَسَتُرْضِعُ لَهٗۤ اُخْرٰىۗ
Ku zaunar da
su daga inda kuka zaunar daga gwargwadon sãmunku. Kuma kada ku cũce su dõmin ku
ƙuntata
a kansu. Kuma idan sun kasance ma'abũta
ciki, sai ku ciyar da su har su haifi cikinsu. Sa'an nan idan sun shãyar da mãma sabõda ku, sai ku bã su tsãdõdinsu. Kuma ku yi shãwara a tsakãninku
bisa abin da aka sani. Kuma idan kun nũna
talauci to wata mace zã
ta shãyar da mãma sabõda shi (mijin). (Surah:
At-Talaaq, Ayat: 6)
Idan kuma ba
ta yarda ba shikenan, sai ya nemi wata ta shayar masa.
Matar da aka
ce babu haƙƙin
ciyarwa ko mazauni a kan mijinta a bayan saki, ko wacce ta gama idda, ko ta
haife cikinta, ya zama dole ta rabu da gidan mijin domin babu wata alaƙa da
ta rage a tsakaninsu. Sai ta koma gidan iyayenta ko danginta.
Daga wannan
lokacin, haƙƙin ciyarwa, tufataswa da mazauni ya tashi daga kan mijinta ya
dawo kan iyayenta ko danginta. Nassoshi da yawa sun kwaɗaitar da iyaye ga ciyarwa a kan ’ya’yansu,
kamar yadda Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce: ‘Mafificin
dinaren da mutum ya kashe shi ne dinaren da ya kashe shi a kan iyalinsa.’
(Muslim).
Haka kuma ya
tsawatar a kan yin rowa da ƙin ɗaukar
nauyin iyali: ‘Ya ishi zunubi ga mutum ya tozarta wanda yake ciyarwa.’
(Abu-Daawud)
A kan haka ne
ma wasu nassoshin suka halatta wa mace ta ɗebi
daidai gwargwadon abin da ya ke haƙƙinta da ’ya’yanta
daga cikin dukiyar mijinta da ya zama ƙanƙamo, ko da kuwa ba da saninsa ba ne.
(Al-Bukhaariy da Muslim)
Sai dai kar a
manta fa: Duk maganar da ake yi a kan ciyar da ’ya’ya maza da mata da sauran
dangi, yana zama wajibi ne kawai a lokacin da ’ya’yan suka zama talakawa kuma
marasa ƙarfi,
waɗanda ba za su iya
nema da kansu ba. Amma shari’a ba ta ɗora
wa wani mutum ciyar da ’ya’ya ko danginsa ƙarfafa da suka ƙi neman na-kansu, suka
shantake suka zama cima-zaune ba! Musamman a lokacin da ake cikin halin ƙaƙa-ni-ka-ki
irin wannan. (Tamaam Minnah)
Don haka,
shawarar da ya dace a bai wa irin waɗannan
zawarawan a nan ita ce:
1. Ku yi haƙurin
zama a cikin gidajen mazajen aurenku, irin yadda uwayenku suka yi kuma suke yi
a gidajen mazajensu, watau ubanninku da suka haife ku.
2. Kar ku riƙa
neman fita ko rabuwa da su. Domin mijin aure da gidan aure daraja ce, kuma
rufin asiri ne ga mace.
3. Tun kafin
aure da bayan aure ku yi ƙoƙarin samun sana’a
ta halal da za ku dogara da ita a cikin rayuwa. Kar ku dogara ga abin hannun
wani: Iyaye ko miji ko ɗan’uwa
ko dangi.
4. Ku yi
amfani da sadakin aurenku wurin ƙara jali a cikin sana’o’inku, kar ku yi gaggawan cinye shi a kayan tanɗe-tanɗe da lashe-lashe ko maƙulashe!
5. Kar ku sake
harkokin sana’o’in su shagaltar da ku daga kula da ayyukanku na asali a cikin
gida, kamar haƙƙokin miji da tarbiyyar ’ya’yanku.
Ina kyautata
zaton cewa rashin hali da ƙuncin rayuwar da iyaye suke ciki ne ke
sanyawa ake gaya muku irin waɗannan
maganganun da ba ku jin daɗin
su. Don haka, ku yi haƙuri kuma ku yi ƙoƙarin neman na-halal ɗin ku, kuma ku taimaka
musu. Da haka, sai ku ga komai ya wuce, in shà Allâh.
Amma kuma su
ma iyaye dole su san cewa: Takurawa ’ya’ya zawarawa da sauran ’ya’ya maza da
mata, da gaya musu baƙaƙen maganganu irin wannan kan iya kangarar da su. Wani lokaci
kuma ya sanya su kauce hanya, su fice daga gida da himmar neman nasu na-kansu
ta mummunar hanyar da ba ta dace ba!! Sai kuma a zo ana tafa hannu, ana
sallallami!
Sai mu kiyaye.
Allaah Ta’aala
ya shirye mu gaba-ɗaya.
WALLAHU A'ALAM
Muhammad
Abdullaahi Assalafiy
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.