Ticker

6/recent/ticker-posts

Na Cancanta (Kashi na 4)

Ina ƙoƙarin ƙarasa ajin su Rumaisa da mu mun gama Exam ta ƙualifying da muka zana chemistry ranar, zan je na faɗa mata saƙon da Mama ta ba ni na kaimata da Rumaisa ta rigani ta howa a yau

Malam Hamid na hango jikin birandar ajinsu Rumaisa da waya kunnensa da alama waya ya fito amsawa daga cikin Library ɗin da ya ka sance gurin zamansa dako kiransa za ayi aji a nan ake samunsa, a yadda na fahimci Malam Hamid bai fiye son hayaniya ba duba da yadda ko yana koyarmana yake yi

Ban san ya hango ni ba shi ma da ina ƙarasowa inda yake tun kafin na gaishesa ya faramin magana da yake ƙoƙarin cire wayar kunnensa

"Sumayyah"

Na amsa da

"Na'am Malam ina yini”

Ya dube ni

"Lafiya lau, ina za ki haka”

Nace

"Gurin ƙanwata”

Malam Hamid mutum ne mai son ɗalibansa musamman indai kana gane subject din da yake koyarwa hakan ya sa muke mutunci sosai dan nidai inason physics sosai maganarsa ta katse min tunanina don ban yi ƙoƙarin tafiya ba har lokacin da ban san dalili ba

"Kin dai hanani number ɗinki, kawayenki duk sun ba ni gashi saura kwanaki ya rage nabar Kano"

Kallonsa na yi don indai ban manta ba a ƙarshen shekararmu Ss1 ya zo makarantarmu kuma gashi yanzu muna Ss2 karshen shekara

"Kina ta kallona ba za ki ba ni ba ko, to kimin kwatancen gidanku na zo"maganarsa ta katse min tunanina na kuma sauke kaina daga kansa

"Ba hanaka na yi ba Malam ba nida waya ne, batun gidanmu kuma. . "

Ban ƙarasa zancen ba ya yi magana

"Ba a bari irina ya zo ko?"

Murmushi na yi Jin kalamansa ta don ta ina talaka kamarni za a ce saika zaɓi wanda zaizo gidanku ba tare da kana da dalili Mai karfi ba, duk da bawai na san rayuwar Malam Hamid ba amma inada yaƙinin rayuwarsa tafi tamu inganci

"A'a Malam kawai dai na ga ba’a Kano kakeba ba lallai ka gane kwatance naba”

Ya ɗan zaro ido

"Waya faɗa miki, ni ɗan kanone ina gidan kakanninane a Katsina”

Na dubesa alamun na tabbatar ɗinnan

Kai ya ɗagamin alamun eh ya ce

"Anan ma unguwar Gandun Albasa Babana yana da gida amma gidan wani abokin Babana nake zaune tun da na zo shi a can Nasarawa GRA gidansa yake, kin ga ko ni ɗan gari ne”

Na dubesa nace

"Haka ne amma dai yanzu mune 'yan gari”

Ya harareni

"Bayan na ji ance zuwa kuka yi ko daga ina kike gwarzo ko gwarzaye ne namanta Halima ce dai ta faɗamin"

Nayi murmushi

"Gwarzo ne”

"Ok yanzu ba za ki ba ni number ɗinba kota Mamace” na dubesa

"Mama ba tada waya saidai ta Baba”

Yace

"A'a barta ma rinƙa gaisawa a wayar Halima”

Na ɗaga kai alamar eh ba wai dan na gaji da hira da Malam Hamid ba mu kayi sallama, ban san daliliba bana taɓa gajiya da hirarsa duk lokacin da muka haɗu haka harso nake period ɗinsa ta shigo jinina da Malam Hamid sai na ce ya haɗu ka sancewar Malam Hamid ya iya tsara zance, dalilin da ya sa ba ko yaushe nakeson haɗuwata da shi ba musamman ba tare da su Halima ba fassarar ɗalibai tuni a fassara maganar da muke a cewa muna soyayya ne da malamai sun yi dokar hakan a makaranta ko malami saurayin ka ne to ku bari ki fita can waje ku yi firarku idan ya zo gidan ku, ajinsu Rumaisa na ƙarasa na faɗa mata saƙon na fito da na yi sa'a na tarar ba malami

Batul da ta gama kufula na tarar da ita inda na barta da shaf na manta da batun wata Batul da na ce ta zo muje ta rakani faɗawa Rumaisa saƙo taƙi ta ce min dai bari ta jirani a nan na dawo mu tafi ka sancewar tare muke tafiya da muna karasawa layin gidanmu take tsayawa ta samu napep hakurin da nakeso na bata ta katse zancena

"Kin ga ba abun da za ki cemin taho kawai mu tafi "

Bayanta na bi da ita har ta yi gaba ina sauri har na ƙarasa gurinta muka ci gaba da tafiya da shiru ya ratsa tsakaninmu

"Yi hakuri mana ƙawata”

Batul ta dube ni da hararata

"Ba wani haƙuri kina can kin samu Malam Hamid, ban ma san wacce tattaunawar kuke ba”

Na kalleta

"Wai dama kina hango mu"

Ta ɗaga kai

"Eh man da na yi niyyar zuwa to saina hango ana kallon love shi ne naki zuwa”

Wata muguwar harara na gallawa Batul

"Banasan wulaƙanci Batul, wanne irin kallon love”

Dariya tayi

"Nufinki ba musan komai ba, nifa na san danke Malam Hamid ke kirana waya, tun da kullum in yana kirani tambayarki kawai yake”

Na ɗan ja tsaki

"Wannan matsalarkice ni soyayya ma bata dame ni ba, bare kuma har na yi da malaminmu"

"Kanki ake ji mudai 'yan kai amarya ne Katsina dama ban taɓa zuwa ba” faɗin Batul tana dariyar shaƙiyanci da na san halin Batul ba ma ka mata komai ba tana zolayarka bare na ɓatamata rai amma baisa na ƙi tankamata ba

na sake haɗe fuska

"Batul ban san irin wannan, ke kanki kin san tsarin mijin da nakeso Malam Hamid bai kala da su ba kuma ma kin san bana sha'awa soyayya da malami nasha faɗamiki ina gudun kar wasu su ji su Kama”

"To sai me dan sunji aibu ne hakan, ko harammunne kika aikata, kuma batun kala aike ma kin san Malam Hamid komai ajin budurwa ba zatace ta girmi Hamid a wanda za ta so ba” ta karasa zancen tana gyara littafan dake rungume hannunta

Cikin ɓacin rai

"To ke mai zai hana ki sosa”

Ta sa dariya

"Ai dan ba ni ya nuna yana so ba”

Shirun da taji na mata yasata sassauta murya

"Gaskiya Sumayyah wannan ba tsari ba ne ban san kalar mijin da za ki ce ya yi miki ba, Yaya Hakeem da yake tamkar yayanmu shi ma kin nuna bai miki ba da ya nuna yana sanki, haba Habiba ban san wanne kalar miji kike son aure ba, tun da kinada tabbacin ba ci gaba za ki yi da karatu ba ya kamata ki aje komai ki zaɓi miji ki yi aure tun da kina samun maneman, sai dai kuma ban sani ba ko mai kuɗi kike jira”

Batul na kalla da ba dai abin haushi ba ana fara magana tiryen tiryen za ta bauɗe

"Batul bana tunanin Malam Hamid da Yaya Hakeem tafiyarmu za ta daidaita ba dan na san asalin Hamid ba amma na san na Yaya Hakeem, kuma kema sanin kanki ne ban taɓa tsammanin zan samu dacen auren mai kuɗinba, amma darajata nakeso bayan aurena”

Batul ce taja ta tsaya da ni ma banida zaɓi ban da tsayawar

"Wacce daraja ce da idan baki tunanin za ki samu gurin Malam Hamid ba kike tunanin ba za ki samu gurin Yaya Hakeem yayan Halimanki da kowa ya shaida kaunar da take miki da ita da nata iyayen dama duka 'yan uwanta, da kowa ma shaidane kedai kawai ki ce baki son Yaya Hakeem ɗin"

Nayi murmushi dan gaskiyane Batul ta faɗa kawai bana sha'awar auren Yaya Hakeem da ko Batul bata san daliliba bayan Halima da ita ce ta yi ƙoƙarin haɗa ni da Yaya Hakeem kawai don ta nuna soyayyarta gare ni, duk da ƙawance tunna yarinta har zuwa yanzu ya haɗa Halima da Firdausi budurwar Yaya Hakeem da suke son junansu amma ta yi ƙoƙarin canza akalar soyayyarsu take ƙoƙarin azata akaina, shi ma Yaya Hakeem don ya farantawa Halima yake ƙoƙarin biye mata, da a kan hakan muka fara ƙoƙarin kai ruwa rana da Halima da har yanzu ba mu dawo daidai ba, don na faɗawa Halima ba za a haɗa baki dani gurin cin amanar Firdausi ba da take ni ma ƙawa gareni saboda dalilin Halima na daban na san kawoni cikin danginsu. . .

Maganar Batul ta katse min tunanin da nake

"Shike nan tun da kinƙi don Allah ki amince da Malam Hamid yanzu"

Nayi tsaki na ci gaba da tafiya Batul ba dai matsala ba sam bata gane karatun kurma, kamar na faɗa mata aurenne a gaba na kome ma oho toma auren ma ai daidai ruwa daidai ƙurji dan ko da gani ma ido ba mudu ba yasan kima ina zan haɗa kaina da Malam Hamid duk da ban san asalinshi ba na lura dalilin hakan, ina jin kiran da Batul keyi min na shareta na ci gaba da tafiya cikin sauri harna ƙarasa layin gidanmu na shige kwanar gidan namu. 

**** **** 

Masu Neman Wannan Littafi na Iya Tuntuɓar:
Marubuciya: Halimatussa'adiyya Ibrahim Khalil
Lambar Waya: 08124915604
Na Cancanta

Post a Comment

0 Comments