Waya baba ya miƙomin da nake zaune ina wanke wanke a tsakar gidanmu karɓa na yi da ina duba wa na ga alamun an Kira wayarne ina ƙoƙarin tambaya waye Baban ya ce
"Kiyi magana ɗan uwanki ne Samir, ki kawon wayar idan kin gama ɗaki”
Nayi murmushi da na ƙaƙarosa don
tuni na gano wannan Samir ɗin
ne mai tambayarnan na ce ma Abba
"To"
Nayi 'ƙoƙarin kara wayar a kunnena
" ƙanwata ya kike”
Maganarsa ta katse tunanina na
maida hankalina ga wayar
Ban basa amsa ba na canza zancen
"Yaya Samir ina yini”
"Lafiya lau yasu Mama” hakan
da ya faɗa na ayyana a
raina Allah ya sa kar tambayar ta zarce
"Lafiya lau ya kowa da kowa”
Yace min
"Alhamdulillah"daganan
shirun 'yan sakanni ya rasa tsakaninmu Samir ya yi 'ƙoƙarin sauke numfashi
"Hala tsoron mutane kike
ko?"
Na tsaro ido kamar yana ganina
"Ni ɗin kuma?"
"Eh mana ina kallon
yanayinki wancen karan saboda tsoro haka kika tafi ba mu gama gaisawa ba”
Nayi murmushi kamar yana ganina
"Kai Yaya Samir ban da gaisawar
da mukayi
"Ina wata gaisawa bayan tambayata
tasa kin gudu"
Nayi dariya na ce
"Waya faɗama saboda tambayarka na
gudu"
"Saboda na san hakanne, dan
haka nake duk inda naje don duk na fara manta mutane tun da na dawo daga karatu
kin san ba a nan ƙasar na yi ba, ko 'yan Gwarzo saida suka yi zancen tambayartawa,
to bare ke da mukayi nesa da juna, yaushe za ki zo Katsina?"ya ƙarasa
maganar yana tambayata
"Babu rana”
"Ah haba dai idan kun gama ƙualifying
zan zo na tafi dake?"jim na yi jin abin da Yaya Samir ya faɗa sai da ya sake magana
"Ko bakya son kizo gidanmu, bayan
kuma yanzu muka gama magana da Abba ya ce min saina zo"
Bani da zaɓi jin Abba ya amince sama da ni ma na amince
"To shike nan Allah ya kaimu
lafiya”
Yace
"Amin amma yaushe za ku gama
ƙualifying
ɗin"
Kamar ba zan basa amsaba
"On 20"
"Ok zan zo On 25 sannan kin
shirya komai ko?"
Shiru na yi Masa
"Shike nan tun da ba za ki
magana ba na lura har yau baki gama sabawa dani ba” ban basa amsa ba
"Sai anjima” kawai na faɗa na katse wayar na kaiwa
Abba wayarsa na dawo na ci gaba da wanke wanke na a raina ina tunanin ko wanne
zama zan yi gidan Baban Katsina muna nesa da juna ba su taimaka mana bare kuma
naje inda suke na ɗora
musu nauyi, inada yaƙinin Baban Katsina bai san da zancen zuwana ba kawai Yaya
Samir ya shirya zancen zuwan nawa, amma dai a yadda na san babu mai sonmu a
dangin Abba babu wanda zai buƙaci muje inda yake haka nan ba tare da
wani daliliba da ni ma na san dalilin Yaya Samir da na fahimci yanasan zumun ci
zanje haka na karasa aikin da nake jikina a sanyaye ɗakinmu kawai na shige na kwanta ina tuno
wayata da Yaya Samir ban san dalili ba tun bayan gama wayarmu na ji hankalina
bai kwanta da zuwana Katsinan ba
Sallamar Halima ta katse min
tunanin da nake yi da sai yanzu na san ta zo gidannamu amsa mata, na yi gefen
tabarmar da nake kwance ta zauna tare da cewa
"Hala dai lafiyarki ƙalau
kizo kika kwanta haka ke kaɗai”
Nayi murmushi
"Bakomai, na yi aikine na
gaji”
Hararata ta yi tace
"Wanne irin gajiya, yanzu
Mama ta faɗamin kika
shiga ɗaki bayan kin
gama wanke wanke, dan Allah ki faɗamin
damuwarki”
Na ɗan
ja numfashi Halima ba ƙawar da za a ɓoyewa
wani abu bace don tafi ƙarfin a kirata ko da aminiya saidai 'yar uwa na dubeta na fara
magana
"Halima ɗazu Yaya Samir ɗan Baban Katsina yayan Abba
ya kirani waya a wayar Abba a kan cewa mana gama ƙualifying zaizo ya ɗaukeni mu tafi Katsina, shi
ne hankalina ya kasa kwanciya”
Halima ta zaro ido tace
"Katsina fa nidai bana yi
miki sha'awar zuwa dacen da kuke ƙananu waya taɓa tunanin ya ɗauki
wata cikinku sai yanzu da kuka fara girma, dama zaman bauta kaɗai za ki yi da sauki amma
wulakancin da zai rika biyo baya nake gudarmiki da za a riƙa
shimfida miki, shi Yaya Samir ɗinma
akanme zai tunanin hakan"
Na girgiza kai nace
"Wallahi ban saniba Halima
amma shi bai san duk abin da ke faruwa ba, ta yiyuma Baban Katsinan bai san
abunda Yaya Samir ɗin
ya yi ba”
Halima ta ɗaga kai tace
"Eh haka ne amma dai Mama ya
kamata ta yi magana a kan ba za ki ba”
Na dubi Halima nace
"Halima Mama fa ta yi magana
kika ce to ai tanayi abun zai zama abun magana, dama ita da hakannan ma ba
tsira ta yi ba a gurinsu, Kuma Abba fa ya amince”
Tsaki Halima ta yi daga bisani
tace
"Allah ya kyauta zance kawai
don nidai na san ba wani farin ciki za ki acanba dan da zaman da za ki yi acan
wallahi gwara na nan ko ba kullum za ku ci ba”
Da haka muka ci gaba da fira da
Halima da muna cikin firar wayar ta yi ƙara da wayar duk da keypad ce ta ba ni sha'awa
saboda ni ko kamarta ba ni da ita da ita ma yayanta Yaya Baffa ya bata tsohuwar
tashi daya canza sabuwa duba wayar ta kalle ni ta yi murmushi tana 'ƙoƙarin ɗagawa ta ce min "Malam
Hamid ne ɗazu ma ya
kirani waya, yana tambayata naje gidanku na ce masa a'a zanzo dai anjima shi ne
kin ga yanzu ya sake kirana”
Daganan ta ɗaga wayar Sallamar da ta yi
a wayar na ji daganan na ji ta ce "to" ta miƙomin wayar
Na karɓa kawai na kara kunne ba tare da na ce komai
ba Malam Hamid na ji yafara magana cikin muryar da ban ma san ya iya irinta ba tun
da bantaɓa ji ya yi ba
kamar mai jin barci ya ce
"Sumayyahty babu magana”
Jin sunan na yi banbarakwai nanma
dan nasa ba da Sumayyahty yake faɗamin
shiru na yi don ban san amsar da zan bashi ba, shirun da yaji na yi ya ci gaba
da cewa
"Nayi laifine”
Kaina girgiza kamar yana ganina
na ce
"A'a”
Ya ɗan
marairaice murya
"To mai na yi”
"Ka canza” kawai na iya faɗa
"Dame kuma” ya ba ni amsa
Nace” da komai”
Ya ɗanyi
'yar dariya da na ji sautinta a waya ya ce
"Kin ba ni dama na sanardake
dalilin canzawartawa”
Nace masa” Eh"
Sai kawai na ji ya ce
"To kece sila”
Zaro ido na yi kamar yana ganina
tare da cewa
"Ni kuma saboda wanne dalili
Malam"
"Dalilin inasanki, tun
farkon ganina dake Sumayyah na ji hakan da a yanzu nafi tunanin lokacin
sanarmiki yayi. . . . "
Ba tare da na ƙarasa
jin mai zai faɗa ba na
katse wayar hawaye suna wanke min fuskata da ban san da taruwarsuba saidai
zubarsu kawai
Halima ta dube ni bayan miƙa mata
wayar da na yi da duk abin da nake faɗa
tana ji
"Lafiya Sumayyah mai ya faɗamiki Malam Hamid din"
Hawaye na na ci gaba da zubarwa
na dubeta
"Halima so na ya ce yanayi,
ba zan iya haɗa
rayuwata da mutum kamar Malam Hamid ba”
Kallona ta yi cikin nuna danuwa
"To saboda ance ana sonki
kike hawaye, to sai dawa za ki iya soyayyar, gaskiya Sumayyah ki tsaya ki nutsu
kima kanki faɗa haba, dan
ance ana sonka ba'abun gwama numfashi ba ne, so dai game hankali ga wanda ya
nuna yana sanshi ai shi akeso, babu alaƙa tsakaninmu amma buri na ki yi aure”
Na girgiza kai
"Eh na sani amma Halima ke
kanki kin san kina kallon Hamid kin san rayuwarsa tafi tawa koma da ya ne, ni
Kuma na fison auren wanda rayuwarmu ta yi dai dai da juna”
Tsaki Halima tayi
"Wannan ba hujja bace kwata
kwata, kuma banga aibun Malam Hamid, bare kuma na ga wani alamu na da zai nuna
Malam Hamid yafiki ba, ki tsaya ki nutsu ki fahimci hakan dai tukun"
Murmushi na yi da ba ni da zaɓi da ya wuce yadda amma dai
ni haka zuciyata tafi tunani ni kuma nafison auren wanda rayuwarmu ta yi dai
dai da juna
"Shike nan na amince
to"
Dariya ta yi
"To ai ba ni za ki faɗawa ba, kuma baki shawara
da zuciyarki ba ta ina za ki amince masa”
Nima dariya na yi nace
"Aike radiyonsace, kuma
kamar zuciyace ke a gurina, ke kin mafi zuciya saboda zuciya ba lallai duk abin
da ta tsakani na aiwatar ya zama daidai ba, amma ke zuciyace mara sirki da duk
wani abun da zai jawo aikata da na sani, dan haka shawararki ita ce abar ɗauka, danko Mama ita ma na
san hakan za ta fadamin"
Murmushi tayi
"Wato kin janye min
ko?"
Nayi dariya
"Ai dole a janye wa ƙawar
kwarai da kowa ke fatan samu a rayuwarsa, ke na faɗamiki ko aminiya na faɗamiki sunan baidace da keba”
Kai Halima ta girgiza
"Sumayyah banison yabofa, komai
na yi miki cancantarki ce hakan"
Na dubeta
"Cancanta fa kika ce”
Ta ɗagamin
kai
"Kwarai kuwa, Sumayyah
kinada halin da kowa zaiso zama dake, ya kuma ƙarar da komai gurin don son zama dake, kina
da juriya, tare da sanin darajar wanda duk kike tare dashi”
Dariya na yi
"Idan harna ka sance hakan
to kece sanadiyyar zamo wata haka, Halima da a ce zan rubuta littafi akanki
littafi ɗaya ya yi kaɗan gurin bayyanarwa da
jama'a halayyarki, halinki ya girmema kyawunki da shekarunki, kin tallafamin a
lokacin da kowa ya nuna bayason mu hatta a dangi kin yi tarayya dani bisa
tsantsar ƙauna
da gani har zuriyyata kuma kin zauna dani bayan kin fahimci mu talakawane da
kullum suke neman abinci yau da gobe, kikan iya ƙin ci ki ba ni ni naci, duk abin da kike
da shi nawane ni dake, Halima ban san ta ina zan biya ki ba”
Murmushi tayi
" Ai Sumayyah ƙawa ta
gari ba dubawarta abin da kika mallaka ba ne dubawarta cancantarki ya ɗabi'unki suke kyawawane ko
kuwa, shin kina umarni da kyakkyawa ko kuwa, kuma yaya soyayyarki da duniya
take, kina tuna Allah a dukkan lamuranki, ni a nawa tunanin sune abin dubawa
bawai arziƙi
ba domin su ababene masu ƙarewa, a lokacin da akace ba zaka yi ƙawance da wadda ka fita
wani abu a duniya ba to ta ina za ka fahimci ta inane za ka tallafi rayuwar
wasu kuma idan kace sai da waɗanda
suka fika zaka yi mu'amala ta ina za ka san kanada wani matsayi a gurin wasu, idan
ba ka mu'amala da waɗanda
kafi su wani abu ba ba ma za ka fahimci Allah ya yi ma baiwar da wasu ba su
samu irinta ba kullum tunaninka yadda zaka yi kakai gurin da waɗanda suka fikan suka kai
shike nan sai ka fara rashin godiyar Allah ni a ganina kayi Mu'amala da kowa ta
yadda tsoron Allahnka zai riƙa ƙaruwa malam mai ahalari yana cewa idan za
ka so mutum ka soshi domin Allah, kuma dukkan musulmine ai ɗan uwan musulmine”
Na jinjina kai alamun gamsuwa
"Amma Halima 'yan uwana sun
kasa fahimtar abin da ke ɗin
kika fahimta”
Kafaɗata ta dafa
"Yi hakuri Sumayyah za su
fahimtane wata rana, domin talaka da a ce an tanbayesa Yaya yakeso ya rayu a
duniya da ba zaice yanaso ya yi rayuwa cikin talauci ba, kuma arziƙi
nufin Allah ne idan zagayenka ya zo za ka iya samu idan Allah ya ƙaddara
za ka samu, shi ya sa kullum addu'ar da ya kamata mu riƙayi idan Allah baisa za
mu samu shiga wata ni'imaba a duniya Allah ya ba mu dacewa ta shiga cikin
ni'imar aljannah, a wannan duniyar idan akace talaka bai kyautata bautarsa ga
ubangiji ba bana tunanin zai samu hakan"
Jinjina kai kawai na yi alamun ina gamsuwa da maganganun Halima.
**** ****
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.