Ya Allah ina godiya da bisa dukan ni'imominka a gareni. Yanda na fara Lafiya ka ba ni ikon gamawa Lafiya. Alkhairan da ke cikinsa ka ba ni ladansa, sharrin da ke ciki ka yafe min.
Allah ka dauka Alkalamin marubuta a duk in da suke
Gaisuwa ta musamman gareku na hannu dama ta.
- Besty (Sarat Alkasum)
- Maman Amatullah
- Ummu shkura
- Fadila Sani Bakori
- Maman Sharifa
- Mamashu
- ABBA Yakubu
- Dan Salma
- Da Autan Jarumai.
Waɗanda ban samu damar kiran sunansu ba, duk ina mika sakon gaisuwata a gare ku.
Yayyena abun Alfaharina
- Hadiza
- Hussaina
- Hassana
- Maryam
Gaisuwa ta mussaman gareki
Anty Zulai, mutan Kano, surukar Auta na.
Jarumai Writers Association, marubuta masu aiki da Jarumta wajen Fadakar da Al'umma
MAKAUNIYAR SHARI'A
IKILIMA ADAM (Kyauta daga Allah)
09069080725 ko +22953726162 (Whatsapp kaɗai ban da kira)
Marubuciyar da ta nishaɗantar da ku a littattafanta kamar haka:
- Kai ka ja wa kanka
- Kanwata
- RAI DAYA (Jan Za ki)
- RUDANI (mai tafiya daukan rai)
Da sauran su.
Yanzu ga ni ɗauke da sabon littafina mai suna MAKAUNIYAR SHARI'A
****
SHAFI NA SHA UKU
Suka bata amsa da mun kawo muku
sammaci ne daga kotu ". Cewar Dsp Faisal Haruna yana mai kallon yanda
Yasmin ta rikice lokaci daya.
Yasmin cikin zazzare idanu da
tsoro da fargaban abunda ba ta yi zato ba ta ce " a kan wani laifi ake
karar mu". Muryanta na rawa ta karashe zancen, nan da nan taji cikinta ya
murda gudawa na son barke mata, cikin matse kafa da fitar hayyaci da sassauta
murya kada Mamy taji ta ce " Yallabai munyi muku kama da yan daba ne, ko
barayi ko yan Kidnapping ne, nayi tambaya kunyi shiru kuna zuba min idanu
". Ta karashe zancen murya na rawa.
Dps Faisal shi da yaransa
kallonta suke kana suka kwabe baki, cikin tsare gida Dsp Faisal ya ce " ko
alama sam baku kama da barayi ko yan daba da sauransu asalima ke Yasmin kina
kama da Mahaifin Alhaji Isah, watau Alhaji Taufik Sharifai, sai de hausawa
sunce kama da wane bata wane, shari'a sabanin hankali ce, amshi takarda sammaci
daga kotu inda ake zargin ku ba ya'yan Alhaji Isah ba ne sannan kuna zaune
gidansa, kunki tashi, kunsan akwai rayuwa akwai mutuwa kada ya mutu aci gadonsa
bayan ba ya'yansa ba ne ku ". Ya kai karshen zancen tare da mika mata
papper.
Tana karban papper daga hannunsa
suka juya suka tafi suna girgiza kai, ita kuwa cikin daukan salati ta koma
dakin kamar an mata albishir da ranar mutuwarta, tana karasa dakin taga Mamy
tsaye kikam, tsayuwar da bata taba ganin ta yi ba duk tsawon rayuwarta irin
tsayuwa me nuni da zuciyarta ta kyakyashe babu maganar sauran kuka a gabanta. Cikin
razani Yasmin ke fadin " Mamy dan Allah ki zauna na ga sai jijjiga kike, kinsan
lafiya be isheki ba pls dan zauna in miki bayani ". Ta karashe zancen tare
da ƙoƙarin
kama hannun Mamy. . .
Mamy kauda hannunta ta yi tana mai kallon
Yasmin cikin idanu.
" naji komai kuma na shirya
da muje kotun dai, ba mu da karfin daukan lauya ". Juya kwayar idanunta
sama ta yi tana mai cigaba da fadin " muna da babban Alkali ne shi ne
Allah, kuma nasan baze kyalemu ba zebi mana hakkinmu ". Ta karashe zancen
idanun ta na kallon saman cikin rawar jiki
" Yasmin kada wannan ya daga
hankalin mu, daga yau mu fara hada kayayyakin mu, muna jin karshen zaman kotu
sai mu kama gabanmu ". Kukan da take dannewa ne ya kamata batare da ta
ankare ba.
Cikin kuka ta ce " Alhaji Isah yau ni
A'isha ni ce na haifa masa shegu, mutumin da nice silar arzikinsa bayan wahalar
da muka sha na rayuwa ni dashi, mahaifinsa yabar masa makudan kudade na gado, yan
uba suka hana masa kudin har kudaden suka salwanta, da kudin sana'ata na
atamfofi na bashi ya yi jari dashi a lokacin ko naira dari yana gagararsa amma
yau ya nuna nice banza, ya shirin tona min asiri a garin nan, in mun bar gidan
nan ina za mu raba ". ta karashe zancen cikin kuka mai cin rai da bakin
ciki.
" Yasmin kiramin yayyenki su Fauziyya da
safiya amma pls kar ki kira Firdaus dan tanada ciwon zuciya kuma tsohon ciki ne
da ita, sun san halin da ake ciki, dan susan yanzu ba suda gidan Uba.
Yasmin sosai ta fara jin takara
tsanar Alhaji Isah, cikin kuka ta ce " zan ari wayar baba mai gadi in
kirasu, amma pls ki bari anty Firdaus ta san halin da ake ciki".
Mamy cikin damuwa ta ce " ba
za ki gane ba ne, Firdaus mijinta ba me karfi ba ne kuma unguwar su akwai nisa
da cikin gari, baya ga haka batada isasshen lafiya, so kike tashin hankali ya
sa nakuda ya tashi lokaci beyi. . . . . ". Shiru ta yi jin muryan Firdaus
tana shigowa daga dakin sanye cikin doguwar riga fuskarta babu walwala bakinta
na rawa ta ce" da Haihuwa da aure da mutuwa da kaddara lokaci gare su, in
kinga na haihu ki tabbatar lokaci ne ya yi mayan". Ta ƙarshe
zancen tare da kaiwa Mamy runguma.
Cikin kuka ta ce" Mamy duk abin
da ake ciki na sani, ina daga bakin kofa ina jinku, Mamy dan Allah ku in gudu
da ku cen unguwarmu akwai wani dakin bukka sai na kama muku haya, Mamy nasan ba
za ki taba yarda ba, da wallahi cikin gidana akwai daki sai ku zauna ".
Mamy dago Firdaus daga jikinta ta yi cikin
kuka ta ce"Firdaus mun gode da ƙoƙarinki amma kiyi hakuri bazan iya zama
inda kike so ba, hakama bukkah ". Ta karashe zancen cikin raunin murya.
Firdaus zama bakin tsohuwar
katifar dakin ta yi dakyar saboda nauyin cikinta, babbar wayarta mai kirar
Samsung Galaxy ta fiddo tare da dannawa Fauziyya kira domin sanar dasu halin da
ake ciki.
Cikin kuka da tashin hankali ta
shiga baiwa Fauziyya labari daga haka sukayi sallama cikin kuka. .
Cen ɓangaren Fauziyya sosai ta fita hayyacinta har
mijinta daya shigo dakin sai tambaya yake lafiya kuwa? amma ina ta kasa ba shi
amsa ban da hawaye ba abin da ke kwaranya daga idanunta, kuka take mai nuni da
bakin ciki, tun suna yara suke cikin kangin wahala har sun girma abun gaba yake.
ABUJA
Umar Faruk a gwarinfa zaune gidan
Alhaji yana baiwa shukoki ruwa, cikin rashin walwalan rashin ganin ogansa ya
zauna tsakar gidan yana karewa kyawun Gidan da tsaruwarsa kallo, amma a
zuciyarsa yana fadin ai Gidan Alhaji Isah yafi wannan haduwa da komai, ganin sake
sakensa bashi ne mafita ba, ya sa je gun mai gadi ya aro waya, daman ya saka
kati aciki, dan gefe daya ya raba yana kiran number Bala mai Gadi na kwatano
dan a kan wayarsa ake samun su, jin switch off ya sa hankalinsa tashi ba kadan
ba, ya dade yana gwadawa abu daya suke maimaita masa.
So yake bayan sun gaisa ya sa a
nemo masa lambar ogansa a cen garejinsa. Da wannan tunanin ya dan ji sanyi a
ransa.
Mai da wayar ya yi ya fara yunkurin dan fita
waje ya dan ga gari, kasantuwa kullum yana cikin gida, shi kuwa be saba da
hakan ba.
Sosai jikin Mama ta ji sauki, likita
har ya ba su daki, Mansura ce zaune a gefenta tana chat, da dukan alamu ta yi nisa
dan sai darawa take ita kaɗai,
jin karar tsayuwar mota a farfajiyar gidan ne ya sa ta tashi domin lekawa ta
window, cikin jin dadi take kallon Mansur da Ridwan sun fito daga motocinsu, dukansu
suna sanye cikin shadda brown, " waouh ". Ta furta ya yin da ta ga
Rid yana musabaha da wasu likitoci da dukan alamun akwai sanayyah sakaninsu, haka
ma Mansur haka sukayi ta musabaha da likitoci maza masu wucewa, cikin fara'a da
sakin fuska. Wayar Rid ne ya fara ring, hannunsa ya zira cikin aljihun wandonsa,
yana zaro wayar ya kai dubansa a kan fuskar wayar, Ganin commissiner ne ke
kiransa ya sa shi komawa da baya baya tare da dawowa kusan inda ya yi parking
din motarsa.
Bayan sallama da sukayi bayan ya
daga wayar daga cen bangaren, Commissiner da ke zaune a office kana computer na
gabansa ya ce" Dsp Ridwan Muhammad Mai nasara dan Allah akwai aikin da
zaka fara muna tun agida kafun ka dawo aikinka".
Ridwan jin ya ambaci kalmar aiki ya
san aiki ne mai girma wanda shi kaɗai
ake bai wa, ba su taba bashi me saukin yi ba, fesar da numfashi ya yi tare da
jingina jikin motarsa kana idanunsa na kan Mansur da ke cen tsaye yana jiran
isowarsa. Tattara nutsuwarsa ya yi wajen amsa wayar.
" Inajinka". Shi ne
amsar da ya bayar yana kallon Mansur da ke daga masa hannu alamun zeyi gaba
yana jiransa acen, shi ma kai ya daga masa hakan ya sa Mansur yin cikin
asibitin.
Dagacen bangaren Commissiner ya
ce " Ridwan nasan kasan Haruna Karfin Iko ".
Gaban Ridwan sai da ya bada rasss
!!!!!! jin ya ambashi sunan. Nan take yaji kamar yana son ya kara ajiye aikin. Commissiner
ne ya katse masa tunani ta hanyar fadin " ya kayi shiru ina magana?".
" Am sorry wai na tsaya
saurarenka ne, kwarai kuwa nikuwa nasan karfin iko, wannan karan me kuma ya
aikata? ". Ya yi tambaya cikin kadawar harshe.
Nan dai Commissiner ya fara zayyano masa
dalilin kiran nasa da kuma abin da yake son ya masa. Rid cikin gamsuwa da
bayanansa sukayi sallama.
Kasa barin wajen ya yi yana mai cigaba da
jingina jikin motarsa, yatsarsa daya abaki yana juya kalaman Commissiner, jin
wayarsa ta kara yin rîng ne ya sashi kai dubansa akai inda yaga Mansur ne ke
kira, be daga ba illah kawai hanzarta yin cikin asibitin ya yi.
Mansura tana ganin Rid yabar
wajen motarsa cikin hanzarinta tabar wajen window tare da bude jakarta dan
karamin turarenta ta dan fesa ajikinta, tare da mai da sauran cikin jakarta, duk
abin da take Mansur be san tanayi ba dan hankalinsa ya tafi a kan Mama da ke
tari, ban da sannu ba abin da bakinsa ke furtawa. Ƙarar bude kofa ne ya
tabbatar musu da Rid ne ya iso.
Mansura nan da nan ta fadada
murmushinta tana mai jiran isowarsa, shi kuwa yana shigowa dakin fuskarsa ba
walwala sosai dan wayar da ya gama ya sa duk kuzarinsa ya tafi, da sallama a
bakinsa ya karaso tsakiyar dakin, cikin ban girma ya durkushe yana mikawa Mama
gaisuwa. Mama cikinsanyin murya ta amsa masa tana murmushin ganinsa. Yana tashi
daga durkushen kallon Mansura yake yanda take washe masa hakora kamar me tallan
maklin ya sa shi tabe baki kamar ana masa dole ya ce" Mansura yan
makaranta ya me jiki?".
" Jiki da sauki Alhmdulillah
". Cewar Mansura cikin yauki.
Lumshe idanunsa masu kwarjini ya
yi kana ya dan budesu a kan Mansur da ke masa murmushi yana mai nuna masa
kujerar kusa dashi, ba musu ya zauna, suna taba hira shida Mansur.
Mansura cikin iya bariki ta
ce" wai kunga yanda kukayi kyau kuwa, bara na ɗaukeku hoton tarihi".
Ridwan najin haka kamar ya fasa
ihuu dan kwata be yarda yan mata su ɗauke
shi hoto, wata zuciyar ta raya masa ai babu komai, ita ma kanwarka ce. Da haka
ne ya sa shi ɗan yin
murmushin yake, ita kuwa soma daukarsu hotuna ta yi inda cikin dabara ta samu
ta dauki Ridwan shi kaɗai
batare da Mansur ba, cikin jin dadi ta koma ta zauna, shi kuwa Ridwan ji yake
inda zega wayarta dasai ya dauka ya goge hotunansa tass.
Ridwan sai bayan isha'i ya dawo
tsararren gidansu, babu abin da ke dawainiya dashi da yawuce gajiya, tafiya
yake sam ba'a jin takunsa har ya kusa karasowa falon inda ya ci karo da Mamy da
Aminiyarta Madina suna hira da dukan alamu sunyi nisa sosai, cikin zallan takaici
da damuwa Mamy ke fadin " ai yanzu Ridwan be da gindin zama tunda kanwar
uwarsa, Maman Mansur ba lafiya". Ta karashe zancen cikin takaici.
Madina kam sosai ta jinjina
lamarin cikin ban hakuri ta ce " kedai barshi wanda yaki sharar masallaci
ai zeyi na kasuwa, ban da tsabar gulma da kinibibi da neman suna yanzu ace. . .
. . ". Ragowar kalamanta ne ta kasa karasawa ganin Ridwan ya raba ta
bayansu ze fice, kallo daya ya musu cikin kasa da murya ya ce " sannunku
da hutawa ". Mai da kallonsa a kan Mamy da shi din take kallo ya yi, cikin
ban girma ya ce " Mamy ina yininku?!! ". Daga haka ya sakai ze fice
ba tare da ya jira amsa ba.
Muryan Madina ya ji tana fadin
" dan dakata Ridwan, baka sanni ba ne ita kuwa mamy bazaka zagayo ka
gaishemu cikin mutuntawa ba ". Ta karshe zancen tana maganar zuci inda
take fadin " Ai Rid sai na Aure ka wannan yaron haka ya kara yin kyau da
haduwa". Ta karashe zancen tana kallon yanda yake tafiyarsa kamar besan da
ita ba, dan ko waiwaye beyi ba bare tasa ran ya ji ta.
Cikin zallan mamaki Mamy ta
ce" ai baze tsaya ba, na tabbatar in wasu kama gari ne da tuni ya tsaya
wurin ".
Bebi ta kansu ba, kai tsaye ya yi sashinsa
domin a zuciyar sai fadi yake ban da lokacin amsawa wancen makirar matar amsa.
Madina cikin kaduwa ta ce "
Anya Yaron nan beji firarmu ba? ". Ta kai karshen zancen cikin ayar
tambaya.
Kar kada kai Mamy ta yi cikin
shakku ta ce beji komi ba, ai haka yanayinsa yake musamman in har yana tare da
gajiya. "
Kwabe baki Madina ta yi inda suka
ci gaba da tattaunawa, itakuwa Madina babban burinta ta ga Rid dan ya tafi da
imaninta, yanda kasan yau ne ta fara ganinsa.
Ridwan na shiga dakinsa ko wankar
da ya saba beyi ba, hakanan ya fada gado ya kwanta, maganganun Commissiner ne
kaɗai ke masa zarya
cikin kwanyar kansa, haka nan ya ji sam baya jin ze iya barci, tashi ya yi ya
zauna inda ya dauko laptop ya sa a gabansa, wayarsa ya dauka ya fara daukan
wasu bayanai da numbobi yana mai kara matsowa da laptop din gabansa, ganin baya
gani dakyau ya sa shi tashi dauko médical glass dinsa, sanyashi ya yi fara fara
kallo dakyau. . .
Acikin computer sa wani
kayataccen Gida ne yake kallon na Alfarma, yana kallon tsarin gidan da komai, kana
ya kai dubansa a kan hoton da ya bayyana a gabansa ganin An rubuta Amatullah
Haruna Karfin ikoh, zazzare idanu ya yi ganin hoton Amatullah ya bayyana, zumbur
ya miji tsaye bakinsa na rawa cikin kidima kamar ba shi kaɗai ne a dakinsa ba ya ce
" Wannan Yar kauyen. . . . . . . . . . . . .
Muje zuwa
Makauniyar Shari'a taku ce
Share and comment pls
[10/23, 5:37 PM] Kyauta Daga
Allah: Makauniyar Shari'a
Sai a lahira
NA
IKILIMA ADAM
(Kyauta daga Allah)
Kai ka Jawa kanka
Kanwata
Rai daya jan za ki
Rudani
RAYUWAR Ma'aurata
Kaicona
Duk wanda kuke so sai ku tuntuɓeni a kan wannan lambar
09069080725
Akwai rangwame sosai ga me buƙatar
dukansu.
Kar ku manta Makauniyar Shari'a
littafin kuɗi ne free
page ya kusa karewa.
SHAFI NA HUDU
Wannan Yar kauyen Daguzau ce? me
ya kawo hoton ta a nan " yake tambayar kansa cikin zallan mamaki, hannunsa
na zoomin din hoton, nan da nan ya fara tariyo abin da ya faru a kauyen da kuma
irin takaicin da ya daya kwasa akanta, cikin kadawar tunani yake ƙoƙarin
nazari a kan lamarin anya kuwa ita ce? rasa me bashi amsa ya sa shi kara nusawa
cikin tunanin son gano gaskiya, sai hamma yake. ciki kasala yake toshe bakinsa
hade da fara lumshe idanunsa, idanunsa na cigaba da tariyo masa hoton cikin
computer a kasalance ya yarufe laptop din, ba tare da ya kashe komi ba. Wannan
karan kwanciya ya yi ba tare da ya yi adu'oi da ya saba na kwanciya barci ba. Yadauki
awa biyu yana barci inda sosai barcin yau ya masa ma mugun kamu . Ahankali daga
waje ake turo kofar dakinsa, sanin da aka masa baya kulle kofarsa sai weekend, suna
tura kofar sannu ahankali cikinsandasanda suka fara leko kai, ganinsa yana
kwance ya baje yana barci, alamun ya yi nisa sosai dan ko kwanciyar kirki beyi
ba a bakin gado ya kwanta.
Mamy da Madina kallon juna su
kayi suna rarraba idanu a kan dakinsa da sam babu takarce, computer da ke
gabansa suke kallo, cikin kasa kasa da murya Madina ta ce " Saratu ko za
ki iya fita dakin dan Malam yace ke Mahaifiyarsa ba za ki iya aikin ba dole sai
an samo wani, da muje waje samun wani gwamma na yi miki mun rufawa juna
asiri". ta yi magana cikin kasa da murya. Mamy jin hakan ba ta yi musu ba
ta fice tare da jan kofar ahankali ta fita cikinsanda. Ita kuwa Madina tana
ganin fitar Mamy ta karaso tsakiyar dakin, gab da shi ta karaso tana karewa
kyakyawar fuskarsa mai haske da sheki kallo, sajen fuskarsa yanda suka kwanta
lub lub take bi da kallo, bata san sanda ta furta " Ma sha Allah", Kasar
zuciyarta. Kallon yanda yake barci bil hakki take tana kwabe baki, cikin karfin
hali da ƙoƙari
irin nata, ta zauna kan gadon nasa ahankali, hannayenta masu kaushi ta sanya
ahankali tana shafa fuskarsa, shi kuwa Ridwan acikin barcin ya dan kara motsawa
hakan ya sa ta yi hanzarin cire hannunta, durkushewa ta yi da kanta tana ƙoƙarin
sumbatarsa a baki, kamar yana sane sai ya kifa a gadon. Ahanzarce ta dago tana
kallon ikon Allah cike da fargaba, mutum sai ka ce mai ido hudu, ganin yanda
yake a kife hannayensa duk ya sake su bakin gado, cike da ƙoƙari da
rashin tsoro ta kamo hannunsa daya tana shafawa ahankali, wani bakon yanayi ta
ji yana fisgarta ji take tsigar jikinta na ta shi, nan take ta ji yarrrrrrrrr a
ilahirin jikinta, abin da zata iya rantsewa duk auren da ta yi a baya bata taɓa jin hakan ba, jikinta na
tsuma kamar mazari ya sa ta yi hanzarin sakin hannunsa wanda ya janyo hannun
buguwa da bakin gadon. Daga cikin barcin ya ji zafin buguwa, hakan ya sa ya
yamutsa fuskarsa, tare da fara yunkurin juyowa, Madina na ganin réaction dinsa
son tashi.
Ahanzarce cikin azzama ta labe bayan labule
cikin tsananin tsoro da fargaba.
Shi kuwa zaune ya yi bakin gado
yana kallon hannun nasa da ya buge din, cikin jin inda ya bigen na masa zafi, ya
rike dai dai inda ke masa ciwo yana matsawa ahankali tare da ciza labbansa, tsaki
yake ta jerowa ta yanda akayi ya kwanta ba Alwala da adu'oi, tashi ya yi yana
mika tare da kai dubansa kofar dakinsa cikin idanunsa mai ɗauke da tarin barci, ɗauke ganinsa daga nan ya yi
ya dawo dashi kan labulen dakinsa da yake gani dishi dishi tare da tsurawa
wajen idanu sosai ba kiftawa, rike da kungunsa ya ke bin wurin da kallo sosai, kana
ya kai dubansa a kan kasan labulen. Har ya fara yunkurin tashi domin zuwa wurin,
Madina na ganin ya tashi kamar ze nufo inda take ban da innalilahi babu abin da
take maimaitawa wani uban zufa ne ya karyo mata lokaci daya.
Ganin ya canza akalarsa zuwa banɗaki, ya sa ta fara sauke
nauyayyen ajiyar zuciya. Tana jin sanyi na ratsata ganin ya shige banɗaki.
ganin ya shiga, kwararan ajiyar zuciya ta
ringa sauke wa akai akai, kana cikinsauri da hankali ta bude kofar ta fita tana
haki, koda ta karaso wajen Mamy zuru zuru da idanu take bin Mamy da kallo cikin
boye tsoronta hade da zama kan kujera ta ce " wallahi Saratu Danki Ridwan
Aljanunsa suna da karfi sosai, amma a karshe dai sunce sai kin taimaka min
wajen gudanar da aikina ". Ta karasa zancen baki na rawa.
Mamy da zallan mamaki take
kallonta, cikin hanzari ta ce " wani Irin taimako zan baki, fadi kawai
kinsa baze gagara ba".
" Inason mu sanyawa Ridwan
maganin da ze sanya ya fita hayyacinsa na tsawon awa biyu ko uku, amma acikin
abincinsa". Ta karasa zancen cikin bukatuwa.
Mamy cike da faduwar gaba ta ce
" ai Ridwan kwata kwata tunda ya yi wayau baya cin abincin Gidan nan, kuma
ko da yana ci taya zan amince a sumar min da yaro har tsawon wannan lokutan, kinsan
bazan yarda ba gaskiya, Malamin naki besan aiki ba ". Cewar mamy cikin takaici.
Madina kuwa ranta ya soma baci, cikin
fushi ta dau jakarta da ke kan Centre table tana fadin " ai ke ce kika ce
bakya son ya yi aure yanzu kuma ɗan
ana neman hanyar da baze taba sha'awar yi ba kinzo kina fadamin maganganu, wannan
ba komai kike min ba illah gorin haihuwa, ai na dauka Ridwan ni ma dana ne za
mu iya cika burinki ashe kallon muguwa kike min, bayan ke ce kika bukaci hakan
". Ta kai karshen zancen tare da kama hanyar fita daga kayataccen falon, ahanzarce
Mamy ta bita cikin damuwa ta fara bata hakuri, tare da tabbatar mata Ridwan
baya cin abincin Gidan, da wannan bayanan ne 🔥ta sauko tare da cin
alwashin kullum zata ringa zuwa sanya masa magani na kwana bakwai daga nan shi
ke nan babu shi babu Aure sai dai a lahira. Mamy taji dadin hakan daga gare ta
inda suka dawo falon tare da ci gaba da tattaunawa.
Cotonou
Ranar Alhamis
Yasmin tsaf ta gama harhada
kayayyakinsu domin zama acikin shirin ko ta kwana, Fauziyya da Safiyya da
Firdaus ko wannen su ya zabga uban tagumi, cikin karfin hali Fauziyya ta fesar
da numfashi cike da bakin ciki ta ce" ai yaran Alkali sune suke kawo
sammaci daga kotu ya akayi Dsp ne ya kawo bayan ba huruminsa ba ne?". ta
yi tambaya cikin tsananin bacin rai.
" Ai abu in akace babu Allah
aciki ko meye ai zaka gani, sun wakilci yaron Alkalin ne dan su zo su ganewa
idanunsu ya muke ciki ". Cewar Safiyya tana hura.
" Ni fa tunda abun ya kai ga
haka wallahi banki inci Uban Alhaji Isah ba, haba ! ga abun magana ace ba za muyi
ba, kuma wallahi ko da bashi ne sai mun harhada mun dauki lauya mu ma ". Cewar
Firdaus cikin fada.
Fauziyya ta amshi zancen da fadin " ai
dole mu dau lauya, in ba haka ba cutar zata yi yawa kusan shekara goma be tare
da Mamy shi be sake ta kuma yana kiran mu shegu ze fada mana ta inda aka same
mu ". ta yi magana cikin fusata.
Duk hirar da suke Mamy da Kakarsu Mariya suna
jin su babu wanda ya tanka musu domin, su kansu kukan zuci suke daga zaunen.
Yasmin da yanzu taga zata iya
tofa bakinta cikin maganar cikin muryan kuka ta ce " wallahi ankara kawo
mana wani takardan sammaci daga yaron Alkali cewar sa ranar monday za'a fara
zaman kotu ". Ta kai karshen zancen a raunace.
Gabakidaya zazzare idanu suka yi
har da kaka Mariya, cikin kuka kaka Mariya ta ce " Ni na dauki cikin Isah
har tsawon wata tara da kwana tara, na shayar dashi, na ci kashin sa da
fitsarinsa, in har ina hakkin akansa ya zama dole na masa baki ". Juya
kwayar idanunta ta yi zuwa sama alamun za ta yi mummunar furuci akansa. ta ci
gaba da fadin " Isah kamar yanda kasani kuka kasa iyalinka da yayayenka
kuka ya Allah ya. . . . . . . ". Cikinsauri Mamy tasa tafin hannunta ta
rufe mata baki, cikin kuka take girgiza kai baki na rawa ta ce" kar ki
tsine masa wallahi ze kara lalacewa, wallahi inason Isah, kuma nasan kinfini
sonsa, sai de ni da ke mun tsani halayayyensa, Isah mutum ne da nasani mai
tausayi da jinkai, nayi imani inhar Isah na ne wallahi ko da yaran nan nazo
Gidan nan ze rike min su, amma shedan ya masa kidan ganga baya ji baya
gani". ta karshen cikin kuka.
Kaka Mariya kuka take harda
shidewa, murya na rawa ta ce " A'isha ki barshi ya kara lalacewa kuma ni
Mariya na ce Isah sai kagani". Ta kai karshen zancen a raunace tana jin
komi zata iya masa.
dan kullum da bakin ciki suke
kwana suke tashi.
Shigowar me Gadi da waya ne da
sallama a bakinsa ya sa sunyi shiru, tare da basa amsa cikin kasa da murya, tashi
Yasmin ta yi dan amsar waya daga hannunsa, dan ta san be wuce Umar ne ke kira, tana
karba cikin hanzari ta bawa Mamy wayar tare da gayamata me kiran nata.
Murya a raunace Mamy ta fashe da
kuka ya yin da ta kai wayar saitin kunnenta domin bawa Umar labarin halin da
ake ciki domin yanzu tafi buƙatar ganin ya dawo gida.
Cen Ɓangaren Basma.
Zaune take bakin gadonta Alhaji
Isah na gefen ta yana harhada wasu takardun aikinsa, cikin fara da sakin fuska
ya ce " Basma ga wannan takardan na baki mallakar gidana da ke unguwar Gbegamey
dan nasan yanda kike son gidan nan ". Ya yi furuci cike da begenta.
Cike da tsananin jin dadi ta ce
" tu es sûr? ma'ana ka tabbatar, ya bata amsa da " oui ma
chérie". Ma'ana kwarai kuwa masoyiyata. cikin jin dadi ta kai masa kiss a
goshi, sannan cikin iya bariki ta ce " kai de dan Albarka ne wallahi ga
shi Allah na fiddaka tsakiyan makiya, kuma ranar monday hummm A'isha zata gane
illah cin amanar miji". Ta kai karshen zancen cikin yatsine fuska.
Kallonta yake kamar me nazarinta,
sannan ya yi dan jim kamar yana son fadin wani abu ko tuno da wani abu da yake
ta mancewa tsawon rayuwarsa, hakanan ya ji be ji dadin furucinta ba, a fili
kuma ya ce " Hummm kedai Allah ya kaimu kowa ma ya huta. Dan ni da A'isha
kotu ce zata raba.
Cikin yauki ta kara narkewa
jikinsa har takardunsa suka fadi kasa reras, idanunta masu wutar fitina ta
sauke cikin nasa suna kallon juna, murya cike da shagwaba ta ce " wai
yaushe zaka saki A'isha ne, na ga babu Aure tsakanin nagari da mugu da".
ta yi furucin tana cunno baki gaba.
Bakin nata yake bi da kallo, nan
da nan yaji kalmar sakin ta soke shi har kasar zuciyarsa, ta maza ya yi tare da
fadin " Basma bana son firan A'ishah pls maganar saki a barta sai nan gaba,
zan mata har saki uku". Ya karashe zancen yana juya yin kalamanta.
Ita kuwa ranta babu dadi amma
kuma ta dau alwashin nan gaba shi ne ze zo mata da maganar ya saki A'isha ta
karashe tunaninta tana yar dariya.
Gwarinfa
Kashe gari Ranar Juma'a.
Da sanyi safiya Amatullah ta fito
daga dakinta, tana sanye cikinsabuwar dinkinta doguwar riga atamfa da ya zauna
mata daram ajikinta har shap dinta da hip dinta duk suka bayyana, sosai dinkin
ya mata kyau wanda ya kara mai da babban yarinya, Hasina ta dinka mata bisa ga
umarnin karfin Iko. Cikin gidan har teloli gare su da kasuwa masu siyar da
kayan miya, su atamfa leshi, harda gareji akwai cikin gidan, sauran kuwa ba'a
cewa komi.
Yau ne karo na farko da Amatullah
ta sanya kafafunta a farfajiyar Gidan, cikin zallan mamaki take kallon yanda
gidan yake ci kamar kasuwa, kuma sam babu hayaniya kowa harkan gabansa yake, sautin
zazzakar murya a nan karatun Alkur'ani mai girma, ta ji daga dayan bangare na
Gidan, hakan ya sanya ta fara bin inda take jiyo karatun ahankali tana tafiya
bakinta na dan motsawa kamar duk abin da yake karantowa ita ma tana maimaita
shi abakinta. Sai da ta iso gab da madaidacin massalaci me kyaun haduwa da
tsaruwa cikin zallan mamaki ta ce " massalaci acikin gida? ganin babu me
bata amsa ya sa ta yin shiru, barin wannan tunanin ta yi ta fara ci gaba da
tafiya, har ta iso inda karantun ke tashi, jin muryan dalibai yan amshi na
tashi, kusantowarta wurin yana dai-dai da tsananta bugawar zuciyarta, ahankali
ta matso kofar massalacin tare da da lekawa domin ganin abin da ake. Zararan
idanunn ta ware a kan fari kyakkyawan dattijo da ya tankwashe kafafunsa yana
sanye cikin farar jallabiya fuskarsa ɗauke
da gilashi, cikin kaduwa da al'ajab take masa kallon kamar ta taɓa ganin fuskar sa, muryan
dalibai ne daga ciki ya katse mata tunani tana jin daga ciki wata daliba tana
fadin " Malam ya hukuncin wanda ya labe yana gulma bayan ba'a san da
zamansa a wurin ba, ina nufin yana son yaji kwaf". ta yi tambaya yanda
kasan sako ta aikawa Amatullah.
Amatullah zazzare idanu ta yi tana
nazarin wannan tambayar anya be da hadi da ita kuwa?, wata zuciyar ta raya mata
ai karatunsu suke ba su san da zamanki ba, fesar da numfashi ta yi tare da
yunkurin komawa cikin gidan, muryan Malam ne ya dakatar da ita, jin yana fadin
" gulma ba shi da kyau da yawan gulmace gulmace ake koyon munafunci, sannan
akwai gulma mai fa'ida irin mutum ya zo wuce wa yaga ana karatu sai ya tsaya
dan ya saurara domin ya amfana, na shi akwai lada kam a wajen Ubangiji '
wallahu Ahlam". Ya bada amsa yana mai cigaba da karatunsa.
Sanyayar ajiyar zuciya Amatullah
ta sauke jin amsar da ya bayar.
Tana ganin ana ƙoƙarin
tashi ne ya sa ta fara yunkurin barin wurin har ta karya kwana zata fice, taji
sautin muryan Malam daga sama yana fadin " dakata ". Ya yi furucin
yana mai kusanto inda take cikin kasaita da kamalarsa, innalilahi wa'inna
ilairajun ". Ya shiga maimaita da bakinsa, kana cikin rawar murya ya ce. .
. . . . .
Makauniyar Shari'a taku ce
Comment and share
[10/23, 5:37 PM] Kyauta Daga
Allah: Makauniyar Shari'a
Sai a Lahira
Na
IKILIMA ADAM
(Kyauta daga Allah)
09069080725 whsap
SHAFI NA SHA BIYAR
Kana cikin rawar murya ya ce
dakata Baiwar Allah ". Furucinsa ya yi dai-dai da tsayuwarta. Karasowa gab
da ita ya yi yana ƙoƙarin ganin ta juyo dan babu abin da yake bukata sama da yaga
fuskarta.
Ita kuwa daga tsayen take ji wani
irin faduwar gaba mai karfi, a hankali ta juyo domin ganin wanda ya tsayar da
ita, kwalalo idanu ta yi ganin Malam ne wanda ta gani yana koyar da karatu, cikin
rudewa take kallon kyakkyawan dattijon fari sol wanda yake nuni da a
kuruciyarsa ya yi tashen kyau, bangare daya na zuciyarta tana hasaso mata
kamanninsa kamar ta taɓa
ganinsa ko a hoto ko kuma a mafarkinta.
Malam ganin ta tsura masa idanu
ta shiga duniyar tunani ne ya sa shi katsee mata hanzari ta hanyar fadin.
" Yan mata ya sunanki? Kuma
tun yaushe kike Gidan nan, me ya sa kika labe kina jin karatu bayan kinada
damar shigowa daga ciki ". Ya kai karshen zancen yana jin zuciyarsa na
tsinkewa abun da yake son tabbatarwa ya gani da idanunsa, hawaye ne suka samun
daman cika a idanunsa, cikin hanzari ya sa tissu ya dan goge hawayen ba tare da
ya bari Amatullah ta fahimci halin da yake ciki ba.
Rau rau da idanu take kallon sa
rasa amsar da zata basa ya sa ta fadin " a yi hakuri Malam daga yanzu zan
fara zuwa karatu dan banyi nisa sosai ba ". Ta karshe zancen cikin cool
voice dinta.
Shi kuwa sosai ya shagala da kallonta cikin
boye abin da ke kasar zuciyarsa ya ce " baki fadamin sunanki ba".
" Suna na Amatullah amma
ainahin sunana Faridat, yan kauye na kirana da yar wahala". Ta karashe
zancen cikin tsantsar kuruciya.
" Innalilahi wa'inna
ilairajun ". Malam ya shiga maimaitawa ba kakkautawa hakan ya sa Amatullah,
dan tsoracewa har ta fara tunanin ko duka ze mata ne, ahanzarce tabar wurin ta
shige sashin su, ta bar shi a nan tsaye.
Shi kuwa yana ganin ta fice ya
lallaba ya samu wuri daga nan gefe dakali ya zauna babu abin da kwanyar kansa
ke juyawa sai kalaman Amatullah.
Amatullah tana karasawa daga
cikin falon, cikin rudewa taga Ƙarfin Iko zaune a kan kujerar falo ya
daura kafafunsa daya kan daya yana kallon tashar Tauraruwa in da ake sanarwa da
neman agaji a kan wani yaron kauyen wanda rai yake hannun Allah, sakamakon
bugawar da yan daba suka masa. Amatullah cikinsanda sanda ta karaso falon murya
na ta rintsina gabansa.
Ina wuni! Abba ". ta yi furucin
idanunta na kan TV da yake kallo ba tare da ta jira amsar sa ta tashi tsaye
cikin kidima take kallon Salim a cikin TV shida iyayensa yanda suke kuka suna
neman taimako Naira miliyan Biyar domin fitar da salim kasar waje. Cikin
gigicewa da fitar hayyaci ta ce " innalilahi wa'inna ilairajun Salim
dinannnn". Yanda ta yi furucinne ya sa karfin iko dawo da kallonsa akanta
cikin zallan kaduwa da kalamanta.
Duka hanayyenta ta daura akai ya
yin da take kallon Salim a cikin TV yanda ya rame ya kare baka ganin komai nasa
sai kasusuwa ma'ana ya koma kamar skeleto. Cigaba da jero salati take tana kuka
kasa kasa idanunta cike da hawaye masu dumi. Ƙoƙarin barin falon take izuwa dakinta, taji
daga cikin TV ana fadin dan Allah ataimaka ma wannan yaron dan rayuwarsa tana
cikin hatsari, ga Mai buƙatar taimaka masa ya zo Asibitin Aminu Kano". Tana jin
karshen zancen ta fara sauri sauri wajen yin sashinta. Azafafe taji ƙarfin
iko ya rike hannunta wanda ya yi sanadiyar juyowarta ba shiri, yanda ya rike
hannun nata take kallo da kuma yanda ya tsareta da idanunsa masu kwarjini. Dago
kai ta yi tana kallonsa, cikinsassaita nutsuwa ta ce " ka sake min hannuna
wlh rikon da kamin akwai zafi". Ta magana cikinsanyin murya. .
Kyawawa fuskarta yake karewa
kallo na tsanaki, kana cikin damuwa kasar zuciyar, saman fuskar ba yabo ba
fallasa ya ce " waye salim? meye alakar ku kuma me ya sa kike masa kuka, me
ya sa za ki ambaci Salim dinki a gabana, Amatullah kinsan me kike fadi kuwa
ayanzu fa kin kama hanyar zama budurwa kuma wanda ze aure ki kike yabon wani
agabansa". Ya karashe zancen yana hura kofar hancinsa.
Ita kuwa hannayen da ya sa ki
take kallon yanda ya yi ja, bata kara yarda sun hada idanu ba kanta a kasa ta
ce " Salim yace inna girma ze zauna damu ya gina min gida ni da papy".
Tana kai karshen wannan zancen Ƙarfin Iko rintse idanunsa ya yi da karfi
domin sosai yaji tsananin kishinsa ya motsa.
Taci gaba da fadin " shi ne
wanda ya taimaka muna Lokacin da aka nemi aka kashemu, dole nayi kuka domin ina
tabbacin wannan halin da yake ciki saboda mu ne, kuma bakina ni da papy baze
iya fadin Alkhairan da Salim ya mana, dole nayi kuka yana cikin wani hali ban
da ikon taimaka masa ". Ta karashe zancen tana mai jin tsayuwar ta isheta.
" Zan bada millon goma a
masa magani, ki saurareni zuwa gobe, amma a daren yau zan kawo kudin su kwana
adakin ki ". Ya yi furucin yana mai jin tsananin kishinta, amma kuma yana
son taimakawa Salim kodan ya faranta mata rai.
Amatullah bata tsorata jin ze
bada kudin ba dan ta san yana kudin da ba suda iyaka yanda ta samu labari gun
Hasina, murmushi mai sanyi ta yi wanda yakara bayyana zallan kyawunta, cikin
jin dadi ta fara masa godiya shi kam hakan da ya ganta ba karamin sanyasa cikin
nishadi ya yi ba.
Bayan magrib
Amatullah zaune a tsakiyar
dakinta muraja'a take yi na karatun da Papy yake koyar da ita na surori.
Shigowar Hasina hannunta ɗauke da jaka ne ya sa ta
kai dubanta akanta tana sanye cikin doguwar riga mai tsantsi baki tare da bakin
hula akanta, cikin jin dadi ta kai ayar karatun ta tare da mata sannu da zuwa
cikin fara'a. Hasina ta ce.
" Amatullah yar gatan Haruna
karatu ake?".
"Eh karatu nake, kuma nakai
aya". Cewar Amatullah.
" Ma sha Allah, Allah ya
bada lada ".
" Ameen Nagode sosai". Fuska
ɗauke da yalwatccen
murmushi.
Numfashi Hasina ta fesar tana
karewa Amatullah kallo na musamman kana cikin muryanta ta dabi'a ce ta ce
" muga kitson da Nana ta miki, sannan ga sako Haruna yace in kawo miki
zakuyi Magana". Ta karashe zancen tana mai kallon kitson kan Amatullah
data bude mata cikin hanzari ta furta.
"Ma sha Allah".
" Nagode kwarai ". Ta
kai karshen zancen tana mai amsar jakar daga hannun ta.
Sun shagala suna hira tsakaninsu
wanda har ya sa Amatullah darawa dan sosai Hasina ke ɗebe mata kewar Papy.
. . . . . . . . . . . . . . . . .
. . . . . . . . . . . . . . . .
Umar Faruk bakin sa na rawa yaje
gun mai gidansa tare da fada masa buƙatarsa na son tafiya garinsu, Alhajin ya
tausaya masa matuka hakan ya sa ya ba shi kudin mota tare da fadin " in
komai ya daidaita dan Allah ya dawo ze kama masa aiki a kamfaninsa. Sosai Umar
yaji dadin hakan ya kuma masa godiya tare da zama a cikin shirin gobe asabar ze
bar garin. .
Ridwan sosai yake shiri bayan
Sallah isha'i yanda kasan ze je wurin shakatawa, wandon treequater ya sanya
tare da brown din rigarsa cotton, mai daukar idanu, anutse tattare da kamalarsa
ya gama shirinsa tsaf, gaban mirror yaje yana taje kansa kana cikin hanzarinsa
ya fesa turaruka masu kamshi ajikinsa ta cikin madubi yake kallon kansa shi
kansa ya san ya yi kyau, jin wayarsa na rîng ne ya sa shi hanzarta sanya flat
din takalminsa hade da fita domin ya san be wuce Mansur ne. . .
Cikinsassarfa yake taka matakalan
step din, wanda ya jawo hankalin dukan kannensa da suke falon kallon sa, yana
saukowa ya yi dai-dai da fitowar Mamy ita da Madina da idanu suke binsa ganin
yana gaisawa da kannensa, kana ya tsaya su na dan taba hira da kaninsa Faisal
tare da fada masa ya shirya gobe tare da za su fara fita aiki. Kannensa mata
kuwa bayan gaisuwa be kara ce dasu komai ba. Ƙoƙarin ficewa yake daga falon ya ji murya
Madina tana fadin " Haba Ridwan baka ganmu ba ne". Cak ya tsaya ba
tare da ya waigo ba, cikin kasa da murya ya ce sannunku da fitowa iyayena
". Tare da fara yunkurin fita falon.
Murya Madina yaji again tana
fadin " na ga kamar sauri kake dan Allah ka saukeni gida, motata ta
lalace". ta yi magana cikin jiran amsa.
Cak ya tsaya yana nazarin
kalamanta kana cikin muryansa ta dabi'a ya ce " zan baki kudin Napep zan
baiwa me Gadi ya baki, dan ba hanyarmu daya ba". Yana kai karshen zancen
ya fice daga falon.
Da idanu suke bin keyarsa da
kallo daga su har kannensa, Faisal ne ya yi murmushi domin ba karamin burgesa
takun Ridwan yake ba.
Madina rike da baki suke kallon
juna da Mamy, kana cikin hanzarinta ta ce " Mamy bari nabi sahunsa nasan
ma ze saukeni". ta yi furucin tare da fita ba tare da ta jira amsa ba.
Su Anisa me za suyi in ba dariya
ba, ita kuwa Mamy ta fara tsorata da Lamarin Madina a kan Ridwan kasa magana ta
yi hakan ya sa ta samu wuri ta zauna cikin ya'yanta.
Madina tana karasowa ya yi daidai
da kunna wutar motarsa ze fice daga Gidan, hannun da take masa ne ya bashi
damar danna madanni sauke gilashin motar, kana ya dawo da kallonsa a kan ta jin
tana fadin " Dan Allah Ridwan ka sauke ni diyar antina ce ba lafiya kafin
na samu napep da aiki ". Ta karashe zancen cikin magiya ".
Kallonta yake tuno da ai ita ma
kamar Uwarsa take hakan ya sa ya ce " to shiga kofar baya ".
" Haba dana kai ba drever ba
gwamma in zauna gaban zefi ". Ba ta jira cewarsa ta shige ta gaban motar, tare
da cika kujerar da manyan mazaunata.
.
Ya kai mintuna biyu be tada motar
ba lissafi da nazarin matar yake, barin wannan tunanin ya yi tare da tada
motarsa, daman ya san Gidanta a lugwai yake hakan ya sa be tambaye ta kai tsaye
ya fita da hancin motar daga cikin gidan.
Sun sha tafiya da ya kai akalla
minti ashirin, wayarsa ta hau ruri yana dubawa yaga Mansur ne daga wayar ya yi
yana mai cigaba da tukinsa cikin kasa da murya ya ce" Mansur ina hanya zan
ajiye Mamata Madina Gida ne, ka jirani ina nan zuwa ka ce wa Mama pls aidole
inzo cin abinci". Ya karashe zancen tare da katse wayar.
Madina sosai ranta ya ba ce jin
ya ce mata Mama, cikin boye damuwar ta kakalo murmushin dole tare da fadin
" wai kai yaushe zaka yi Aure ne Ridwan?". ta yi magana domin ta san
amsarsa be wuce baya son jin zancen aure kamar yanda ya saba.
Cikin tsantsan mamaki da rudewar
tunani a bazata ta ji ya furta.
" Ai na kusa Aure kwanan nan,
baki ga na fara gyaran dayan sashin cikin gidanmu ba to a nan zata zauna
Amarya". Ya yi furucinsa cikin tabbatarwa.
Zazzare idanu Madina ta yi ƙoƙarin
yin magana take, taji yana fadin " mun fa iso". Ya yi furucin yana
mai nuna mata da jiransa ake.
Jiki a sanyaye ta sauka tare da
rufo kofar, muryanta na rawa ta ce " Rid Nagode Allah ya maka Albarka
".
Be bata amsa da Ameen ba sai dai yabita
da kalmar sai anjima. Daga haka yafice daga unguwar.
Ita kuwa cikin hanzarinta ta
karasa gida tana mai jin takaicin tambayar da ta masa tana kuma rantsewa da
buwayar Ubangiji sai ta Auri Ridwan ko ana ha maza Ha Mata.
Rid mintina sha biyar ya dauka
kafin ya isa Unguwar su Mansur, me Gadi na ganin motarsa ahanzarce ya wangale
masa babban gate din Gidan.
Cusa hancin motar ya yi yana mai
daga mai Gadi hannu, tare da zarcewa farfajiyar Gidan.
Parking space ya ajiye motar, fitarsa
daga motar ya yi dai-dai da karasowar Mansur shi ma irin shigar Ridwan din ya
yi komi irin daya, murmushi kwance a fuskokinsu suka kama hannayen juna, bakin
Mansur na rawa ya ce " kai Abokina har gida kaje kai kawar Mamarka ka
barni da jiranka gashi ina jin yunwa".
" Wallahi matar ce ta cika
naci ".
" To ai ita ma Mamarka ce
dole ta yi iko dakai ".
" Hummm ni karshe ma saida tasa na fadi abin
da bashi ne ba".
" Ahaf ka ce kayi kwaba tunda kasan karya
ba dabi'arka ba ce Lallai ka tabbatar kayi abin da ka fada mata ". Ya
karashe zancen suna mai karasowa falon kusan a tare.
Suna isa falon ya yi tozali da
Mansura da ke sanye cikin doguwar riga atamfa ba karamin kyau ta yi da shigarba.
Cikinsakin fuska da walwala take
fadin " oyoyo yaya Ridwan har ka iso". Furucinta ya yi dai-dai da
fitowar Mama cikin riga da zani atamfa Mai kalan ruwan kasa.
Ita ma da murmushi take fadin.
" Lale marhaba da Dana
". Murmushi ya sakar musu dukansu yana mai cigaba da tafiya izuwa
kayataccen falon, cike da ban girma ya gaishe da Mama kana cikin dan sakin
fuska yake amsa gaisuwar Mansura.
Bayan taba yar hira da Mama ne yake fada mata
Aure zeyi cikinsatin nan kuma sha'awar yin Aure ya zo masa ne a daren. ".
Mansura da ke ƙoƙarin
shan lemun acikin kofin glass ba tare da ta ankare ba ta saki glass din ya fadi
saman tayis jika kake. . . . . . . . . . . . . .
Makauniyar Shari'a taku ce
Share and comment pls
[10/23, 5:37 PM] Kyauta Daga
Allah: Makauniyar Shari'a
Sai a lahira
09069080725
SHAFI NA SHA SHIDA
Ta saki glass ɗin saman tayis kas kas ya
tarwatse a kasa, "subuhannallah" ta furta cikin zazzare idanu tana
kallon yanda kofin ya tarwatse, cikin kidima ta dago kai tare da kai dubanta a
kan Ridwan shi da Mansur har da Mama, kowannensu kallon Al'ajab yake mata.
" Hummm am sorry wallahi ban
kula ba ne bansan yanda akayi ya subce daga hannuna ba " ta yi magana
murya kasa kasa kamar me shirin yin kuka.
Ridwan kar kada kai ya yi cike da
kulawa tare da fadin " ba dai ki ji ciwo ba ko? " girgiza kai ta yi alamun
a'a cikin kasala rashin kuzari da tsananin faduwar gaba, kama hanya gun dauko
tsintsiya da mopper tayi. Da idanu yake bin ta da kallo, ganin yanda take
tafiya kamar wacce kwai ya fashewa a ciki, mai da kallonsa a kan su Mansur ya
yi tare da zama kan dîner table din, cike da jin dadi yake kallon tulin abincin
da Mansur ya cika masa a plate, sosai ransa ya biya ganin tuwon shinkafa miyar
taushe da naman rago, kamshi abinci sosai ya daki hancinsa cikin yanayinsa na
walwala yake kallon Mansur da shi ma din shi yake kallo cike da burgewa da dan
guntun murmushinsa ya ce " wannan abincin na mu uku ne ko? ".
" Ina ce kaga nawa nima a gaba". cewar
Mansur yana dariya.
" Haba Mansur kasan duk sona da abinci
bazan iya cinye shi ba, bata abinci kuma ba shi da kyau".
" in ka rage akwai wacce zata ci
sauran".
Danpp jim ya yi alamun tunani kafin ya dau
cokali pme yatsu ya fara kai lallausan tuwo a bakinsa, dadin abincin pyasa ko
kara kallon Mansur beyi ba ya fara ci cike da nutsuwa.
pp
P Mansura bayan gama mopper dan
gefe ta samu ta labe tana kallon yanda yake cin abinci, jajayen labbansa ba
karamin rikitata suke ba. Mama data fito cikin corrido da mamaki take kallon
Mansura na leke, guntun murmushi ta yi kana ta karaso tare da tsayawa bayanta
ita ma tare da kai dubanta an yi a kan abunda take kallo, ga mamakin ta Ridwan
ta gani, murya a sanyaye tare da yin kasa da murya ta ce " haba Mansura
yanzu in ya ganki kina masa wannan kallon ai sai ya daina zuwa cin abinci gidan
nan pls banason hakan ". ta yi magana cikin bacin rai.
A furgice Mansura ta waigo tana sauke ajiyar
zuciya, cike da jin kunya ta ce " Hummm ai ba shi nake kallo ba ". Ta
karasa zancen tare da fita tsakar gidan, domin jiran fitowarsa.
Da idanu Mama ta rakata tana girgiza kai.
Bayan kammala cin abinci, sun sha lemuka ba
laifi kana Ridwan ya fara shirin yiwa su Mama sallama tare da fada mata ta
shirya cikin watan nan zata je Umra. Mama ba karamin farin ciki ta yi ba, gefe
daya kuma sai ta bata rai kamar ba abun Alkhairi ya mata ba, cikin bayyanar
damuwar fuskarta ta ce " Rid Nagode kwarai da dawainiyaya da kake dani
Allah ya saka maka da Alkhairi, sai de Ridwan bazan ji dadi ba ace Mahaifiyarka
wacce ta haifeka ko Umra bata taɓa
zuwa ba, ni kam nayi hajji ya kai hudu, Umra ba iyaka, pls ka tai. . . . . . .
. . . . ".
" Dakata ". Shi ne farkon abin da ya
furta kana cike da jin zafi tuno masa da Mamy ya ce.
" Mamy Mahaifiya ce, kunsan an ce Hajji
kiran Allah ne, ina ga Allah ne be kirata ba " ya kai karshen zance tare
da ficewa domin baya son ta kara yin wata magana da zesa ta ga rauninsa.
Daga Mansur Har Mama da idanu suka raka shi, kana
Mansur cikin kasa da murya ya ce " Mama pls dan Allah ki kyale Rid tunda
baya so a masa maganar Mamy, yana da ilimi addini dana zamani, kuma an ce ruwa
baya tsami banza ke dai mu dage da saka shi cikin addu'a ze fi ". Ya
karasa zancen tare da bin sahun Ridwan din.
Mama kam shiru ta yi tana kallon fitar Mansur.
Ko da ya isa compound din gidan Hango Ridwan
ya yi shi da Mansura tsaye jingine a jikin motarsa da dukan alamu magana suke a
yanda ya hango Ridwan na magana ya tabbatar magana yake mai cike da damuwa, jan
burki ya yi tare da samun wuri daga gefe ya zauna yana jiran Mansura ta bar
wurin.
Mansura cikin murya kuka ta ce " Ridwan
zan fada maka sirrin zuciyata wallahi ina sonka tun ranar dana yi wayau nasan
kaina dan Allah ka kaunaceni kar ka ce mun nayi hakuri ".
Ridwan in ransa ya yi dubu ya baci daman
wannan kalmar zata fada masa tun dazu take ta jan zancen da tsawo.
Kallo daya ya mata cikin kasa da murya ya ce
" ni kam koda kika ji nace zanyi aure Yar Daji zan aura banason wayayyiyar
mace, kuma Nagode da kulawa". Yana kai aya, ya fara neman Mansur da idanu,
hangosa ya yi yana tahowa, ita kuwa Mansura aguje ta bar wajen tana rusa kuka
mai cin rai, domin kuwa ta tabbatar samun Rid ba abu me sauki ba ne.
Mansur na karasowa babu bata lokaci shi ma ya
shiga tashi motar domin masa rakiya rabin hanya.
Benin République
Yau takama ranar Litinin inda a
yau ne Alkali ze fara sauraron kararraki da ya shafi Isah Sharifai da
Uwargidansa A'isha Muhammad.
Tun safe kowa ya shirya daga
Fauziyya, Firdaus Safiyya, hatta Yasmin duk sun shirya tsaf, Kaka Mariya tana
sanye cikin kodaddiyar atamfarta, kowannen su fuska babu walwala, cike da
damuwa Mamy ta ce " wai ko ya labarin Umar ne anya kuwa ya taso kuwa haba
ai ya kamata ace ya karaso? " ta yi furucin cin damuwa.
Fauziyya cikin kwantar mata da
hankali ta ce " yanzu haka be samu damar tasowa ba ne, kawai a kyaleshi
Allah sheda ne baya garine shiyasa be samu zaman kotu ba. Kokan ta gama rufe
baki wayarta ce ta fara ruri inda wakar Hamisu breker ke tashi waka mai taken ku dakata makiyan mu bayanzu, mai son ganin
bayan mu ba yanzu ba ahanzarce ta daga ganin number Nigeria ce ta san be wuce
Umar, cike da zalla mamaki da Al'ajab taji dan sanda na fadin " Umar yana
heatquater na yan sanda bisa babban case da aka dade ana nemansa shekara da
shekaru dan haka duk sanda kuka shirya kuna iya tahowa Abujan". Dan sanda
na gama magana ya katse wayar.
Dagacen kallon Umar Yake yanda yake kuka mai
cin rai, murya na rawa ya ce " yace wallahi ko tsuntsun ban taba kashewa
ba bare mutum dan Allah ku fahimceni iyayena suna bukatata a dai dai wannan
lokacin " ya kai karshen zancen yana kuka mai tada hankali.
Yan sanda ko ajikinsu kowannensu
babu wanda yakara bi ta kansa.
Dagacen bangaren su Fauziyya
Innalilahi wa'inna ilairajun suke ta maimaitawa cikin tashin hankali Fauziyya
ta ba su labari, nan dakin ya dau salati, cikin tsananin tashin hankali Mamy ta
ce " Fauziyya dan Allah kubani poison in sha na mutu, kila in samu sauki a
cikin zuciyata ". Ta karashe zancen tana kuka.
Dukan su kuka suke, Yasmin cikin
kukan da ya ci karfinta ta ce " Mamy wai mu kaɗai ne muke rayuwa cikin kunci ne?" ta yi furucin
murya a raunace, babu wanda ya bata amsa a cikin su kowannensu da idanu suka
bita ganin lokacin na gab da karantowa ya sa suka tashi domin tafiya kotun, Mamy
da taimakon Fauziya take tafiya domin saida ta tallafeta ajikinta tana kuka
kasa kasa.
Ɓangaren Alhaji Isah shi da Basma da
ya'yanta sun shirya tsaf cikin fararen shadda gezner kowannen su sosai dinki ya
masu kyau da cikar haiba, cike da jin dadi da walwala suka fito harabar gidan, kokan
su karaso har su Yasmin sun fice.
Basma da mijinta mota daya suka
shiga, ya'yan nasu kuwa a dayan mota suka shiga inda babbar diyar Basma Nasra
ta tuka motar.
Court.
Tun daga sauke su Yasmin a kan mashin
din da ya kawo su suke karewa hadadden court din kallo, cike da fargaba da
tashin hankali, Mamy ke kallon yanda lauyoyi ke kai kawo a wajen wanda yake
nuni da ahanzarce suke domin lokaci na gab da cika.
Soma rarraba idanu suke dukansu
suna neman inda za su ga lauyar su, Yasmin cikin damuwa ta ce " Mamy
kinganta cen tana magana da wani lauya" ta yi magana tana mai nuna Lauyar
da yatsarta. Gabadakiya cike da hanzari suka yi wajen lauyan ganin tana shirin
shigewa filin hall din.
Suna isa wajen ta, cikin damuwa suka zagayeta
tare da soma tambayarta inda za su zauna.
Lauya Hadiza Ibrahin da ke sanye cikin kayan
aikinta, kallonsu take Cikin yanayinta da ke nuni da rashin walwala ta ce
" ku kwantar da hankalinku shi Shari'a da kuke gani sabanin hankali ce, ni
Hadiza Ibrahin zanyi iya ƙoƙarina ganin na kwato maku yancinku". Duk wannan bayanan
da harshen French take yinsa.
Ko ba komai Mamy da ya'yanta sun dan ji
sassauci damuwar su dayan bangaren kuwa hankalinsu ya tafi a kan Umar da ke cen
a tsare. Suna ƙoƙarin shiga hall tare da barister ya yi dai-dai da isowar Basma
da mijinta da ya'yanta harma da yan uwanta. Da idanu suke binsu da kallo tare
da yin gaba suka wuce su.
Kaka Mariya cike da damuwa take
mamakin halin Isah, cikin takaici take fadin " ku shiga daga ciki ko".
Bayan kowa ya shiga an zazzauna, Alhaji
Isah a sace yake kallon A'isha da ita da Mariya, da yaga suna ƙoƙarin
dago Kai sai ya yi wuff ya ɗauke
idanunsa.
Isowar Alkali ya sa gabakidaya
kowa tashi kamar yanda aka saba, Alkali na zama kowa ya zauna. .
Cike da kamala mai gabatarwa ya mike tsaye
file cike a hannunsa da dukan alamun akwai kararraki bayan nasu. Cike da
kamalarsa yake fadin " Barka da zuwa ya mai girma mai Shari'a. Karar farko
da za mu fara shi ne a kan Alhaji Isah sharifai da mai dakinsa A'isha Muhammad,
wacce yake zargin ta haifa masa ya'yan da ba nasa ba, kuma tana zaune masa
acikin gida da daurin gindin Mahaifiyarsa". Yana kai karshen zancen ya kai
file da ya danganci karar gaban Alkali.
Alkali Auwal Hassan dage gilashin
idanunsa ya yi yana mai kallon file din da ke gabansa, kana ya dauka a hannunsa
hakan ya sa mai gabatarwa samun wuri ya zauna.
Alkali cikin daga murya ya ce.
" Lauyan mai kara ya gabatar da
kansa". Yana kai ayar zancen ya yi shiru yana kallon Barister da ya tashi
daga zaune.
Suna na Barister Sani Muhammad, nine
lauyan da ke kara, tare dani akwai. . . . . ".
Tashi Lauyan ta yi da kanta tana mai gyara
wuyar rigarta, cike da girmamawa ta ce " Sunana Shamsiyya Adam, nice
mataimakiyar Barister Sani". Tana gama fadin haka ta zauna.
Alkali sake gyaran murya ya yi
tare da fadin Lauyan me kare wanda ake kara Bismillah.
Barister Hadiza Ibrahim cike da
kamala ta tashi cikin ban girma ta gabatar da kanta tare da abokin aikinta
Mahfouz.
Kotun daukan shiru ya yi na wasu
dakiku, Alkali sake bawa Lauyan me kara dama ya yi domin shigar da korafi.
Cike da kwarin gwiwa Lauyan me
kara ya mike bakinsa na rawa yace " ya mai girma mai Shari'a Alhaji Isah
yana neman a raba shi da wa'yannan ya'yan da ba ta hanyar. . . . . . . . . . .
. . . .
Makauniyar Shari'a
Comment and share please.
***
Littafin nan, na kuɗi ne. Da zaran free page ya kare za ki daina ganin sa. Hanzarta ki biya naki kada a yi babu ke.
Kibiya dari biyar kacal domin samun shiga group na musamman.
Domin Karin bayani a tuntuɓe ni ta wannan lambar 09069080725 ko + 22953726162.
Siyen nagari mai da kuɗi gida.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.