Ya Allah ina godiya da bisa dukan ni'imominka a gareni. Yanda na fara Lafiya ka ba ni ikon gamawa Lafiya. Alkhairan da ke cikinsa ka ba ni ladansa, sharrin da ke ciki ka yafe min.
Allah ka dauka Alkalamin marubuta a duk in da suke
Gaisuwa ta musamman gareku na hannu dama ta.
- Besty (Sarat Alkasum)
- Maman Amatullah
- Ummu shkura
- Fadila Sani Bakori
- Maman Sharifa
- Mamashu
- ABBA Yakubu
- Dan Salma
- Da Autan Jarumai.
Waɗanda ban samu damar kiran sunansu ba, duk ina mika sakon gaisuwata a gare ku.
Yayyena abun Alfaharina
- Hadiza
- Hussaina
- Hassana
- Maryam
Gaisuwa ta mussaman gareki
Anty Zulai, mutan Kano, surukar Auta na.
Jarumai Writers Association, marubuta masu aiki da Jarumta wajen Fadakar da Al'umma
MAKAUNIYAR SHARI'A
IKILIMA ADAM (Kyauta daga Allah)
09069080725 ko +22953726162 (Whatsapp kaɗai ban da kira)
Marubuciyar da ta nishaɗantar da ku a littattafanta kamar haka:
- Kai ka ja wa kanka
- Kanwata
- RAI DAYA (Jan Za ki)
- RUDANI (mai tafiya daukan rai)
Da sauran su.
Yanzu ga ni ɗauke da sabon littafina mai suna MAKAUNIYAR SHARI'A
*******
SHAFI NA TAKWAS
Bayan rigarsa suke kallo, inda yaga
an rubuta MASTER da babban baki, nan da nan hantar cikinsa ya kada wani irin
gumi mai dumi ya ringa sassarfo masa dukan ilahirin jikinsa, ji kake gab!!
gab!! da karfi.
Ahankali mutumin da ya ba su baya ya waigo
yana busan sigari da tashin hayaki, cikin isa da kasaita ya ke taku irin na yan
daba hannunsa daya sanye cikin Aljihun rigarsa. Cikin razana Amatullah ke
kallon fuskarsa a rikice da tsoro, ta fara ja da baya baya, bakinta na rawa ta
ce, " kaine?".
Be bata amsa ba illah cigaba da
takunsa ya yi yana nufo inda suke yaransa suna cigaba da bashi hanya har ya
karaso daf dasu, cikin tsananin bacin rai da ya bayyana a fuskarsa ya ce, "
Ina zaku tafi da sanyin asubahin nan? baku san tun lokacin da nasan kuna zaune
a nan wurin na fara gadin ku ba? saboda bana son abin da ze taba min Yarinyar
nan, akanta zan iya yin komai. " Ya kai karshen zancen yana kallon Papy da
ya dukar da kansa idanunsa a kasa. Kara zuko sigarin ya yi tare da turnuke su
da hayaki, silan haka ya sa Amatullah kwarewa har numfashin ta na tsarkewa, nan
da nan ta fara tari tana yi tana bubbuga kafafunta sosai hayakin ya shiga hudar
hancinta ya hau kanta tare da haddasa mata ciwon kai lokaci daya. Papy lura da
yanayin da Amatullah take ciki hakan ya sa ya ajiye kayan hannunsa, hanzarta
karban kayan da ke hannunta ya yi tare da ajiye su akasa. Kana janyo ta tare da
kai mata wawan runguma da ke nuna tausayi da jin kai na Mahaifi, hannayensa ya
sa yana mai dan bubbuga bayanta. Duk abin da suke Karfin Iko na kallon su shi
da mabiya bayansa da suke sanye cikin face mask.
"Zan canza muku wajen zama in kama muku
haya acikin gari". Cewar Karfin Iko yana cigaba da tashin hayakin sa.
" Babu inda za mu bi ka, ka barmu inda ka
ganmu, bana bukatar taimakon ka ". Cewar Amatullah cikin kuka mai gunji, ba
tare da ta dago kanta daga jikin Papy ba. Karfin Iko cak kalamanta suka cika
zuciyarshi da zunzurutun mamaki dan ba zato ba tsammani ya ji amon muryanta
cikin kuka wanda ya kara sanya dukan gabobin jikinsa yin sanyi kamar kankara, kana
yana mai kara kallon yanda take kara shigewa jikin Papynta da ke rungume da ita
yanda kasan sace ta za'a ko raba su. Sanyayyar iska mai kadawa da yanayin
sanyin asubahi ya buso su hade da ni'imattacen shaka. Nan da nan Amatullah ta
kara matse Papy ajikinta dan sam bata son sanyi.
Karfin Iko jefar da Sigarin hannunsa ya yi, ya
take da kafafunsa kana, ya juyo da fuskarsa, yana mai kara kallon su karo na
barkatai, cikin babban muryansa ya ce, " Haba Yarinya kul kada na kara jin
kina fadin in fita daga tsabgarku, hakan babban zunubi ne, maganar bakyason na
canza muku muhalli, to ku zabi in da kuke son zama zan biya kudin haya ". Yana
kai karshen zancen ya fara ƙoƙarin daukar kayan nasu. Papy da sai yanzu yaji ze iya
magantuwa ya ce, " na amince ka samar muna wajen zama amma don Allah kar
ka kama muna daki da kudin haram. " Ya kai karshen zancen yana mai kallon
Karfin Iko cikin idanu.
Gabakidaya wajen sosai har yaran
nasa suke juya kalaman Papy, hatta Amatullah ita ma kam kalamansa ta daura a
ma'auni tana tankade da rairaya amma sam ta kasa gane inda Papy ya dosa. Karfin
Iko murmushi ya yi na gefen baki, kana cikin muryansa na dabi'a ya ce, "
na muku Alkawarin da kudin gadona zan kama muku haya, dan ma garin mu ba Abuja ba
ne da Gida zan baku ku zauna har iya adadin lokacin da kuka bukaci komawa
muhallinku ko in ce Garin ku. " Papy sosai ya ji ya gamsu da Karfin Iko, kallo
daya ya masa ya tabbatar da gaskiya yake fadi har kasan ransa. Kafin su bar
wajen saida ya ba su dubu ashirin kudin cefane, kana ya ba su kwana uku su
zauna ciki shiri za su canza muhalli.
Papy komawa suka yi bukkansu suna
juya kudaden da ke hannunsu, lissafin rayuwa yake hakan ya sa cikin karfin hali
ya ce, " Amatullah ". dago kai ta yi tana kallonsa da idanunta masu
tarin barci, kana ta lumshe su tana mai sauraren me ze fadi. " Ina son ki
sani duk duniya ban da kamarki, kuma ba zan so ganinki cikin damuwa ba, ina son
ki sani rayuwa aduk yanda ka tsinci kanka hakuri ka ke yi, dan haka ina mai
rokon ki Please ko babu ni kar ki jefa kanki cikin halaka ".
Kamar an tsinkaye da Allura, afirgice
ta bude idanunta, tare da dan murza su tana son tabbatar da abin da take ji
daga bakin Papy.
Nan da nan ta nemi barcin da take ji ta rasa, tattaro
kuzarinta ta yi tare da zama tana face dinsa dakyau, damshin hawayene suka cika
kwarmin idanunta, cikin rawar murya da tsoro da fargaba ta ce, " Papy
bangane me kake nufi ba? Kar ka ce zaka guje ni dan Allah bansan kowa ba sai
kai ban taso da uwa ba, ban taso da uba ba, Papy in ka guje min waze jibinci
lamurana?. " Ta kai karshen zancen tana sheshekar kuka.
Dubanta yake cikinsanyin murya da tausayawa da
jin kai ya ce, " Amatullah nasha gayamiki akwai mutuwa kin san mutuwa bata
sallama Amatullah banason ki sawa kanki damuwa aduk lokacin da mutuwa ta yi awon
gaba dani pls my Friday ". ya karashe zancen domin kwantar mata da hankali.
Duk da hakan sam bata ji sassauci ba, bakinta na rawa da tsoro ta ce, " mu
ba mu da dangi ne? ina mahaifiyata Papy? ba mu da yan uwane, mu kaɗai muke rayuwa ne, kuma
kana ta yawan ambato mun zancen mutuwa shin ya kake son na kasance in babu kai?.
" Ta jera masa tambayoyi cikin muryan kuka.
Cak wutar lantarki jikinsa ya ɗauke, nan da nan ya ji zufa
ya keto masa, cikin kasa da murya ya ce, " Amatullah zan miki takarda full
na address din Gidanmu in har kin samu zuwa kawai kice kina son ganin dan Gidan
kawai, kuna tozali da shi kawai ki mika mishi papper, amma sai bayan raina ko
wani abu ya gifta za kiyi hakan, a nan in sha Allah za ki san tarihinki hatta
Mahaifiyarki, batun mutuwa Amatullah ko muna so ko ba mu so tabbas sai ta raba
mu ". Ya karashe zancen yana maganar zuci inda yake fadin " Amatullah
mun kusa rabuwa daman nasan wannan ranar zata zo, Allah ya sa kije gida lafiya,
Amatullah banson barinki adaidai wannan lokacin ba amma tun da na fahimci kin
fara hankali babu sauran zama ni da ke Diyata ". ya kai karshen zancen
yana mai kuka mai cin rai, shi da ita babu mai rarrashin wani domin kukan ya ci
karfinsu.
Benin Cotonou
Alhaji Isah Sharifai, cikin
tsadaddan shaddarsa ya fito compund din Gidansa, hannunsa rike da bakar jaka, ba
karamin haduwa ya yi ba cikin shigar hash color, hular kansa ya tsaya gyarawa
yana mai kallon, Meenat da ke kusanto inda yake murmushi a kyakkyawan fuskarsa.
Ahanzarce ta karaso tana mai rike hannunsa mara ɗauke
da jakar, Yarinya ce wacce bazata wuce shekaru sha bakwai ba, sanye cikin red
habaya mai adon stone hannun riga da tsakiyar riga, ta yi rollin din kanta da
dankwalin rigarta, doguwa ce fara sol dan tana mugun kamannin da mahaifiyarta
Hajiya Basma. Nan da nan ta karya murya cikin cool voice dinta ta ce, "
Daddy ni fa yau so nake naje bikin kawata kuma kudin da ka ba ni, naira million
biyar satin da ya wuce sun kare, pls ka karamun biyar din dan zanyi bajinta a
wajen taron". Ta karshe zancen cikin shagwaba. Alhaji fuskarsa ɗauke da Annuri ya ce, "
Haba daughter in kina son kudi, kawai ki ce na tura miki, kin ga Zahra'u tana
Dubai tana karatu, zanso kema kije. . . . . . ". sauran kalamansa makalewa
su kayi sakamakon ganin, Yasmin cikin shigar makaranta ta fito daga sashinsu, sanye
cikin tsohuwar uniforme mai kalan bleu da fari da jakarta da ta rungume, kafarta
sanye take da da safa cikin takalmin makaranta mai igiya, Yarinya ce me kimanin
shekaru 16 aduniya farace sol zubin larabawa, duk da dushewan fata da ta yi hakan
be hana nunawa ita din fara ce sosai ba. Ɗauke ganinsa a kanta ya yi yana kallon
yanda Meenat ke binta da kallon mamakin ganinta, shi kuwa kauda kansa ya yi ya
fara ƙoƙarin
shigewa daya daga cikin jerun motocinsa, da mamakinsa sai gani ya yi Yasmin ta
bi kusa dashi har sun kalli juna ta ɗauke
idanu bata gaishe shi, bakaramin shock ya shiga ba duk da ya san duk tsawon
shekaru ko baze amsa ba zata gaishe shi, cikin hanzari ya kara kai dubansa
akanta, hango ta ya yi cike da girmamawa take gaishe da Tanimu me Gadi. Meenat
da ke kallonsa tabe baki ta yi cikin siririyar muryanta ta ce, Daddy pls ina
jiran kudin, ka tabbatar ka tura su kafun kafita ". ta kai karshen zancen
tare da barinsa ta yi cikin gida cikin hanzarinta domin kaiwa mominta labari da
dumi duminsa, shi kuwa sai da ya share minti biyar ya tunanin sabon halin
Yasmin, barin tunanin ya yi tare da yin transfert din kudin a account din
Meenat. Ahanzarce ya tada motarsa. Tanimu mai Gadi cikin hanzarinsa ya bude
masa gate, Alhaji na ƙoƙarin fita daga Gidan ya fara jero masa gaisuwa har kasa, amsa
masa ya yi yana mai ƙoƙarin danna hancin motar wajen Gidan, yana fita da hancin
motarsa daga gidan ya hango Yasmin bakin titi alamun napep take nema, tsaida
tukin motarsa ya yi yana kallon yanda take daga hannu wajen tsayar da mashin, tana
yi tana kallon agogon hannunta da dukan alamun hankalinta a tashe yake ganin za
ta yi latti, wata bakar mota ta faka gabanta kallon daya ta yi wa motar ta fara
yunkurin barin wajen, wanda ke cikin motar kyakkyawan matashi ne ajin farko, kallon
daya zaka masa kasan dan hutune, domin agogon da ke hannunsa na diamon ne, kara
binta da motar ya yi yana mai fadin " Baiwar Allah dan, dan Allah bari na
sauke ki makaranta da dukan alamu kin rasa abun hawa ". Ya kai karshen
zancen yana mai ƙoƙarin bude murfin motarsa, ita kuwa kin tanka masa tayi, tare
da samun mashin a daidai lokacin, ba ta jira sunyi ciniki ba ta fada masa
makarantarsu, hawa mashin din ta yi inda suka bar wajen, shi kuwa matashin
murmushi ya yi jin sunan makarantar da zataje, daga haka yaja motarsa ya yi
gaba.
Alhaji Isah Sharifai shi ma tada motarsa ya yi
tare da fara bin sahun Yasmin, har ta iso makarantarsu, tana ƙoƙarin
shiga ya yi daidai da isowarsa makaranta, kallon skul din yake da kyau ganin
ansa Raudat school nan dai ya shiga bin dalibai masu shige da fice a makarantar.
Wani dalibi ya gani, samun kansa ya yi da tsayar dashi ta hanyar kira, tambaya
ya fara masa domin son sanin ajin da Yasmin Isah Sharifai take Cikin zazzare
idanu dalibin ya ce, " Tabb wai Yasmin Sharifai, ai yanzu ta ce adaina
kiranta da Isah sharifai ".
Zazzare idanu Alhaji ya yi
bakinsa na rawa ya ce, "
Wani suna take son a dinga
kiranta da shi? ". Ya jefo masa tambaya.
" Yasmin Umar, shi ne sunan
da tace mu ringa kiranta da shi kuma mu kanmu ban da malaman mu, har mun fara
manta asalin Isah Sharifai din ". Ya kai karshen zancen yana mai bin hanya
domin yin uzurinsa. Shi kuwa Alhaji Isah kamar an datsa shi a wajen ya dade
yana juya kalaman yaron, cikin rashin kuzari ya tada motarsa tare da barin
wurin.
Meenat tana isa sashinsu labari
taba hajiya Basma a kan Yasmin ta fito farfajiyar Gidan bayan ta san suna nan
ita da Daddy. Hajiya Basma cikin tsoron kada shirinta ya lalace ta ce "
Meenat kyaleta dan uwarta zata gane shayi ruwa ne sai nayi sanadin da za su bar
gidan nan daga ita har shegun ya'yanta, da kuma Mariya da ke zaune a gidan mu, dan
kawai ta haife shi sai ta tare mana a Gida ta ci zamaninta, ta zo kuma tace
zataci da surukai haba wannan zancen karya ne wallahi ". Tana kai karshen
zancen ta fara ƙoƙarin lalubo wayarta, dayan hannunta na kan Diyar Asma'u da ke
kwance saman cinyarta yar kimanin shekaru goma a duniya. Waya take yi da
kawarta, nan da ta shiga bata labarin abin da ke faruwa, daga cen bangaren
sosai ta nuna jijjiga da batun nata inda har ta nuna mata ya kamata, a yi sabon
shirin domin gudun bacin rana.
Duk hirar da suke Meenat da Asma'u sai
murmushi suke, cikin yaukin murya Asma'u ke fadin " ni wlh na tsani ganin
su Yasmin cikin Gidan ubanmu, Daddy yace ba ya'yanshi ba ne to a kan me za su
zauna mana Gida". ta kai karshen zancen tana kara matsewa jikin Mamarta. Hajiya
Basma murmushi da ita kaɗai
ta baiwa kanta sani take yi.
ABUJA CITY
Bayan kwana uku
Safiyar Litinin da misalin karfe goma
Ridwan yan jaridu makil a kofar
Gidansa, yana daga cikin dakinsa sai tashin hayaniyarsu yake ji, duk da asaman
bene yake, ahankali ya fara yunkurin sauka daga kan lallausan gadon barcinsa, idanunsa
ba su gama wartsakewa, sanye yake cikin tsadaddan kayan barcinsa mai kalan
ruwan toka, ahankali ya kai dubansa a kan agogon da ke makale a bangon dakinsa
inda yaga karfe goma da kwata, jin tashin hayaniyar na karuwa ya sa shi tattaro
kuzarinsa tare da yin wajen window din dakinsa. Lallausan hannunsa ya sa domin
janye window glass din Dakinsa, tare da zura kansa domin ganin me ke faruwa, cikin
zallan mamaki da rudewar tunani yaga. . . . . . . . . . . . . . . . .
Makauniyar Shari'a taku ce
Comment and sharhi pls
[10/23, 5:37 PM] Kyauta Daga
Allah: Makauniyar Shari'a
Sai a Lahira
NA
IKILIMA ADAM
(kyauta daga Allah)
Littafin nan, na kuɗi ne da zaran free page ya
kare za ki daina ganin sa. hanzarta ki biya naki kada a yi babu ke.
Dari biyar kacal
3115484026 Ikilima Adam firts
bank
Tura shaidar biya a kan wannan
lambar (09069080725) ko kuma kati kuna iya turawa ta wannan number.
Siyen Nagari mai da kuɗi Gida
Jarumai writ association marubuta
masu aiki da jarumta wajen Fadakar da Al'umma. 📚📚
SHAFI NA GOMA
Yana kara kusanto inda take, tsoro da tashin
hankali suka kara tafasar da zuciyarta, damshin hawayen da ke faranti a idanunta,
dashi take kallonsa, murya a raunace ta ce, " dan Allah kar ka cutar dani,
ban da kowa sai Allah sai Papyna". Ta karashe zancen cikin sheshekar kuka
da jan majina. Kallon ta yake kallon tausayi wanda ze iya fadin a kundin
Rayuwarsa, tun barinsa Gida be ga abunda ya bashi tausayi kamar ita ba, yasha
kashe rai, ya caka wuka a cikin mutum, ya yi garkuwa da mutane, kuma ya yi
informa na yan bindiga duka babu inda baya taka rawar gani, sai kukan Amatullah
ne ze karya masa zuciya. Kafe ta da idanu ya yi yana kallon yanda take matse
jikinta, cikinsanyi murya ya ce " gayamin sunanki? Papyn dinki ya tafi
yabarki na har abada a kan idanuna ya hau mota a tasha kuma na ganshi ya ganni
da bakinsa ya ce min, in mai da ki kar kashin ikona dan haka ki share hawayen
ki, zan zame miki gata kuma zan kula da lamuranki in sha Allah ". ya
karashe zancen yana mai kallon yanda ta zazzare idanu jin wai Papy ya bar garin.
Amatullah sabon babin tashin
hankaline ya bayyana karara tattare da ita, kuzarinta natsuwarta walwalanta duk
sun tafi lokaci daya, maganganun Papy take tariya, hakan ya sa ta saki kuka mai
sauti, tare da rusa uban kuka mai gunji tana fadin " ya Allah !! Ya Allah
!! ya Allah !!. "
Karfin Iko ganin kamar kukan ba bari zatayi ba
sai ta gaji dan kanta hakan ya sa murya a khausashe ya ce " tashi muje ko
kuma in ɗauke ki da
kaina, zabi ya rage naki ". Ya yi magana iyakar gaskiyar sa, yana mai
kallon yanda ta fita hayyacinta lokaci daya.
Sosai da tasha jinin jikinta tana mai dago kai
tana kallonsa da jajayen idanunta, so take ta yi magana ta kasa, ganin yanda ya
haɗa rai yana mai
tsurawa kyakkyawar fuskarta idanu babu kiftawar idanu.
Gani ya yi kamar bata da niyar motsawa hakan
ya sa shi janyota da hannayensa tare da janta tana kuka yana janta, tana ihu
mai kururuwa sai fadi take " Jama'a ku taimaka min ze saceni ". disashewar
muryanta ya sa ba'a jinta, har bakin titi suka isa daidai bakar mota kirar
Mercedes-Benz, kafin ya karasa tuni aka bude masa murfin motar baya, turata ya
yi cikin zafin nama, kana ya sa hannayensa ya rufe gam, ta dayan bangaren ya
shiga ya zauna yana mai kallonta tana kuka mai cin rai ta saka kanta a tsakiyar
kafafunta, numfashi ya fesar kana ya kalli keyar drever tare da bashi izinin
tafiya.
Babu bata lokaci me zaman drever ya ja motar
yana tuki yana kallon Amatullah ta gilashin motar yanda ta cika su da sheshekar
kuka, na kusa dashi ya kalla ya tabe baki, shi ma na kusa dashin girgiza kai
yake yana jinjina al'amarin. Karfin Iko ransa ya dan soma baci a kan yanda take
ta kuka babu sassauci ganin kamar hakan ze sanya sa damuwa ita kuwa ze sanya
mata ciwo yasa, cikin kakkausar murya ya ce " wallahi ki min shiru ko na
sa bindiga na harbe kanki kowa ma ya huta hatta Papy naki baze kara sanyaki a
idanu ba ". Ya karshe zancen cikin dan bacin rai.
Nan da nan tasha jinin jikinta tare da hadiye
ragowar kukanta, soma goge hawayenta ta yi tana mai matse bakinta dan sosai ta
tsorata dajin in ya harbeta bazata kara ganin Papy ba, bayan tun tasowarta Papy
ya nuna mata illah harbi da wuka duk wanda aka cakawa mutum mutuwa zeyi. Bakin
ta na rawa ta dago kanta daga durkushen cikin rawar murya da ban hakuri ta ce
" kayi hakuri bazan sake ba dan Allah kar ka ce zaka harbeni ina son ganin
Papyna ". Ta karshe zancen cikin tsananin tsoron sa da ya shige ta lokaci
daya, dama cen tana tsoron sa be kai na yau ba ne. Drever dana kusa dashi
dariya su kayi dukansu jin yanda take magana cikin rawar murya.
Karfin Iko be bata amsa ba saidai cigaba da
bin ta da kallo yake yana fadi a kasar zuciyarsa Amatullah ke tawa ce har abada
baki da miji kamar ni baki da mafi cancanta sai ni, zan zama mijin ki uban
ya'yanki ". Ya karshe zancen zucin yana mai kar kata idanunsa a kan titi, kallon
tituna yake amma sam hankalinsa amma ta gefen idanu yake kallon ta.
Unguwar gwarinfa na cikin Abuja kai tsaye suka
nufa, inda suka karya kwana izuwa layin Gidan nasa, babban Gida na Alfarma
wanda ya cika da kayan Alatu da kayan more rayuwa, tun daga babban get din kake
hango manya bishiyoyin furanni da aka shuka, haka ma wajen gidan kananan
furanni ne zagaye da wajen gwanin burgewa da ban sha'awa. Horn ya shiga yi, babu
bata lokaci mai gadi ya wangale musu babban gate din gidan, Amatullah wawware
idanunta take ganin sabon gida ginin zamani wanda komai na more rayuwa yana
ciki, parking space drever ya paka motar, kana cikinsauri sauri aka budewa
karfin Iko murfin mota ya fito, yana fita da kan shi ya zagaye domin budewa
Amatullah kan ya karasa ahanzarce yaran nasa ya sa hannu ze bude, hannu ya daga
masa alamun wannan aikinsa ne, cikin hanzarinsa ya sa murdaddun hannayensa ya
bude murfin motar, tare da bin ta da kallo na tsanake, ita kuwa ban da
innalilahi wa inna ilairajun da Papy ya koyar da ita in har tana cikin tashin
hankali babu abunda take maimaitawa a kasan zuciyarta, kana bakinta na dan
motsawa kadan kadan kamar me shirin yin magana, lura da kallon da yake bin ta
mai nuna alamun ya gaji da jira ya sa ta sauke fararen kafafunta a kasa, zararan
idanunta take bin farfajiyar gidan da kallo ganin ma'aikata masu kai kawo da
manya manyan samudawa da ke safa da marwa acikin Gidan, kasa cire idanunta
akansu tayi, batare da ta ankare ba taji hannunta cikin nashi yana janta izuwa
hanyar da ze sadashi da babban falon Gidan. Kallon bayansa take yana gaba tana
binsa, har suka iso gaban haddiyar kofa mai kamar lu'u lu'u ya ci ado kamar na
zinare, sakin hannunta ya yi ya danna wasu numbobi da duk alamu code din kofar
ne, tana ganin ya shiga ta bi bayansa ga mamakinta sai ganin wani kofar glass
ta yi again, shi kam kofar da kansa ya bude kansa, wanda hakan ya sa ta so
callara ihu dan tsoro, duk a zatonta ko tsafi ne, gaba da ya yi ne ya sa besan
halin da take ciki ba, ganin kamar kofar ze rufe bata iso ba ne ya sa shi ɗan juyowa fuskarsa ba yabo
ba fallasa, da mamaki yaga ta rintse idanunta, siririn tsaki yaja kana ya
fisgota tare da jan ta zuwa kayataccen falon da aka narka dukiya, naira ta yi
kuka a wannan tsararren falon, gabakiya falon kalan hash color ne hatta carpet
din falon, sanyi Ac da ke kadawa ya sa ta fara mammatse jikinta tana bin sa har
ya zaunar da ita kan kujerar falo mai taushi da dadin zama, ya salam ta furta ya
yin da ta ji mazaunanta sun sha taushi mai sa nutsuwa da gangar jiki, wawware
idanunta take tana mai kai dubanta a kan television da ke ajiye kan kyakkyawar
mazauninsa, sassanyan ajiyar zuciya ta sauke tana kallonsa yana ƙoƙarin
barin falon, tare da hawa kan matakalan step da idanu ta rakashi cikin dan
tsoro tsoro, papper da ke hannunta ta hanzarta ɗaukewa
ganin ya fadi kasa, maganar zuci take dan yau shi ne karo na farko da taga bene
kan idanunta duk da papy yasha zana mata a takarda, mai da hankalinta ta yi gun
kalle kalle ta har idanunta suka kai kan hadadden fankar da ke kadawa a sama, kana
ta kai dubanta a kan kwayayan kwan fitilu masu launin furanni, tana sauke
idanunta ta mai da kallonta gun diner table wanda yasha jeren kwanukan abinci
da babban wamers da cokula, jok din ba karamin burgeta ya yi ba ganin yanda
yake kamar buta, dan tsaruwa da kyau ƙoƙarin tashi take domin tabawa taji takun
tafiya hakan ya sa ta kara rike takarda hannunta da karfi, sunkuyar da kanta
kasa ta yi tana mai jin buguwar zuciyarta yana tsananta. Jin an karaso kusa da
ita ne ya sa ta dago kai sama, cikin kidima take kallon katuwar mata me kiba
sosai, da murmushi matar take kallonta kana tana kallon Karfin Iko dashi din ma
Amatullah yake kallo, fesar da numfashi ya yi tare da saka duka hannayensa
cikin aljihun wandonsa, cikin muryansa ta dabi'a ya ce" yan mata nan za ki
zauna tare da kulawar Anty Hasina dan haka, ki saki jikinki da ita agidan nan
kaf bakida kamarta bayan ni, sannan duk abin da kike so ki sanar mata in sha
Allah za'a miki. " Yakarashe zancen yana mai kallon Hasina da idanu, ita
ma kallonsa take tana murmushi kana tana kallon Amatullah da tattare wuri daya.
" Yan mata ya sunanki kuma
shekarunki nawa, wace makaranta kike, meye level dinki a karatun boko da
islamiyya". Cewar Hasina Ta jero mata tambayoyi ba kakkautawa kamar jiran
wannan ranar take.
Amatullah dago idanunta sama ta
yi tana kallon Matar daga sama har kasa kana cikin rawar murya ta ce "
Sunana Faridat, amma papy yana kirana da Amatullah ko My Friday, kuma mutan
kauye suna kirana da Yar wahala, shekaruna goma da biyar ". Ta karashe
zancen cikin gaskiyarta da tsantsar kuruciya.
Daga Karfin Iko har Hasina sai da
suka dara kusan tare, da murmushi kwance samar fuskarsu, Karfin Iko kallon
Amatullah yake kamar ba ita ta yi magana yanzu ba.
" Waou Nice name, zan de kiraki da
Amatullah suna yamin dadi, goma da biyar ba suke nan shekarun ki goma sha biyar?".
Ahanzarce Amatullah ta gyada mata kai kamar kadangaruwa.
Cigaba da magana ta yi fuska a
sake ta ce " Ma sha Allah saidai baki gayamin level dinki a. . . . . ".
Saurin katse ta Karfin Iko ya yi ta hanyar
daga mata hannu, tare da zama kan kujera da ke kusa da Amatullah. Jikake tsitt
a falon ban da bugawan zuciyoyinsu. Mama Hasina gefe daya ta samu ta dan raba a
kan lafiayyan Carpet din tsakiyar falon.
" Amatullah wannan da kike
gani yar uwata ce, kamar yanda na dauko ki haka itama na dauko ta daga gidanmu har
muka saba nida ita, dan haka ki saka ranki a inuwa kema za ki saba kamar ita
kuma za ki ji dadin rayuwa, ki manta komi na baya ki fuskanci Alkibla, sannan
ina da dokoki na Gidan nan, ba'a fita daga gidan nan, ko me mutum yake so ya yi
magana da zaran kin dan kara wayau zansa a daura mana Aure ni da ke dan kin min
ba karya ". Ya karashe zancen yana mai kar kata bakinsa, duk da maganganun
da yake idanunsa na kan Television da ke kashe.
Anty Hasina da Amatullah kusan atare suka
kalli junansu, murmushi Hasina ta sakarwa Amatullah, hakan ya sa Amatullah
dukar da kanta tana juya kalaman wai Karfin Iko ne yake fadin ze Aure to ta ya
ya, lissafi ne ne ya darzan mata a zuciya lokaci daya, kallon Hasina take da
idanu ganin ta tafi wajen Karfin iko ta zauna har tana ƙoƙarin rage masa kayan
jikinsa, kauda kanta gefe ta yi tunani fal aranta Papy ya tafi yabarta sabon
babin kuka ne yake son fara zuwa mata, kukan da take shirin ne ta katse ganin
anty Hasina ta kama hannunta tare da mikar da ita, idanunta da suka kawo ruwa
take kallon Hasina da shi domin so take ta ji ina zata kaita, tana mai kallon
yanda Hasina ke sakar mata murmushi.
" Haruna yace aka kai ki
masaukin ki, cen zan kai ki dan haka muje, ki saki ranki nan gidan akwai
ma'aikata maza da mata akwai malamai masu koyar da yara, sannan akwai sashin
marayu duk wanda kike son hira dashi acikin su kofa abude take ". Ta kai
karshen zancen ne tana jan hannun Amatullah izuwa masaukinta.
Amatullah sosai take juya kalaman
wai sashin marayu in har bata manta ba Papy yace mata wanda beda Uwa da Uba ko
kuma ya rasa daya daga cikinsu shi ne maraya. Nan da nan jikinta ya yi mugun
kankara, barin wani tunanin ta yi ta fara sheshekar kukan rashin Papy, ba suke nan yana nufin ya tafi ya barta ba suke nan har abada, tunani take me ya sa
Papy ya dauki danyen aiki akanta, wata zuciyar ta ce " yo ai saboda Karfin
Iko ya san inda kuke ne ya sa ya gudu, nan da nan taji babu abin da take ji da
haushi sama da karfin Ikon. Ajiye tunaninta gefe ta yi sakamakon jin karar bude
kofar da Hasina tayi, hakan ya sa tabi sahunta gun shiga babban daki me fadi, gado
ne aciki sai wadrobe, babu wasu takarce adakin, da idanu take bin dakin da
kallo, ganin yanda iskan fanka ke tashi ba sauki daga sama, fankan take bi da
kallo hade da dan lumshe zararan eyelashe din idanunta. Ita dai kallon Hasina
take ta nuna mata tsarin dakin har toilet da ban daki duk ta kaita, fuskarta ɗauke da murmushin rahma.
Wasa farin girki
Umar Faruk satinsa daya acikin
Abuja, ya rasa inda ze sanya kansa domin tun acikin mota aka sace wayarsa da
kayansa, bashi da komi daga shi sai suturar jikinsa, kuka yake zaune a bakin
masalanci tashar daya sauka, ya fara tuno da kalaman Kanwarsa abun soyuwarsa
Yasmin a kan bata son yaje Abujan, tuno da halin da Mamy zata shiga ya sa hankalinsa
kara tashi. Kuka yake rerawa tsakaninsa da Allah domin wanda ya zo domin shi
babu yanda zeyi ya same sa, kuma ya san shi ma mutumin zeyita nemansa, ganin
babu mafita ne ya sa shi tashi tare da zuwa wajen drebobi masu lodin fasinja
Cotonou, Muryansa na rawa ya ce " Drever dan Allah wani bezo cigiya a
wannan tashar ba? ". Ya idasa zancen murya na rawa.
Drever da idanu yake kare masa
kallon tsafta kana a hanzarce yace wlh kuwa yau kwana biyu ba suke nan wani yana zuwa cigiya kuma da
dukan alamu ya gaji da kai kawo da yake. Wata irin mummunar faduwar gaba ne ya
ziyarci zuciyar Umar, cikin rawar murya da tashin hankali ya ce. . . . . . . .
Makauniyar Shari'a taku ce.
Comments and share pls
[10/23, 5:37 PM] Kyauta Daga
Allah: Makauniyar Shari'a
Sai a Lahira
NA
IKILIMA ADAM
(kyauta daga Allah)
Littafin nan, na kuɗi ne da zaran free page ya
kare za ki daina ganin sa. hanzarta ki biya naki kada a yi babu ke.
Dari biyar kacal
3115484026 Ikilima Adam firts
bank
Tura shaidar biya a kan wannan
lambar (09069080725) ko kuma kati kuna iya turawa ta wannan number.
Siyen Nagari mai da kuɗi Gida
Jarumai writ association marubuta
masu aiki da jarumta wajen Fadakar da Al'umma. 📚📚
SHAFI NA SHA DAYA
Cikin rawar murya da tashin
hankalin da ya bayyana karara afuskarsa ya ce " dan girman Allah be bar
muku number wayarsa ba? ". Ya karashe zancen murya a raunace, sabon babin
tashin hankali ne ya bayyana karara a fuskarsa, yanzu ba suke nan inhar be kara waiwayo tashar ba
shike nan wahala ta same shi, ji yake kamar ya kurma ihu dan tsantsar bacin
ciki, tunaninsa katsewa ya yi jin Drever na fadin.
" Gaskiya ba mu amshi
lambarsa ba amma shi kam ya amshi namu, yace zeyi ta tuntuɓar mu ko za'a dace ". Drever
na kai karshen zancen ya barsa agurin tare da shiga motarsa domin zuwa shan mai.
Faruk ya danji sanyi aransa domin
hakan ya tabbatar masa ze iya kira a kowani lokaci, tashin hankalinsa befi
tunanin abin da ze ringa ci kafin yaga Megidansa ba, yana hangar me shayi a
ketaran titi dabara ta fado masa a kan ya sa ya yanke shawarar yaje ko Allah
zesa adace ya ɗauke sa
aiki koda aikatau ne.
Sun sha tafiya mai dan nisa a
headquarters na yan Sanda kafin suka samu zama kan kujeru na afarman saukan
baki, Commissioner da ke zaune a kujerar da ke kallon nasu, fuskarsa babu yabo
ba fallasa yake kallon kowannensu musamman Ridwan da ya dukar da kai tun
shigowarsa dakin, sosai yake ji tsananin tashin hankali wacce ba'a sanya mata
rana, sanye yake cikin farar shadda wacce yasha aiki farin zare gun kwararan
tela, farar hularsa nake bi da kallo yanda ya zauna masa daram akansa ba
karamin kyau gilashin da ke sanya a idanunsa suka kara masa ba. Dakin zagaye
suke da ma'aikatan yan sanda kowannensu goye da hannayensa ta gaba. Commissioner
Bashir Muhammad ne ya yi gyaran murya hakan ya sa kowa dago kai suna
fuskantarsa, fesar da numfashi ya yi idanunsa na kan Ridwan da shidin ma shi
yake kallo.
" Haba Ridwan Mai Nasara
taya zaka ajiye aiki yau kusan shekara daya ba suke nan, anyi anyi dakai kaki komawa a kan
aikinka, ai zamanka amatsayin shugaban KEDCO na Nigeria ba shi ne yake nunan
cewar bazaka iya hada ayyukanka ba, tun da ka tafi ba'a samu mai ƙoƙarin
ka ba har ila yau, Ridwan ka tuna fa abaya ba ka dau aiki dan ka ajiye ba ina
da yakinin ba tsoro ne ya sa ka ajiye aiki ba, akwai kwakwaran dalilai, haba
Ridwan talakawa suna bukatarka wa'yanda aka tauye musu hakkinsu suna bukatarka,
Ridwan naso ace kaine a kan kujerata, amma kuma zamanka a wannan kujerar baze
baka damar yin aikin da ka saba ba, haba !! haba !! haba !! kayi tunani mana, dan
zatin Ubangiji ka dawo aikinka ya Ridwan ya karashe zancen murya kasa kasa
alamun takaici.
Ridwan jikinsa har tsuma yake kamar mazari, kasa
jure zaman da yake ciki a kan kujerar ne ya sa ya mike ahanzarce tare da bin
gefe sauran jama'a ze raba su ya fice cikin hanzarinsa, har ya kai hannunsa kan
handle din kofar ze bude yaji kakkausar muryan Commissioner Bashir yana fadin
" Ridwan yanzu kana nufin ban isa dakai ba?". Ya karshe zancen yana
kallon keyarsa cike da takaicin taurin kan nasa.
Cak yatsaya be cire hannunsa a
kan handle kofar ba, be waigo ba, ban da tsananin buguwar zuciya ba abin da
yake tsananta a tattare dashi, kamar baze waigo ba yanda yake tsaye kikam, Commissioner
da sauran ma'aikata da idanu suke kallonsa kowannensu. Ba zato ba tsammani suka
ga ya waigo, jajayen idanunsa da suka kada jajir suke bi da kallo, daga inda
yake tsayen ya kara gyara tsayuwarsa, cikin rawar murya me nuni da zallan bakin
ciki ya ce " Afuwan mai girma Commissioner Bashir, ban bijire ba kuma na
yaba da nagartan aikina da kuka yaba, kuma ina mai muku fatan samun wanda
yafini ko da a nan kusa nasan za'a samu fiye dani kar ku damu, na ajiye aiki
bazan. . . . . ". Sauran kalaman da ke shirin furtawa ne suka samu damar
makalewa jin wani dattijon dan Sanda ya rike hannunsa, idanunsa sun kada jajir
kamar gauta yana girgiza masa kai alamun kada ya karasa furucinsa ya san in har
rantsuwa ta shigo ciki tabbas Ridwan yabar abunnan har abada babu waiwaye.
" Dan Allah Dana kayi hakuri,
ko dan tsufana, kar ka cire hannu acikin aikinka, kar ka ce zaka raba hanya
damu ya kai yaron kirki ". Ya karshe zancen yana ƙoƙarin durkushewa kasa dan
magiya .
Ganin haka ahanzarce Ridwan ya
durkushe wajen tarosa hakan ya sa idanunsu tsarkewa cikin na juna shida
dattijon, be san sanda ya kaiwa Dattijon wawan runguma ba, domin dattijon yana
daga cikin wanda yake jin dadin aiki dashi a headquarters.
" Baba zan dawo aiki nan da
wata daya in sha Allah". Ya karashe tare da dagowa dukansu daga durkushen,
kallonsa ya mai da a kan hall din yan dakin yanda aka zuba musu idanu ana
kallonsu, Commissioner murmushi kwance a kan fuskarsa yake fadin "
Alhmdulillah ". A Kasar Zuciyarsa. A fili kuma kasa magana ya yi dan farin
ciki.
Ridwan be tsaya jira abin da za
su fadi ba ya hanzarta barin office din jiki babu kwari.
Dattijon kuwa dawowa tsakiyar
dakin ya yi yana kayataccen murmushi, bakinsa na rawa ya ce " Yallabai in
sha Allah tunda Dsp Ridwan Mai nasara ya dawo aikinsa zancen ya kare kawai
lokaci za mu jira, ahaka da suka ci gaba da tattauna tsare tsarensu.
Shi kuwa Ridwan a farfajiyar
ma'aikatan yana gaisawa da yan sanda da ke kai kawo, murmushi kwance kan
fuskarsa yake gaisawa da wani abokin aikinsa da ya zo wajensa suna tattauna
yaushe rabo, juyawar da zeyi idanunsa ya sauka a kan yan mata yan tallah masu ɗauke da robobin abinci, irinsu
shinkafa da wake da miya da salad, nan da nan ransa ya ɓaci, suna hada idanu da Ridwan nan da nan
hantar cikinsu ya kada sunsan ya hanasu kawo tallan abinci da kananun
shekarunsu, ƙoƙarin
yi musu magana yake yaji muryan Mansur yana fadin " kaga shiga Mota muje
zan duba Mama batada lafiya sosai fa ". Ya karashe zancen cikin tsanani
damuwa.
Ridwan hankalinsa ya ɗauke a kan yan mata masu
tallah, be tsaya bata lokaci ba ya shige motar inda suka ba motar wuta a 360
domin gani suke sam basa sauri ayanda akace Mama tana jin jiki.
Kasar Benin Cotonou
Alhaji Isah Sharifai zaune a
farfajiyar Gidansa shi da Hajiya Basma wacce take sanye cikin kananun kaya riga
da wando ba karamin kama jikinta ya yi ba, shikuwa daga shi sai gajeren
wandonsa da rigar shan iska mara hannu, babyn wasan yara ne a hannunsu yana
jefa mata tana mai da mashi, fuskokinsu ɗauke
da murmushi mai sautin, cikin shagwaba fuska ta duniyanci ta ce " Alhaji
ni de ko sai ka goyani". Yanda ta yi furucin sosai ya basa dariya har
kuncinsa ya lotsa.
Cikin yar tsokana yake fadin
" kema kin bi wakar nan da ake ya yi ko? ai ba matsala ba ne dan masoyi ya
goya abar kaunarsa kuma. . . . . ". Kasa karasa ragowar kalamansa ya yi
ganin Yasmin ta fito kamar wata yar mabarata, ahanzarce dan sauri sauri take
tafiya, sam bata gane inda take sanya kafafunta, tana karasowa kusan Alhaji da
Matarsa, kallo daya ta musu ta ɗauke
kanta, ganin su ma ita din suke kallo da mamaki fuskokinsu sannan babu fara'a a
fuskokinsu. Da idanu Alhaji ke bin ta da kallo ganin kodaddiyar doguwar rigar
da ke jikin ta, kara rufe baki ya yi ganin ta isa gun Baba Mai Gadi, muryanta
na rawa ta ce " Baba Dan zatin Ubangiji ka taimaka ka ba mu aron dubu daya,
wallahi yau kwana hudu ba mu samu labarin yaya Umar ba, kuma Wallahi Mamy olsa
dinta ya tashi kwana biyu ba mu ci ba, dan zatin Ubangiji kamar yanda Allah ya
taimakeka ka taimaka mana wlh inna samu zan mai da maka kudin ka, ko kuma in
antina ta zo za'a baka, wlh kakata ma yanzu haka tana cen kwance, kar ka ce min
babu komi a hannunka dan Allah !! ". ta karshen zancen cikin kuka mai
gunji.
Bala mai Gadi cikin rudewa ya ce
" Subuhannallah muje daga ciki ina da dubu biyar zan baku har sai kun samu
". Ya kai karshen zancen yana mai shiga dakinsa domin dauko kudin, da kuma
robar faro faron kununsa a hannunsa.
Yana fitowa mika mata kudin ya yi
kana ta yi gaba cikin hanzarinta shima ya take mata baya.
Duk abin da ke faruwa a kan idanun Alhaji Isah
shida Basma, siririn tsaki yaja, tare da kai dubansa a kan Basma cikin nuna
kulawa ya ce " daman dan A'isha baya garin nan?". Ya yi mata tambaya
cikin rawar murya.
Basma na dan nan ta bata fuska kamar wacce
akayi wa albishir da ranar mutuwarta cikin jin haushinsa ta ce " wai kai
Alhaji kai har yanzu baka san sharrin Yasmin ba, duk pretendin take, domin a
tausaya mata take kuma wallahi karya take, ni dazun ma na ga Umar din, amma
kaji yar rainon matsiyaciyata tana fadin baya garin, wai kai Alhaji ina ruwanka
da lamarinsu ne, kasan dai yaranta ne ka daina sanya mata idanu da yayanta, ban
da abunka ma, kabarsu acikin Gidan ka kar yau mutuwa ta riskeka suce suna da
Gadon ka, gaskiya ka dau mataki ". Ta idasa zancen cikin ruwan bala'i. Alhaji
sosai maganganunta sukayi tasiri a ilahirin jikinsa, kamar ankada shi da ganga
zumbur ya mike, ya kama hanyar da ze sadashi da sashinsu Yasmin cikin zafin
nama, ita kuwa Basma ganin ya fice sai da ta ranka guda kana tabi sahunsa tana
tafiya tana karairaya har ta iso inda yake. Bankada kofar da karfi ya yi ya
shigo dakin.
A kidime Yasmin da Baba mai Gadi
suke kallon yanda yake huci kamar zakanya.
Mamy da ke shan faroron kunun da me Gadi ya
kawo mata da shanyayyun idanunta take kallonsa dan zata iya rantsewa rabonta
data sanya shi a idanunta anfi shekaru uku.
Shi kuwa kallon su yake yana hura
hanci kana ya kalli gefensa ganin Basma tana kusa dashi, ita ma kallon banza
take binsu dashi tana kwabe baki .
Cikin zazzafan kalamai ya ce " Aishatu na
baki daga nan zuwa gobe ku tattara ina ku, ku bar min gidana, sannan ina fatan
in zaku tafi ku hada da Mamata ku tafi da ita dan kun shayar da ita guban
halinku, wanda ni Isah bazan iya zama da ita ba, sannan. . . ". Ba tare da
ya karasa ba, Yasmin ta dakatar dashi ta hanyar fadin .
" wallahi tallahi, na
rantsewa wanda numfashina yake hannunsa idan. . . . . . . . .
Makauniyar Shari'a taku ce
Comment and sharhi pls
[10/23, 5:37 PM] Kyauta Daga
Allah: Makauniyar Shari'a
Sai a Lahira
NA
IKILIMA ADAM
(kyauta daga Allah)
Littafin nan, na kuɗi ne da zaran free page ya
kare za ki daina ganin sa. hanzarta ki biya naki kada a yi babu ke.
Dari biyar kacal
3115484026 Ikilima Adam firts
bank
Tura shaidar biya a kan wannan
lambar (09069080725) ko kuma kati kuna iya turawa ta wannan number.
Siyen Nagari mai da kuɗi Gida
Jarumai writ association marubuta
masu aiki da jarumta wajen Fadakar da Al'umma. 📚📚
SHAFI NA SHA BIYU
Wallahi tallahi, na rantsewa
wanda numfashina ke hannunsa idan kaga mun fita sai da kwakwaran hujja da ze
tabbatar mana mu shegu ne kamar yanda kake ambata ko wani time ". Cewar
Yasmin cikin tsananin bacin rai, dan hankalinta ya gushe bare har ta gane
girman wanda ke gabanta.
Mamy kuwa rintse idanunta ta yi domin
taji takaicin tanka masa da Yasmin tayi, cikin raunin murya me nuna da sam babu
kuzari tattare da ita, tace " Haba Yasmin Mahaifinki kike jifa da wannan
munanan kalaman ". Ta idasa zancen tana kallon Baba Mai Gadi da ke ƙoƙarin
fita daga Dakin yana yaba ƙoƙarin Yasmin acikin ransa dan ta burgesa.
" Ahirr dinki ko da wasa kada ki kuskura
ki kara alakantani da ya'yanki nace ya'yan nan ba nawa ba ne kinki ki gane, tsinannun
yayanki za ki ringa dangantani dasu dayan tunda ya san ni ba mahaifinsa ba ne
ya gudu yabar Gida, shi kuma la'anannen danki Umar tsabar ana son in mutu aci
dukiyata shiyasa yaki barmin gidana, ta Allah ba taku ba". Cewar Alhaji
Isah cikin kakkausar murya.
Mamy idanunta cike da hawaye tana kallon yanda
Basma ta daura hannunta daya a kan kafadarsa tana taunan Cingam ji kake karar
karas. Bata ankare ba hawaye Masu zafi suka fara bin kuncinta.
Ahanzarce ta shanye kukanta jin
ya cigaba da fadin" tunda ba zaku barmin gidana ba ku saurari sammaci daga
kotu nasan a nan ne za'a mun iya daku, sannan ke Yasmin har kinada bakin da za
ki dubi tsabar idanuna kice bazaku fita ba, to wallahi kotu ce zata rabamu nida
ku, dan asirinku be kamani ba wallahi kamar yanda kuka shanye Mamata haka kuka
shanye me Gadi, shi ma hada shi zanyi da ku yabi ku dan babu amfanin zama da
wanda ya rabe ku ". Ya kai karshen zancen yana mai jifar Yasmin da Mamy
mugun kallo kamar yaga kashi. Ita kuwa Basma sosai taji dadi hakan ya sa ta
kara cakumosa tana ƙoƙarin rungume shi ta baya, shi kuwa kaucewa yake ba tare da ya
kara bin ta kansu ba ya fice daga sashin nasu a zafafe shida Basma.
Yana fita suka fashe da marayan kuka dukansu, cikin
rawar murya da tsananin tsoro Yasmin ke kallon Mamy da jikakkun idanunta, murya
na rawa ta ce " me Alhaji Isah yake nufi yana nufin mu ba ya'yan sunnah ba
ne, in har hakane waye Uban namu? Mamy kalmar nan yafi kona min rai in muna da
wani uban ki nuna mana, ya fi mu zauna gidan uban w. . . . . . . ". Ragowar
kalamanta makalewa su kayi sakamakon jin wawan mari à kuncinta.
Arazane take kallon Mamy hannunta
rike da kuncinta, domin ba karamin radadi ke shigarta ba, hawaye kamar saukan
ruwa haka ta yi ta silalo su.
" Yasmin wai har ki dubi
tsabar idanuna ki ce in nemo muku Mahaifin ku me kuke tunani, wallahi bakuda
Mahaifi sama da Isah, kawai cin fuska da rashin tsoron Allah ke damunsa, tunda
yace ze kaimu kara kotu, Yasmin ban da mafita illah kawai aje kotun, Yasmin ban
da Iyaye ni Marainiya ce, na taso hannun Matar babana bansan kowa ba, ita kanta
ta rasu yanzu, damar gidan haya muke zaune, Yasmin bawai dadi ne ko haduwar
gidan nan ya sa muke zaune cikinsa ba, muna zaune ne dan bamuda yanda za muyi
kuma bamuda kudin kama hayah, Yasmin kinsan Uwa be cancanci tana zubar da
hawaye gaban yarta ba, amma yau Yasmin dole ce ta sa nayi, babban tashin
hankalina Babu labarin Umar nasan duk inda yaji wannan labarin wlh ze wanko
kafa ya dawo Gida, ina rokon Allah a duk inda yake Allah ka kare min shi ya sa lafiya
lau yake, radadin yamin yawa Yasmin, rana zafi inuwa kuna ". Ta karashe
zancen tare da kaiwa Yasmin wawan runguma, kuka suke dukansu babu mai rarrashin
wani.
Kaicona
Alhaji Isah yana zuwa bangarensa,
zaro babban wayarsa kiran iPhone 15 prox max, keybor din wayar ya shiga tare da
dannawa dan sanda waya, ganin ba'a daga ba ya fara safa da marwa cikin zafin
rai da takaicin kalaman Yasmin da ke yawo saman kwakwalwar kansa. Jin an daga
wayar ne ya sa shi zama kan hannun kujerar mai zaman mutum daya, fesar da
zazzafan numfashi ya yi yana mai magana cikin kakkausar murya tare da fadin
" Dsp Faisal Haruna dan Allah ka zo gidana akwai case din da nakeson atura
kotu ". Ya kai karshen zancen yana mai kasa falalan kunnuwansa gun
sauraren amsa daga cen bangaren.
Dsp Faisal cikin girmamawa ya ce
" Alhaji angama, ka kira lauyarka mu hadu dashi a gidan tare". Daga
haka sukayi gaba da waya inda sukayi sallama. .
Gefensa ya kalla ya hango Basma tana masa
kyakkyawan murmushi mai nuni da tsantsar farin ciki, shi ma murmushin ya mai da
mata, cikin muryansa mai nuni da takaici ya ce " Basma badan ke ba da
wallahi kullum sai inyi ta kallo yaran nan amatsayin nawa bayan shegu ne, kai
wallahi A'isha ta cuce ni tsakanina da ita sai kotu". Ya kai karshen
zancen murya kasa kasa.
Murmushi take sauke masa tsabar farin cikin, cikin
azzama ta karasa gabansa tare da jero masa kiss a goshin sa, cike da jin dadi
ta nuna godiya a garesa a kan yanda ze cire guba a cikin gidansa.
Abuja Gwarinfa
Hasina zaune a tsakiyar dakin
Amatullah, cikin idanu take kallon yanda take kuka ba kakkautawa ganin kukan
zeyi yawa tunda aka kawota shi ne abin da ta sanya agaba da anbata abinci
saidai tasa kuka tana kiran Papy.
Hasina zama bakin gadon ta yi tana kallonta
cikin idanu, kana cikinsanyin murya ta ce, Haba Amatullah so kike ki kashe
kanki, kinsan dai Papy baze so ya ganki cikin Matsala ba bare har yaji bkayason
cin abinci, ki taimaka kici koda kadan ne. " ta kai karshen zancen tana
jinjina lamarin yarinyar.
Amatullah kamar bata jin ta haka
ta yi banza da ita. Cikin zuciyar da bata san tana dashi ba sai yau, cikin da
fadafada ta ce" ni kawai a mai dani inda aka daukoni inje inga Papyn kuma
wallahi baku kaini ba saina jaza muku bala'i. Ta karashe zancen cikin tsiwa.
Hasina da murmushi kwance a fuskarta take
kallonta yanda Amatullah ke juya karamin bakinta, hakan ba karamin burgeta ya
yi ba, numfashi ta fesar fuskarta ba yabo ba fallasa cikin tsare gida ta ce
" Amatullah nasan ko ban ban haifeki ba nayi kanwa da ke, ke karamar
yarinya ce ina tausaya miki matuka, amma Haruna ba kanwar lasa ba ne duk yanda
kike ganinsa ya zarce tunaninki, ki ajiye kuka agefe ki rungumi kaddara, dan ni
nan da kike gani a bola aka tsinceni tun ina yar shekara biyu zuwa uku, Maman
Haruna Allah yajikanta ita ce ta raineni tare da mahaifinsa, bayan ba ransu shi
ne Haruna ya dawo dani kar kashin kulawarsa duk da haka ni Hasina bazan bari ya
aure ki ba kamar yanda ya furta, dan babu wacce ya dace ya aura sama dani, wa
ze aureni in yaji cewar ni shegiya ce ko kuma akace ban da asali, dole Haruna
dai ze aureni domin shi kaɗai
ne ya san zafina kuma yake gudun a wulakantani, Amatullah ki godewa Allah, ke
har yanzu ne kike kukan Papy, mu da ba mu ga papy da mamy ba me za mu ce?".
Ta kai karshen zancen hawaye na bin kuncinta.
Sosai Amatullah ta gigice ganin yanda Hasina
ke kuka ta tabbatar har kasar zuciyarta ne, cikin hanzari ta matso kusa da ita,
tana mai share mata kwalla da hannunta, sannan ta ja dogon numfashi, idanunta
masu damshi hawaye ne take kallon Hasina dashi, murya a raunace ta ce "
Papy na ya gayamin kada in bari babba ya yi kuka akaina ba tare da ya cutar
dani ba, dan Allah ki yafe min ". Ta kai karshen zancen tana mai harhada
dukan hannayenta wajen rokon afuwa.
Hasina da murmushi ta warware ma ta hannayen
ta tana mai kallon ta cikin idanu.
Amatullah ta ciga da fadin "
daga yau in sha Allah na rage damuwar da nasa wa kaina, zan ringa cin abinci, amma
bazan taba daina tunanin Papy ba, zanyita addu'a Allah ya nuna min shi ". Ta
karashe zancen cikin cool voice dinta.
Mama Hasina murmushi ta sakar mata tare da
kama hannunta ta mikar da ita domin su je ta bata abinci abinci ta ci, domin na
dakin har ya yi sanyi. Ba musu ta bi bayanta tana mai rarraba idanu a kan hadadden
Gidan da sam bata gajiya da kallo.
Dayan bangaren
Ridwan da Mansur da kanwar Mansur
mai suna Mansura sai kai kawo suke bakin dakin da aka rubuta emergency da duk
alamun mamar su Mansur tana ciki.
Mansura kallon Ridwan take yanda
sukayi cirko cirko gaban kofar shida Mansur ta san jira suke docto ya fito. Kara
zubawa Ridwan idanu ta yi ganin yanda suke magana shida amininsa aminci yarda
kaunar juna, Amana duk ta hango tattare da abokan juna. Kasan zuciyarta tana
tunanin yanda zatayi Ridwan ya fahimci tana sonsa dan ita da gaske wallahi
sonsa take, shiyasa take son ta yi amfani da amincin da ke tsakaninsu wajen
shawo kan Ridwan din.
Fitowar docto ne ya sa ta bar
tunaninta ganin sun Ridwan sun tsare shi da tambaya.
Ridwan ya ce " docto ya
jikin mama baka ce mana komi ba". Ya kai karshen zancen yana kallon yanda
docto ke sauke ajiyar zuciya.
" Mun yi ƙoƙari
gaskiya wajen dai-dai numfashinta yanzu haka oxygène ne ahancinta in sha Allah,
muna sa ran daga nan zuwa gobe zata iya farkawa dan haka ku biyoni office domin
jin cikakken bayani ". Ya karashe zancen dai-dai lokacin da sauran
likiticin mataimakansa suka fito daga dakin emergency, su kam ko tsayawa ba suyi
ba suka yi gaba gabadayansu har docto da yabi sahun su.
Ridwan da Mansur kallon juna su
kayi suna juya, watau har sai zuwa gobe ne zata farka, ganin tunaninsu babu
mafita ne ya sa suka hanzarta kama hanyar zuwa office din docto.
Mansura kuwa mayataccen idanunta
ta zuba bayan Ridwan kallo yanda yake tafiya cikin kasaita da haibarsa.
Bayan kwana biyu
Umar Farouk aiki ya samu wajen me
shayi inda shi ne yake masa wanke wanke kai shayi da indomi, kullum me shayi ke
sallamarsa kudin aikinsa duk da befi na abinci ba yake ba shi, hakanan yaji sam
hankalinsa ba akwnace yake ba, zuciyarsa na tsananta bugawa da ƙarfi zumbur
ya mike ya samu me shayi da ke hira da customer murya na rawa yace " dan
Allah megida ka aramin wayarka zan sanya kati in kira gida inji lafiyarsu, wani
wawan kallo mai shayi ya jefe shi dashi cikin jin haushinsa ya ce " Allah
yakyauta in baka wayata, dudu yaushe ka fara aiki da har zaka sanya kati kayi
kira". Ya karashe zancen cikin fada.
Daya daga cikinsu da ke zaune yana cin indomi
da kwai ne ya ce " Haba me shayi babu kyau wulakanta dan Adam wlh wannan
yaron daga ganin yanayinsa kasan yana cikin damuwa, in bazaka taimaka masa ba
pls basai ka hada masa da bakaken ma maganganu ba".
Nan fa cece kuce ya barke
tsakaninsu in da akarshe mutumin ya yi zuciya yabar abincin jin me shayi na
fada masa to shi ya bashi wayarsa mana, yana tashi ya kama hannun Umar cikin
zuciya da barci rai ya ce" yaro ka yarda dani ka kuma yarda da Allah muje
zan taimaka maka, kabar aikin wahala ba abin da yake baka sai nacin abinci
". Ya karashe zancen yana jan hannun Umar.
Umar cikinsanyi jiki da rawar
murya ya ce " Alhaji kayi hakuri ni na hakura da wayar ma, ƙoƙarin
zuwa gaban me shayi, da yake sake baki, domin bashi hakuri, tuni Alhaji ya hana
cikin fada ya ce " kai bazaka bashi hakuri ba kyale dan iska, wanda be iya
magana ba, in zaka shigo mu tafi zan sama maka aikin da za'a ringa biyanka
domin alamu ya nuna kai me iyali ne duk da kanada kananun shekaru. Umar kuwa
nan da nan Mamy ta fado masa a rai dan haka be tsaya wata wata ba ya shiga
motar.
Me shayi na ganin sun fice sosai
hankalinsa ya tashi domin be bata samun yaro me biyayya irin Umar ba. Nan fa
mutane sukayi ta masa Allah wadai da mugun halinsa shiyasa kullun ya kasa zama
da masu aiki.
Me shayi na ƙoƙarin
tattare kwanukan shayinsa yaji sallama da bakon murya, ahanzarce ya daga kansa
yana kallon mutumin da ke sanye cikin farar jallabiya fuskarsa babu walwala ya
ce " bawan Allah daga tasha na fito ina cigiyar wani yaro me suna Umar aka
cemin a wajen ka yake aiki? Dan Allah Ina yake inason ganinsa ni uban gidansa
ne. " Ya karshe zancen cikin kosawa da amsa.
Zazzare idanu me shayi ya yi
ganin babban mutum ne mai kamala da haiba agabansa, cikin rudewa ya ce "
wallahi yanzu nan wani ya tafi dashi sakamakon mun dan samu sabani ni
dashi". Nan fa ya koro masa dukan abin da ya faru tsakaninsu.
Mutumin sosai ransa ya baci, cikinsanyin
jiki ya koma motar ya zauna tare da dafe kansa cikin damuwa.
Bayan kwanna uku
Benin Cotonou
Yasmin cikin takaici ta ce "
Mamy me ya sa da yaya Umar ya kira baki gayamasa halin da muke ciki ba ". Ta
kai karshen zancen tana cin tuwo miyan kuka wanda suka kada shi lami babu magi
bare gishiri a ciki.
Ƙarar kwankwasa kofa ne ya sa Mamy yin
shiru ba tare da taba Yasmin amsa ba. Ahanzarce yasmin ta bude kofar cikin
tsananin rudewa ta ga jami'an yan sanda su uku, bakinta na rawa ta ce "
bayin Allan lafiya kuwa. ". .
Suka ba ta amsa da " mun kawo muku sammaci ne daga. . . . . . . . .
*************
Littafin nan, na kuɗi ne. Da zaran free page ya kare za ki daina ganin sa. Hanzarta ki biya naki kada a yi babu ke.
Kibiya dari biyar kacal domin samun shiga group na musamman.
Domin Karin bayani a tuntuɓe ni ta wannan lambar 09069080725 ko + 22953726162.
Siyen nagari mai da kuɗi gida.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.