Lokacin da Fatiha ta faɗa masa mahaifinta ya ce ya turo aifa yai murna iya murna ji yake kamar anbashi sarautar mulkin mutan Nigeria koma na nahiyar Afrika baki ɗaya ashe ada shi ba so yai ba shirme ne kawai yanzu ya san mene so me ake nufi da ƙauna yadda kawai cewa akai ya turo anman farin cikinsa yazama maras misaltuwa.
Lokacin da ya jema mahaifin sa da batun shi ma
yaji daɗi yadda fajar
yaga farin ciki fuskar mahaifin nasa ya masa daɗi
gami da yadda mahaifin nasu ya wuce masa gaba duda kuwa ba shi yaje ba amininsa
ya sa saidai yaji daɗi
dan ada baya sa baki a abun da ya shafesu.
Lefen da ya haɗawa
Fa'iza da suka dawo masa da shi shi ne aka fito da shi ya haɗo abubuwan da ba'a rasa ba
maza ne suka kai duda kasantuwar lefen ba wani mai yawa bane sai dai za a iya
cewa a dangin su Fatiha ba'a taɓa
kamarsa ba sakamakon auren zumunci suke ba kuma arziƙi ne dasu ba.
Kan ka ce mene wannan maganar lefen ta baza
gari duk dsngin nasu maganar lefen suke inda da yawa maganarsu ita ce anya ba
lashe kurwar yaron mutane taiba har yaji zai aureta ya haɗo da uban lefe haka.
Sudai shiru sukai suka toshe kunnuwansu inda
ummanta tafi kowa farin cikin ganin ɗiyar
tata tasamu miji kuma wanda take so yake santa.
Wata shida aka saka wanda shi ma yayyenta ne
suka zaɓi hakan dan su
samu su kintsa sosai yadda zasu fidda ƙanwar tasu inta fajar ne shikam asa ko
wata guda ma yana jin yai nisa Yaita ma Fatiha mita ita dai dariya ma ya dinga
bata.
Cikin lokutan da suka rage soyayya da shaƙuwa
mai ƙarfi
ƙara
ƙaruwa
tsakanin masoyan biyu gurin Zamansu na agric yazama matattar fajar dan yanzu ko
zaman office baya yi yana fitowa daga aji zai yo gurin ko ba ta nan haka zai
zauna yana jiranta yana kallon hotunan da ya mata awaya.
Inko suka ɗan
samu saɓani taƙi zuwa
gurin sedai ta koma gida ta ganshi a ƙofar gidansu sosai suke san junansu kana
ganinsu kaga masoya duda da wuya kaji suna hirar soyayya ko dan sun riga sun
saba da hirar rayuwa ne oho.
Tun Fatiha na jin kunyar kar ‘yan
ajinsu suzo suganta da shi a gurin tun da sunsan malami ne dandai ya ɗaukesu GSP harta sake dan
randa ta karanbanin ce masa dan Allah ya dena zuwa gun tun da dai yana zuwa
gida kaca kaca sukai yaita mita wai ya gane shi baikai wanda zataso wasu su
ganta da shi bane shi ya sa take faɗin
haka taita ba shi haƙuri daƙyar tasamu ya yaƙura.
Duk wanda ya san Fajar ya san da Fatiha ta
jima da zama a ransa ɗalibansa
ma sun sanda akwai wata me suna Fatiha arayuwar sa dan kuwa ko misali zai basu
lokacin karatu za ka tsinci sunan Fatiha shi ne kan gaba.
Wannan sabuwar
ɗabi'ar tasa ita tafi ɗagawa Farida hankali yadda
taga ya dulmiya cikin kogin san wata duk damuwarta dai ta ƙaru duda
kuwa ayanzu sun saba da shi sosai takan kirashi ma awaya su gaisa har wasa da
dariya suke duk sanadin project ɗinta.
Ada tana jin daɗin
kiransa dam har hira suke ta chat ma haka sai dai banda ayanzu domin kuwa maga ɗaya biyu zai fara mata
hirar wata Fatiha itakam ta tsani sunan sosai takejin kishin me sunan duda
batasan ta ba.
Ji take ina ma ita ce ta samu fajar tasan ko
bakomai zatasha kulawa dan yadda ya damu da mesuna Fatihan nan ko ba ta waje
tasan kam tanashan kulawa irinsu malam Fajar ne basu iya soba in kuma suka fara
shi basu san wani abu denashi ba.
Tausayin kanta ya cika ta itakam wannan masifa
har ina haka.
Fatiha kanta har tausayin fajar take yadda
yakesan ta musanman in ta tuno ta mutuwa sai tausayinsa ya cikata ko ya zai yi
in ta mutu tasan tana san sa sai dai yadda take ganin ƙaunarta ƙara ra
atattare da shi ya sa take ƙarasa godewa Allah da yabata me ƙaunarta.
Farida ce zaune a office in Fajar ita da Ma'u
yana duba project ɗin
da ta kawo masa sa'a ma taiyi taga office ɗin
abuɗe ta shiga ta hau
roƙensa
kan ya duba dan ta kwan biyu da kawo wa kullin baya nan baya zama suna hira
sama sama.
Fatiha tai Sallama sanye take da leshinta milk
da hijabinta ruwan zuma tai kyau sosai yana jin muryarta ya ɗago yana murmushi ta jima
batazo Department ɗin
yau mamaki tai niyar bashi.
Yadda yake faman washe baki ya sa faridar
Fahintar wannan ce Fatihan da alama ta zuba mata ido ta ganeta ita ce yarinyar
da ta gansu kwanaki sai dai yau da ta kalle ta sosai se take mata kallon sani
sedai ta rasa ina tasan ta.
Fajar ya katse mata tunani da Faɗin Farida ga ƙanwata
Fatiha ku gaisa farida ta daure suka gaisa yadda ya mai da hankalinsa kan
Fatihar yabar duba project ɗin
ya sa Farida miƙewa Sir za muje mu dawo ok kawai ya ce sukai waje.
💞
Don't forget to vote, comment and follow 💞
Ayanzu fajar baya jin kunyar kowa kan Fatihar
sa dan ko faculty ɗinsu
ta je shi yake riƙo mata takaddun ta zuwa gun motarsa da yawa cikin ɗalibansa sun san yana san
yarinyar yadda yake wani walwala in ya ganta.
Yanzu ma zaune suke a kujerun da suke bakin
political science department suna hira wucewa kawai zasuyi Fatiha ta dubi gurin
ta ce gurin nan zai daɗin
zama ya ce ko mu zauna ne a'a ta ce tunawa datai shifa malam ne beci aganshi da
wata zaune ba gurin yai yazauna ta ce pls kazo mu ƙarasa ta nuno masa
sociology department kaga fa har munzo kinga sedai in nine kike kyamar aganki
tare dani.
Kusa da shi ta je tazauna suka hau fira yana
nuna mata posting ɗin
mutane a twitter dan ita ba ta wani abu da ya shafi social media sosai suke jin
daɗin yanayin kana
ganinsu kaga masoya.
Duk asabar da lahadin duniya inka lalubi fajar
za ka sameshi a unguwar su Fatiha dan ma tana ƙi da tashi ne kullun shi zai ɗaukota yakawota makaranta
ya kuma mai da ita ada ko old campus ɗinma
ta dena binsa sai da taga yai fushi sannan sukai yar jejeniya kan iya old
campus.
***
Ta ɓan garen Faruk kuwa abin
duniya ya masa yawa tun lokacin da ya samu labarin saka ranar yarinyar da ya
riga ya gama tsara rayuwarsa da ita yarinyar da dukkan burinsa akanta yake.
Lokacin da ya zo gidansu Fajar ya zo yadda
yaga ta sake tana ta walwala da wanda aka ce masa shi ne za ta aura ya tabbatar
masa da tabbas yayi rashin burin zuciyarsa sedai duk da haka ya kasa zuwa ya
kalle ta duda ba ta sani ba kusan kullin sai ya zo inda take sana'a wani zubin
ma sai ta tashe yake barin gurin cike da tausayin kansa dan ya san shikam tuni
ta mance da shi yadda yaga ita rayuwar ta kawai take.
Ya san ta mance da babun sa tun da sau ɗaya suka taɓa haɗuwa ta da sunan so daga nan ta dena fitowa dan
ta ji me kawoshi shi kuma ya ba ta hutu ko tayi tunani ashe besani ba hakan shi
ne babban kuskuren da yai ya san ta jima dasashi a kwandon shara ya san tuni
tai zaton daman ba son gaske bane duda ya san da wanda take so ɗin baya mata rabin son da
shi yake mata nace uhummm faruk kenan kanka kawai kasani.
Komai aka sa lokaci asannu zai zo yau take ɗaurin auren Fajar yadda
yake ta wani rawar kai da kai kawo har kunya yake baima ummansa itakam gwanda aɗaura auren na akawo ma
Deeni matar nan ko ta samu ta huta da zumuɗi
dan ita a gurin ta duk zumuɗi
ne da ango kanyi in za a kawo masa amarya.
Yayin da shi kuwa gurin fajar duk cikin farin
cikin Fatihar sa ta kusa zama tasan agaske ta kusa dawowa kusa da shi suyi
rayuwa ta har abada shi baima san yana wani abin ba sai an masa tsiya yakanyi
murmushi kawai dan yanzu ya riga ya gama yadda da so kan mai da mutun zuwa wani
daban da shi kansa baisani ba dan shi da kansa yana mamakin anya shiɗinne kuwa true love make
life colorful.
Ƙarfe uku dai dai aka ɗaura auren Fatiha
Abdurrashid da Fajarudden Isma'il anan masallacin juma'a na BUK old campus.
Fatiha na zaune ya kirata yana tsokanar ta
kaga uwar gida gurin Deeni ta turo baki kamar yana ganinta wane irin uwar gida
yai dariya mai da wuƙar ina nufin amarya kuma uwar gidansa ke ɗaya ce ki yi mulkinki daga
ke ba ƙari
tai murmushin jin daɗi
har kasa na ji kunya wallahi.
Hira suka ɗan
taɓa irin ta masoya
kamin suyi sallama ta rungume wayar tana jin daɗi
wai yau ita ce tai aure kuma Deen ɗinta
ta aura saƙon
da ya shigo wayar ya sa ta duba wayar.
Assalamu
alaikum
Sunana Faruk
bana jin zaki gane ni ina miki fatan alkairi arayuwar auren ki Allah ya sa
albar yabada zurriya ta gari na gode.
Tsintar kanta
da cewa amin tai ta fice daga ɗakin
jin ana kiranta.
Shiko Faruk yana tura saƙon ya
goge number ɗin da yai
mata ma'ajiya da matata gami da share hawayensa yai inda ya ajiye motarsa ya
jata yabar harabar makarantar.
Kai tsaye gida ya wuce ya ɗauki kayansa driver ya
jashi zuwa Aminu kano airport dan daman ya shirya kan zai halarci ɗaurin auren dan ya tabbatar
da cewar da gaske ya rasa Fatiha dan baya san zuciyarsa ta dinga kawo masa
tantama.
Huɗu
dedai jirginsu ya tashi inda ya nufi Jordan dan can ya nufa ba kuma ranar
dawowa dan ji yake duniyar ta masa zafi musanman ƙasar tasa Nigeria.
Da yan macin ranar juma'ar ne da aka ɗaura auren Fajar ya zo
gidansu taƙi
fitowa aikuwa yaƙi tafiya har magariba ganin haka ya sa ummanta tasa dole ta
fito aiko ta haɗe rai
sedai yadda yaketa zolayarta yasata dariya ta ce wai mutum shi ma dai anman ai
lahadi kaman yaune ya langwabar da kai ni wallahi dama abar bikin mayi abunmi
haɗe da na suna ta
zaro ido kaga nayi gida tai ciki tana dariya ya hau kwala mata kira shi ma yana
dariya ganin taƙi dawowa ne yasashi jan motarsa yai gida ransa fes.
Ranar asabar
aka sa ita ce kamu anan gidan maƙotansu za'ayi inda ‘yan
uwan Fajarudden zasu zo dan kama amarya.
Amarya tai kyau sosai kamar wata zinariya kai
bazaka ganta ba kai zaton ‘yar gidan talaka ce ba zato zakai wata ‘yar hamshaƙin
mutun ce duda ba wata shigar alfarma taiba.
Fatiha Fara ce ba sal ba mai tsayi ce cikin
mata tana da jiki ko ba za a kirata siririya ba haka baza'a kirata lukuta ba
tana da yalwal sumar kai wanda ta sakko bar wuya yayinda gaban goshinta ma gashinta
baƙi
siɗin ne a kwance dake
ƙara
mata kyau kazalika tana da dara daran idanu wanda suke farare tasa gashin
idanunta ma zara zara ne girarta kamar zana mata akai ba ta cika dogon hanci ba
sai dai ya dace da yanayin ta ita ɗin
me sanyi ce hakan yake ƙarawa fajar san ta dan yansan mace me sanyi arayuwar sa komai
tai birgeshi yake.
Kowa yaganta sai ya yaba da yanda tai kyau jan
les ne a jikinta mai adon baƙi da zaiba simple make up aka mata tai
kyau sosai kowa yaganta ya san tabbas ita ce amarya ita da kanta tasan tai kyau
har mamaki take na kyan da tai take .
Cikin ‘yan uwan Fajar ɗin da suka zone Hajiya Basira Matar aminin
mahaifin Fajar ta fito da sauri tana faɗin
Ubaida ubaida!!! Wadda ake kira ɗin
ta juyo ganin me kiran tai saurin ƙarasowa tana murmushi suka gaisa Hajiya
Basira ta ce kardai ki bikin ɗiyar
tawa kika zo eh anman ta gurin ango ayya nifa ince suka kuma gaisawa gami da
tambayar juna bayan saduwa.
Kinga ikon Allah aure me haɗa zumunci bayan lokaci mai
tsayi min sake haɗuwa
wallahi fa ai kimma san mahaifiyar Amaryar inji wadda aka kira da ubaida dan
Allah fa inji Hajiya Basira nifa ince danaga yarinyar na rasa ina na san me
kama da ita .
Yarinyar fa wajen Sakina ce sakina dai wacce
sakinar Saliman ki fa karfa kice tun abin da ya faru ba'a zuminci ke wace
Sakinar kar kice mun yayar Salima eh ita fa innalillahi wa'inna ilahi raji'un
to ai yaron Deeni ne ɗan
wajen Salim Haj. Ubaida ta zaro ido na wajenta eh subhanallah anso ayi kwaɓa aibabu aure tsakaninsu.
Ya akai aka ɗaura
maza basu fahimta eh to kinsan mahaifin yarom beje ba itama na yarimyar baijeba
to da madatsala shi ya sa nace suyi bincike suƙa ƙi inji Haj. Ubaidah kinga ban ga ta zama
ba daman gurin Sakinar zani zan amso abu sai insanar mata inui Haj. Ubaida ɗin nima kinga bari mu koma
asan abinyi tun kan duniya ta ɗauka
an ɗaura auren Yaya da
ƙanwarsa...
[10:42 am,
10/10/2023] Faɗima
Fayau: Binto
1
Da sunan Allah
me rahma mejin qai.
****
Tunkinta take
cikin kwanciyar hankali dan har sakin murmushi take lokaci zuwa lokaci kai ka
ce ba'abin da ke damunta cikin duniya,motar kanta abar kalo ce.
Kamar wadda
aka ce tai unguwar kawai ta murda sitiyarin motar zuwa unguwar dorayi, nima dai
yau bara inga ya dorayin take ta fada aranta.
Titin qonannen
gidan mai tai wanda yai har yan babura ahankula take jan motar gurin ya sauya
mata sosai dan ta taba zuwa tun da jimawa, gurin ya sauya sosai ya cika ga
jama'a ko ina.
Matasa ne da
sauran mutane keta hada-hada a dan qaramin titin wasun su hira suke zazzaune
gaban kantunan da ke gefen titin wasu kuwa harkar sa'ar su kawai suke.
Sosai ta qara
rage saurin motar koma ta mance a titi take oho hakan sosai yaja hankalun
matasan dake ta hada hadarsu, wadanda bamasu da niyar kallonta se sun kalle ta.
Kashi tamanin
na masu kallon nata zaginta suke wai su za'ama qaryar mota kadan ne kawai ke
kalla suyi shiru, yayin da wasu ke fatan dama sune da motar.
Dai dai layin
da za ta keta taga wata matashiya gaban kasko na suya mutane sun bai bayeta
yara ko ina na harkarsu, duda batasan me ake soya wa ba jitai kamar ta je ta
siya sosai ta ji sun burgeta ita unguwarsu seka gama yawonka ma baka kowa ba
balle yara.
Idanta ne
yakai kanwata yar matashi goye da yaro wani tana jansa sosai ta ji ta burgeta
dudu yarinyar batafi sa'ar su taslim ba ina ita ce abin da take fada aranta
kenan.
Tazo dedai
mararrabar da ke yan kifi tadan kalla gani tai ba wadda tai mata kawai ta miqe
zuwa unguwar bello, tama mance da yanma tayi tamance da fadan momy tafiya kawai
take hankali kwance.
Unguwar ba ta
kuma birgeta ba seda tashigo unguwar kuka sai take ganin kamar a kauye komai
yai mata dai dai da tsarinta, arayuwarta tana san jama'a kazalika tana san
qauye.
Mai kifin da
tagani gabanta kadan ya sanya tadan faka motar gaba kadan da shi dan tana san
karfashe sosai balle wannan da kamshinsa ya cika mata hanci, gabaki daya idan
yan matansan dake gun kifin yayo kan motar danma basu kula da wadda ke ciki ba.
Bashir ne
tadan bugi tsalha da ke zaune baiko kalli inda motar take ba ya ce kaga wata
shegiyar mota ya dan juya ya kalle ta gami da dan jan qaramin tsaki, Bashir ka
cucen wallahi kasa na baima Uzairu mashin dina jibi yanzu yaqi dawowa kai kuma
kana nan kallon motoci.
Rufe bakin
tsalha da sun kuyar da kansa ga tunanin mashin dinsa yai dedai da futowarta
daga mota, tijjani ya saki wani ashar kut....kai kaga wata halitta tsalha ya
dago yadan kalle ta gami da sakin dariya kai da kake wannan ashar haka in ance
ka kulata za ka iya.
Tijjani ya ce
ban ga fuska bane anman mazaje ai basa tsoron mace duk kudinta ah lallai aiseka
zage kwanji suka saka dariya me kifi da ke ta faman debewa da juyewa ya ce
basshi dai tsalha.
Assalamu
Alaikum ta fada cikin muryarta me sanyaya zuciya cikin zumudi su Tijjano suka
amsa, kifi nake so dan Allah mai kifi yai saurin baro kaskon yana fadin na nawa
ake so hajiya.
Na dubu biyu
da dari biyar ta ce to to ya fada gami da qarawa da manya ko qanana ahadamin
duka dan inji wanne yafi dadi dan gaba.
Yawwa gashi
hajiya anzuba harda gyara tai dariya aiko ba gyara haka za ka ce da gyara yai
dariya hajiya kenan ta zaro dubu uku ta miqa masa gami da daukan kifinta ta
juya Habu yai saurin miqa hannu zai amsa kawo akai miki ya ce tai dariya a'a
basshi na gode.
Hajiya
canjinki inji mai kifi ta juyo No basshi kawai nagide ai zan dinga zuwa naga
guri kodan adinga samin gyara ta fada cikin yanayin barkwanci mai kifi ya hau
godiya,Tsalha da tun dazu bai dago ba yai saurin dagowa danjin anbar har dari
biyar kodai kunnensa ne beji dedai ba.
Dagowarsa tai
dedai da juyowarta wanda hakan yabasu damar kallon juna nadan sakanni taja
qafarta tabar wajen.
Kai tsaye gida
ta nufa se yanzu hankalinta ya koma gida tasan tabbas za ta sha fada gurin
Mommy yayin da gefe daya kuma zuciyarta ta cika taf da tunanin matashin
saurayin da ta gani gurin me kifi wanda batasan komi kansa ba ko sunansa bataji
wani ya kiraba.
Tai sa'a mumy
ba ta nan taslim qanwarta ke fada mata tun rana momy ta tafi unguwa dadi ya
cikata kashedi tai ma qannen nata sannan tai daki.
Saida tai
wanka tai sallah ta hau kan dinning za ta fara cin abinci sannan tama tuna da
kifinta.
Kadija qanwarta
ta kira dje kinga na sayo kifi na mance shi a mota pls jeki ki dauko mun ki
dumamamin shi a oven.
Kai yaya dan
Allah waike baki da aiki sai wahalar da mutane ina ba akwai kifin agida ba shi
ne zaki sayo wani wataqil ma kwantai ne, na ji ni maza jeki ki dumama min shi
ki raba biyu kashi daya kibaima taslim tamin miya dayan ki dansa yai zafi ki
kawon kidan yanka masa albasa.
Ta turo baki
ni wallahi na gaji gashi kuma an bamu aiki a sch kuma da yawa Binto tai dariya
indan aiki ne ki kawao in miki, ba ta kuma cewa komi ba ta dau makullun motar
tai waje rai duk abace.
Abincin ta hau
budewa sakwara ce miyar ajuji dadi ya cika ta best food dinta kenan ba ta jira
komi ba tahau ci.
Jin shiru
kadija ba ta kawo kifin ba ya sa Binto miqewa tai waje wataqil ma ba ta je ta
dauko ba, baya motar da alamu tama barshi ya gama qonewa tana can tana kallon
indian da ta saba ta fada cikin ranta da sauri tai kitchen din.
Ga mamakinta
su ta gani sunyi rashe rashe a qas suna cin kifin salame na gefensu suna miqa
mata kai da qaya se yar tsoka insun ga dama.
Haushi ne ya
cika ta ta ce oh kwantan kenan kike ci ko inda yai dedai da lunkuma wata
qatuwar tsoka da kadija tai abaki cikin irin murya ta wanda yake cin abinci ta
ce kai yaya wannan wane irin kifi ne kwai dadi wallahi.
Taslim ta ce
kema ai fade kike dadinsa ba'a magana salame dake gefe itama cikin muryarta ta
yan qauye ta ce danma ba kansa kuke ci ba sauri binto tai ta dauke farantin da
kifin ke kai tai waje.
Biyota sukai
suna roqon ta temaka ta basu hakan yai dedai da shigowar momy mene hakan kike
gudu kamar wata yarinya ta fada haba momy na siyo abu dan inci anman yarannan
sun zauna suna cinye min shi ne na dauko abuna.
Eyye banda
shirme duk kifin dake gidannan sekin sayo wani momy dan baki ci wannan bane na
daban ne inji taslim.
Dady(qaramin
qanunsu me sunan kakansu) ya ce nima zanci wallahi Binto taja tsaki Allah yan
gidan nan kwadayayyu ne, momy ta ce eyye karki qara cemusu kwadayayyu kya siyo
abu kice bazasu ci ba inkinsan bakya san bawa kowa ki dinga cinyewa a waje.
Muji irin
kifin inji momy din ta dauki guda ta fara ci momy da ke faman mitar akwai kifi
agida se gashi ta cinye ta kuma dauka ta cinye ta kuma dauka ganin za ta cinye
ya sa Binto dauke abinta tai daki dady yabi bayanta kan ta dada masa.
Zonan dady
inji Momy kyaleta in ta ajiyema Abbanku sai ya baka kasan halinta duk girman
nan naka bataqi ta dakeka ba yai dariya maza jeka ka daukon abinci na bazan iya
zuwa dinning ba to ya ce ya miqe.
Sai da hajiya
ta cika cikinta da abinci ta dubi taslim ta ce taslim wai yaushe yayarku ta
dawo, Taslim tadan muskuta gami da cewa ai mum baki dade da fita ba momy tadan
kalle ta kamin ta ce ok duda ta gano qarya take.
Jin tsaiwar
motar Abbansu(me gidan) ya sa duk sukai waje har ita momy din kamar koyaushe
binto ce ta amso kayansa tana manne jikin baban nata dan sunfi shaquwa da shi
kan kowa a agidan suka rankayo sukai ciki cikin farin ciki kamar koyaushe.
Tun da Abban
ya gama cin abinci ake labarin kifi kaini na banu ya fada wannan wani irin kifi
ne Kadija ta miqe tai kitchen ta dauko wanda binto ta ajiye masa a oven tana
tafe tanaci.
Wata uwar
harara Binto ta aika mata tai saurin dauke ido gami da mai da kifin ganin
binton ta dauke ido yasata saurin dauke abinta gami da hadawa da wani dan
qarami.
Abba kaji
irinsa inji kadijan kai nifa abin da harkar qarni kun sani Binto ta dan ba ta
fuska irin na shagwaba Allah Abba da dadi ya amsa yafara ci.
Binto wai a
ina kika sayo kifinnan tai saurin cewa lah Abba a dorayi ne Momy ta saka salati
yanzu Binto bakyajin kunyar qarya dazufa a gadon qaya kika ce hanyarki ta
dawowa daman na san baki dawo da wuri ba duk kinbi kin koyawa yara qarya.
Kunya ce duk
ta rufe Binto sin sin ta miqe tai dakinta momy da dady suka kalli juna sukai
murmushi tabbas yaransu sun shaqu dasu sosai ta yadda ko yaya sukai abin rashin
gaskiya basa buqatar su taresu se sun fada musu suna zaune zasu fada in hira
tai dadi.
Tun bayan da
ta hada kayan lecture dinta na gobe tai nafilfulunta ta fada gado danyin bacci
sai daime tafi awa biyu a kwance baccin yaqi zuwa ranta zuciyarta da idanunta
cike yake da tunanin matashin saurayinnan da tagani gurin me kifi a dorayi
idanunta sun bushe babuma alamar bacci a tattare da su.
Ta dade
akwance qannenta su taslim suka zo basu fi minti goma ba ta fara jin saukar
numfashinsu alamar sunyi bacci.
Duk yadda taso
cireshi aranta ta kasa adazun tayi zaton kamar da ne in taga mutun me kyau ta
ji tana sansa saidai ba ta ta6a kasa bacci kan tunanin wani ba sai yau.
Wayarta ta
dauka ta kunna data tuni messages suka fara shigowa ta WhatsApp yawanci na Isma'il
ne duk na neman soyayyarta tsaki taja gami da fita daga WhatsApp din tai
Facebook nan dinma shi ne aranta tai tsaki ta koma Instagram tahau duba hotunan
mutane da gajerun videos.
Batafi minti
biyar da shiga insta dinba saqon Isma'il ya shigo taja tsaki gami da kashe
datar can kuma hawaye ya biyo kuncinta itakanta ta rasa meke damunta tarasa me
ya sa indai namiji zaice yana santa sai ta dinga jin haushinsa anman zuciyarta
se ta dinga hango mata wasu daban itaman zuciyarta ba ta mata adalci ba ko kadan.......
Pls vote,
Comment and
Share.
Binyo
F.A.Ya'u
****
Batasan
sa'adda bacci ya d'auketa ba tana can tana ta saqe-saqen shirme, sai kiran
asuba ta ji koda ta idar da sallah bacci ta koma da yake yau ba ta da aji da
safe, Sai wajen goma ta farka.
Agaggauce tai
breakfast sannan ta shirya tsaf ta fito cikin shigarta ta hausawa atamfa ce
green super wax ba wata kwalliya tai ba sedai tayi kyau sosai salma taima mum
ta fice.
Tana fitowa ta
ci karo da yaya Isma'il yana shirin shigowa tana ganinsa ta had'e fuska yayin
da shi kuwa bawan Allah gabaki d'aya ya tattaro fara'arsa guri guda adan qagare
irin na wadda aka takurawa ta ce yah "Barka da safiya" dadi ya cika
shi ya amsa lafiya qalau qanwarmu.
Yadda yaketa
wani washe baki ya qara ba ta haushi ta rasa me ya sa shi baya fishi ko kadan
duk abin take masa se ka ce ba jiya ne ba taga saqunansa sunfi aqirga ba taqi
amsa masa ko daya anman duda haka ko ya nuna yaji haushi.
Katse mata
tunani yai da fadin "qanwar anfito ne" tad'an ta6e baki gami da
turoshi ta ce "eh" to ko inzo inkaiki" ya fad'a tai saurin cewa
a'a basshi kawai ai kaima kana da abinyi yai dariya ganin yadda tai din
"to aini ba ni da wani aiki da ya wuce naki Allah."
Wayyo ni na
shi na take fad'e cikin ranta ni wallahi da yah ba d'an uwana bane da se ince
maye ne duk cikin ranta take magana bama tasan ta fito fili ba ya sa dariya to
ai sani ne bakiyi ba tuni na zama mayen saurin toshe bakinta tai tayi waje
kunya duk ta rufeta shi kuma yai ciki yana dariya.
Tana tafiya a
mota tana dariya wato maganar zuci kan iya fitowa fili kenan.
Yau lecture
uku take da ta kammala biyu ta ukun sai yanma wajen uku hakan ya sa ta garzaya
matattararsu ta yan bautar qasa da yawa suna wajen maza da mata yadda ake firar
ne yad'an d'ebe mata kewar matashin da ta gani jiya ad'orayi wanda ta kasa
cirema ranta tunaninsa mintina kadan kamanninsa kan fado mata rai.
Ba ita ta fito
daga F.C.E ba sai wajen biyar saura hakan ya sa take ta sauri dan ta je gida
domin tana san ta had'a questions d'in exam da aka ce ta kawo na students din
da take dauka ta yunwa da take mugun ji.
Batai aune ba
ta hange su daf da ita suna qoqarin tsallaka titi duk yadda taso kauce musu ina
dan gudu take sosai da gudu sauran suka tsallake yayin da dayar ta tsaya diri
diri yayin da akai rashin sa'a sai da ta bugeta.
Hankali tashe
ta fito daga mota ganin yadda jini ya malale gurin yasata fashewa da kuka
kasantuwar yanma ce ya sa tuni gurin ya cika da jama'a cikin police d'in da ke
zaune nan zone one d'aya ciki ta taso ya d'auki yarinyar yasata cikin motar tata.
Yaran da suke
tafe tare biyu ciki suma ya ce su shiga dan suje suga inda za a kwantar da ita
yayin da sauran ya ce su je gida su fad'a.
Kasa tuqa
motar tayi kuka kawai take dan ita ko kad'an batasan taga jini irin mutanen
nance da suke da blood phobia police dinne ya amshi key din yau driving seda ya
hau titi ya ce wani asibiti za mu ta ce Nasarawa.
Suna zuwa aka
amshe ta sabida sunzo da police sa'annan da dama cikin ma'aikatan sun saba da
binto sosai, temakon gaggawa aka baima yarinyar seda binto ta tabbatar ta fita
daga danger hankalunta yad'an kwanta, se asannan ta kira mum ta fad'a mata.
Bada jimawa ba
mum ta iso ita da yah isma'il da abinci se asannan Binto tama tuna wai d'azun
yunwa takeji sosai taci sannan tai sallah ta zauna tana kallon yarinyar.
Yarinya ce
qarama batafi shekara goma ba anman sabida tsabar rashin kula ace an turota
tallah ta dubi sauran yan mayan da suka tawo tare daga ina kuke zuwa nan?
Bilki ta ce
daga garu Binto tadan zaro ido inane garu kuma sukai dariya qauye ne can ta ce
yakai fanshekara sukai dariya ai gaban nan ne sosai towo to me kuke siyarwa
nidai Gyad'a ce inji Bilki.
Au ba abu daya
kuke saidawa ba eh kowa da abin da yake saidawa ta6 kunqi cin abincin fa suka
kalli juna alamar tsoro.
Daqar tasha
kansu suka ci, sai bayan isha ta kira Toli qawar service dinta ta roqeta kan
gobe ba za ta iya shigowa da wurwuri ba za ta turo mata questions din ta
WhatsApp ta temaka ta mata submitting.
Washe gari da
safe bayan kadija ta kawo musu abinci dan Binto qin tafiya gida tai anan ta kwan
shi ma isma'il qeme-me ya ce ina yana nan bayan sun karya ta ce kadija ta zauna
da kubra ita kuma za ta sauke Bilki ahanya seta je gida ta fadi inda suke dan
tasan yanxu hankali duk ya tashi.
Haka kuwa akai
a malan qato ta sauke Bilkin ita kuma tai gida dan shiryawa ta tafi sch dan
tasan yanzu an kusa shiga exam din tata.
Bata wani jima
a gida ba tai makaranta dan tana san ta je taga komi yana tafiya dedai.
Ko da Bilki ta
isa gida tun abakin titi ta hangi jama'u tsububu ana jiran ganin ta ina zasu bullo
yayin da iyaye mata hankalinsu ya tashi sosai dan zatonsu ko an sace su duka
ukun mahaifiyar bilki na hangota ta share hawaye gami da yo wajenta haka ma
mahaifiyar sahura tambaya take ina sahun take.
Nan ta zayyene
musu komi harda qarin bayani kan lefin tsahare ne sunyi sunyi su jata ta maqale
kunsan ita wani irin hali gareta.
Iya aikin san
asibitin nasarawa ko Tsalha ya tambaya eh ba inda Salamatu ta kwanta ba eh
nanfa to ku tawo keda umma Bilki inyaso se in d'auki Bilki a mahin d'ina muje.
Anman ai ka
bari ta ci abinci ko inji ummanta Bilki tai saurin cewa wa ni Yau dai kam na
qoshi da abincin daza abinci mukaci me rai da lafiya ni binsa zan yi ko nasamu
na dare tana fad'e tana d'ane mashin d'in baice komi ba yaja zasu tafi.
Kasan asibitin
da girma ina za mu ganku iya tai saurin tambaya ya ce kinji ta ce emergency to
inda aka fara kai Salamatu kafin asauya mata guri oh oh na ji seka bamu kud'in
mota yazaro dubu uku ya miqa mata gami da jan mashin d'in dan yanzu se ta ce
bai isa ba shi kuma dubu biyu suka rage masa kar yaje ko se yasai magani.
Binto ba ta
jima a sch ba ta tawo ana gama papers din yan NCE one ta kamo hanya kai tsaye
asibitin ta wuce.
Ko da ta dawo
cewa kadija tai suje gida ita da sahura tayi wanka kafin Bilki din ta dawo.
Ganin mara lpy
tata na bacci ya sa itama ta d'an kishin gid'a bakin gadon tuni bacci ya
d'auketa.
Tun da Sahura
ta shiga motar take zuba qauyanci ta kalli can ta ta6a can dan ba irin motar da
suka saba shiga bace.
Bata qara
sakin baki ba saida suka shiga gidan tamfatsetsen gida ne na qin qarawa nan dai
kasa shiru tai seda tai magana ca6d'i ta ce kadija ta ce mene gani nan mu ahe
gidajen da muke zuwa talla mugansu na gayu ahe ba komi bane.
Kadija tai
dariya kawai sahura ta kuma qarawa mu kan ahe a dajin Allah muke kadija ta
sheqe da dariya kai sahura baki da dama kam.
A hankula
Bilki ke ta6a Binto da ke bacci ta bud'e idanunta alamun me bacci da sauri ta
ware su sosai gani fuskar da tun da ta ganta ta kasa sukuni arayuwarta sai take
zaton mafarki take hakan ya sa ta mai da idanunta ta rufe da zummar ci gaba da
baccin ta.
Bilki takai
hannu za ta kuma tashinta Tsalha ya ce kyaleta bacci ne a idanta tabbas muryar
namiji ta ji hakan ya sa tai saurin tashi gami da gyara zama tad'an saki fuska
gami da fadin sannu ko ga guri ta nuna masa daya kujerar da ke gefen gadon
tsahare.
Shuru suka
zauna na tsawon lokaci ba wanda ya ce da kowa komi yayin da Binto take da
abubuwan fad'e da yawa kwarjininsa ya hanata fade.
Ahankula
tsahare ke bud'e idanunta da saure ta bud'esu ganin ta d'orasu kan tsalha dake
zaume gefenta cikin qaraji ta fada Baba da sauri shi ma ya qarasa Tsahare kin
farka sannu yarinyar ta fara kuka Baba qafata.
Hankalin binto
tuni ya tashi wato ma yanada aure harda yarinya Ni kam nashi na.....
[10:42 am,
10/10/2023] Faɗima Fayau:
Binto
2
****
Ta farka abin
da ya ce da ita kenan tai qoqarin danne damuwarta kamin ta ce bari in kira
likita ta miqe gami da yin waje jiki ba kwari.
Sun dawo ita
da doctor ya dubata ya ce ba wata matsala asannu a hankali za ta warke ok
doctor za ta iya cin abinci binto ta tambaya eh why not ya ba ta amsa binto tai
waje ina zuwa ta ce musu.
Yau ba kowa
gurin tsahare umma bilki dake gunta ta fita alwala sai binto tana ba ta abinci
nan cikin dabara take tambayarta alaqarta da mutumin nan me zuwa kullun ta ce
ai Baba ne binto ta kuma mai-maitawa aranta kamin ta kuma tambaya to ina
ummanki naga ba ta ta6a zuwa ba ita.
Tsahare tadan
sunkuyar da kanta ta ce ai bazata zo ba Binto tai saurin cewa sabida me bazata
zoba ai nice yar fari inji tsahare awwo.
Hawaye tagani
idon tsahare mene na kuka kuma umma ta na tuna ni banma san ta ba kamar ya
bakisanta ba inji binto aita mutu tun ina qaram ayya Allah ya jiqanta.
Dan zaman
tsahare a asibiti sun saba sosai da binto wadda take kira aunty haka shi ma
baban nata wato tsalha sun saba sosai dan sukan zauna suyi hira sosai yake
jinta aransa musanman ma yadda yaga tana kula masa tilon yarsa.
Abu kamar wasa
saiga shaquwa mai tsanani ta ta shiga tsakanin Binto da tsalha sun saba sosai
wanda har gidansu yake zuwa su sha hirarsu duda an jima da sallamar tsahare dan
ta warke sarai.
Wasa wasa sai
ga soyayya mai qarfi ta shiga tsakaninsu irin wadda turawa ke kira da pure lada
ada tsalha ya dauka bayan mutuwar salame matarsa bazai ta6a san wata mace ba.
Baima yi
tsammanin zai iya kula wata macen ba sai gashi yanzu yana jin Binto aransa
sosai fiye ma da ita Salamen.
Ita kanta
Binto jinsa take sosai aranta gani take inbata aureshi ba bazata ta6a jin dadin
aure ba bama tajin za ta iya auren wani ba tsalha ba, duda dai jama'a suna kallonsa
dan qauye bagidaje ita kuwa tasan tsalhanta na dabanne ya iya soyayya sosai ya
san takan mace ya kuma san ta yadda zai yi taso shi indai har za ta saurareshi
to zatasoshi duk matsayinta.
Dalhat sunan
da Binto ta sauya mai kenan zaune yake yana jiran fitowarta Taslim ce ta fito
suka gaisa dauke da turen lemo da ruwa ta ce kadan yi haquri gatanan ok bakomi
ya ce tai ciki.
Bata jima da
shiga ba Binto ta fito sanye take da shigarta ta gado wato riga da zani na
atamfa super wax me yarfin ja batai wata kwalliya me yawa ba tai kyau sosai
musan man a idon tsalhanta tun da ta fito yake kallonta yayin da ita kuma ta ke
sakin murmushi.
Binto ba wata
me kyau bace Baqa ce sosai mai matsakaicin tsayi dan ba ta cikin dogaye haka
babu me kiranta qajera ita din mace ce me yawan sumar gashi wanda bai cika
laushi ba wanda mutane kan kira da gashin Hausawa saidai ita nata yanada tsayi
sosai wanda kuma ya zo har gaban goshi.
Bata da qiba
saidai baza'a kirata da ramammayiya ba ita din mace ce me yawan tsafta kwalliya
da ado hakan ya sa mutane bama sa ganin muninta ko kadan kunsan ance mace yar
kwalliya ce.
Sai da ta
zauna suka gaisa gami da tambayarsa diyarsu wato salame dan ta ce yarsa yarta
ce.
Suna zaune
suna hira yaya isma'il yaxo zai shiga ciki duda yagansu yai fuska danshi inda
abun da ya tsana to be wuce ganin binto da wani ba.
Da sauri ta ce
Yah ya juyo yama mance da kishin da yake danshi din yana san yaji ta masa
magana shi kadai ya san dadin da yajeji aransa.
Daf dasu ya zo
na'am qanwar ta gaidashi cikin fara'a shi ma sosai ta masa kyau se ma ince fiye
da yadda taima Tsalha kyau.
Dalhat ga yaya
na ku gaisa ta ce da tsalha cikin girmamawa ya gaida Isma'il din duda kuwa zasu
iyayin sa'anni.
Tace yah ga
Dalhat shi ne mijin da zan aura yadan kalle ta araze ta kuma mai maitawa to to
masha Allah ya fada Allah ya sa albarka ya sa za mu gani suka amsa da amin.
Can isma'il ya
ce to a ina yake kafin tsalha ya ce wani abu ta ce agaru yanama da yarinya daya
mahaifiyarta ta tasu oh Allah sarki Allah yajiqanta suka ce amin bari naje ciki
ko inji isma'il din.
Yana shiga ya
bille ta qofar baya yai garden din gidan jiri na daukansa duk dauriyarsa kasa
daurewa yayi ya fashe da kuka sosai yake san Binto har cikin ransa yakuma san
kowa zai aura bazai ta6a dena san ta ba.
Seda yai kuka
me isarsa har ya godema Allah ya miqe yaje ya wanke fuskarsa gami da samin guri
ya zauna dan ya san yanxu in yafita da matsala dan har lokacin be dena jin jiri
na dibarsa yayin da can ransa yake jin wani irin baqin ciki na taso masa
wayarsa ya dauka yahau karatun alqur'ani.
Binto ce zaune
tana sana'ata wato karatun novels khadija ta dubeta yaya wai yaushe zaki kuma
siyo mana irin kifinnan me dadi Binto ta dan kalle ta aiko yau ma ta ajiye
littafin ku tashi muje suka sa ihu duka yee that's our babbar yaya .
Kai ku tsaya
to dama kudunwa kuke nufi suka marai raice haba babbar yaya aikinsan da kudinki
muke nufi ta koma ta zauna ta6 ka ce zaku mutu baku ci kifi ba.
Mum dake zaune
tana jinsu ta ce haba kekuwa yayan duwa inbaki siyawa yan qannenki ba wazaki
siyawa ta turo baki kai momey sunfa fini kudi aike babbace babba juji inkinayi
se su koya ta6 nidai ba ni da kudi.
Taslim ta ce
to zanbada 1k seki cika to yawwa se yanxu na ji batu ku tashi mu tafi ta zari
mayafinta mum se mundawo.
Suna saukowa
talon qasa inda TV ke akunne binto na kallon ta taja ta zauna wallahi bazani ba
drama din data fi so ake Saloni wai yaushe ma suka fara maimaita shirin nan duk
qannen sukai mata banza gami da komawa sama suna qunquni gami da Allah ya isa
ga wanda yabar TV din akunne.
Tsalhane zaune
yana jiran fitowar Binto hankalinsa duk atashe dan jiya ta kirashi take fada
masa Abbansu na san ganinsa hakuma komi ya ke daga masa hankali ba sai sanin
matsayinsu dana binto ba daya bane ba kuma ko wani mai kudi irin na Binto bane
zai bada diyarsa ga talaka irinsa.
Satin da ya
wuce da ya zo gunta kan jirkitaccen tsohon mashin dinsa duk yai futu futu da
shi kayansa duk sunyi qura gashin kansa jar qasar garinsu ta rineshi zuwa ja
mahaifinta ya fito zai fita yana sauri ya taddasu tana zuba masa ruwa yana
wanke qafa.
Da alama sauri
yake yakan ya sa sama sama suka gaisa kamin ya ce Binto waye wannan din tadan
sauke ido qasa Abba shi ne wanda nake baka labari yai saurin qara kallonsa
sosai kamin ya ce ba laifi ya shige mota, baifi minti biyar ba ya dawo yai ciki
tana Abba ya kadawo da wuri haka yai mata banza haka da zai kuma fita bai amsa
ada lafiyar suba.
Ji yake kamar
cewa mahaifin binton zai yi ya fita harkar diyarsa gashi shi ayanzu yana jin
rabashi da binto kamar rabashi da ransa ne san ta a ruhinsa yake.
Tsoronsa kar
iyayanta su hanashi ita duda bazai ga lefinsu ba matsayinsu ba daya ba ita yar
birni shi dan qauye ita yar masu kudi illimi gamida mulki shi ba dan kowan kowa
ba wanda aqauyensu ma ba kowa ya san dasu ba.
Ita yar boko
wadda har takaiga kammala degree dinta yayin da shi secondary dinma daqyar ya
kammala baida wata sana'a sama da noma se dan acabar da yake tabawa shi ma iya
qauyensu ya san baushe ma kance qwarya tabi qwarya sedai shi so da qaunar Binto
ta hanashi kallon tarin banbancin dake tsakaninsu balle yai tunanin kwarya tabi
kwarya din.
Binto
F.A.Ya'u
****
Asalin Binto
Alhaji mahmud
Hashin shi ne sunan mahaifin Binto haifaffen garin kano ne awannan unguwar mai
dunbin tarihi da ta hadar da manyan mutane kama daga professors, Doctors da
manyan yan kasuwa.
Su takwas
mahaifinsu ya haifa shi ne na shida gidansu ma na sahun jerin masu karatun boko
kaf gidan babu wanda bai boko ba.
yayyensa mata
biyu se maza biyu sauran qannensa duk maza ne se autarsu mace.
Lokacin da yai
kammala degree dinsa ne ya hadu da karima wadda sika qulla soyayya bada jimawa
ba aka daura musu aure.
Auransu aurene
na jin dadi gami da kwanciyar hankali se irin dai matsala da dole in an hadu
mutun biyu za a samesu anman da yake duk su biyun sun san me suke babu wanda ya
ta6ajin kansu.
Aurensu da
shekara daya karima ta haifi yaronta namiji abinka da masu bin al'ada duda
bokonsu aka saka a cirema yaro beli sedai yaita zubar jini bai kwanba ya mutu.
Haka haihuwa
ta biyu shi ma da aka ma yaron kaciya basu zo gida ba yaro ya koma alokacin
suka gano ashe haemophilic suke haifa.
Lokacin suka
tada hankalinsu sosai hakan ya sa yayan Alhaji Mahmoud ya ba shi dansa ganin
yadda suka damu mafarin dawowar Isma'il gidan kenan.
Ahaihuwa ta
uku ne suka haifi mace wadda taci sunanta Binta wadda suka dauki san duniya
suka dora mata haka shi ma isma'il murna sosai dan yayi qanwa lokacin zai shiga
Jss 1.
Komi ya samu
na Binta ne duk kudin makarantarsa ma ya dena kashewa shidai kawai yasaima
Binta kayan wasa.
seda tai shekara
shida suka haifa mata qani wanda take sansa sosai.
Lokacin
Isma'il zai shiga level 1 yana da shekara goma sha shida cif wanda alokacin ita
binta za ta shiga primary 1, qanin ta Bashir wato jaririn da aka haifa sosai
suke sansa ita da isma'il se arasa wanda yafi sansa.
Danma in yan
kishinta suka motsa setace ina bazai dauki isma'il ba se ita haka zaitai mata
doki tanama jaririn qwalo.
Shekarar
Bashir uku Binto na shekara tara hartayi jarrabawar tafiya qaramar secondary
jira kawai ake ta fito ta fara zuwa.
Tun Binto nada
shekara bakwai lokacin Isma'il na level 2 ya fara san ta sedai shi kansa baida
tabbacin wani irin so yake mata ba akullin zatonsa sone irinna dan uwa da dan
uwa.
Bashir shi ne
bai iya fadin binta ba cikin gwarancinsa yake kiranta da Binto tun bataso har
sunan ya bita.
Bashir be cika
shekara Hudu ba aka haifi taslim batai shekara biyu ba aka haifi kadija.
Binto na Ss 2
lokacin isma'il na shekarar qarshe akaratun likitancinsa alokacin tuni ya gama
gane haqiqanin wani irin so yakema yar qanwar tasa sosai yake san ta duniya ba
shi da wani tunani se nata.
Yayin da ita
kuwa aduniya wani malaminsu ke burgeta sosai sedai shi din kokadan babu baqar
mace a tsarinsa danko amsa in baqace ke bama zai nuna kiba balle ki amsa.
Lokacin da ya
dena zuwa ne ta gane basansa take ba burgeta kawai yake.
Haka rayuwa ta
cigaba da tafiya isma'il na mutuwar san Binto yayin da ita kuma zuciyarta
akullun ke hango mata wasu daba.
Binto ba ta da
wata qawa ko aminiya sama da isma'il yayanta komi da shi suke haqawa su binne ba
me ji duda zurfin cikinta baisa koda dawasa ta taba fadawa masa gawanda takeso
ba hakan yai masa dadi dan ya san kenan ba ta kula kowa.
Lokacin da tai
candy yabayyana mata burinsa nan tai fur ina ita batasan zanceba babu ta yadda
za'ai ta auri yayanta cewarta kallon sibling dinta take masa babu batun aure
tsakaninsu.
Tun bai damuwa
yana zaton yarinta ce har kawo yau da take nuna masa wani matsayin mijin
aurenta da zuciyarta tai mata zabi ji yake kamar zuciyarsa za ta fashe.
Cigaban labari
Da fara'arta
ta qaraso inda tsalha yake cikin barkwanci take fadin kaidai kaqi zama dan gida
kullin kazo seka tsaya afarfajiya yai dariya ai wataran dai zan shiga in huta
da gorin nan tai yar dariya gami da dan rissinawa ta gaidashi ya amsa cikin jin
dadi.
Yana daya daga
abin da ke qara masa sant shi ne girmama mutanen isso tai masa zuwa dakin
mahaifin nata.
Cikin mutunci
ya amshe shi suka gaisa yai dan masa tambayoyi abinka da masu illimi awayance
ya kammala nazarinsa kan tsalha tuni ya gano mutumin kirkine matsalar sa kawai
talauci toh malan tsalha ka iya tafiya zakaji komi gurin ita binto din yamiqe
yana godiya ya fito.
Yadda
mahaifinta ya amsheshi ya gano inda ta gado karamci ko kadan bai wani nuna masa
kyama ba ko irin danme zai ce yana san yarsa duda baice masa yabashi ko zai ba
shi ba sai yake jin fargabarsa da yawa ta ragu.
Duk wani
bincike da yakama sunyi babu wata matsala dan tuni ma suka ce sun ba shi
matsalar daya ce ita ce inda binto za ta zauna qauyene gidan yawa ta ce ita ta
ji ta gani za ta iya tuni aka sa bikin wata biyu.
Tuni gidansu
tsalha ya dauka ai tsalha zai auri yar birni yaqi auren yar qauye duk tarin
matan dake sansa na garin.
Ita kuwa
diyarsa murna take sosai dan za ta samu umma musanman ma dataji wace Abban nata
zai aure.
Yan gulma basu
qara tsorata da lamarinsa ba seda sukaga uban kayan lefen da ya hada wanda ko a
auren farinsa be rabinsa ba dan wani dan birnin ma ba lallai ya iya suba.
Umma bilki ta
kirashi ta ce yakamata arage ya ce ina shi inda yanada abin da yafi hk wallahi
shi zaima binto dan ta fi qarfin haka agunsa.
Lokacin da
dangin tsalha suka kai lefe se suka raina abin da suka kai tun daga qofar
gidansu binto yadda suka ga girman gidan tukwicin dubu dari ala basu banda soye
soye.
Tuni qauyensu
ya dauka wata sabuwar gulma wai ana san cutar tsalhane kodai yarinyar tayi
cikin shegene ko kuma yar tsuntuwa ce inba haka wani me kudinne zaikai diyarsa
qauye shidai tsalha ya toshe kunnensa kamar besan anaiba.
Danshi ya san
samun kamila kamar bintonsa sai antona duda kasantuwarta yar birni yar boko
anman su yan qauyen nasu da suke ganin kamar sune masu tarbiyya tafisu sosai.
Yarinya qarama
da batafi sa'ar tsaharensa ba sekaji suna kawo masa hari wai shi takeso wasuma
har girke girke suke masa abin bai fara tsorata shiba seda wasu cikinsa suka
fara kawo masa kansu kan su koda bazai auresu ba suna sansa sosai yake mamakin
yaran hakan ya sa ko kadan bai sakar musu fuska.
Tun saka ranar
Binto isma'il ya tattara yabar nigeria inda ya tafi china dan ya ce yana san
karanta likitancin gargajiyarsu yayinda azahuri kuwa ya tafine dan ya san
zuciyarsa za ta iya tarwatsewa indai aka daura auren bintonsa da wani.
Duk yadda
akaso ya zauna ayi biki yaqi ya ce in time din yayi zaizo yayin da dangi suka
rabu biyu gidansu Isma'il na asali suka haujin yaushin mahaifin Binto kan yaqi
dan uwa yabaima bare.
Sosai family
dinsu suka dau zafi da shi ya ce shifa bemasan da isma'il na santa ba ko kadan
zatonsa shaquwar yan uwantaka ce kawai.
Dayawa cikin
dangi sunce ya fasa baima tsalha yabaima Isma'il ya ce ina shi bazai zama
qaramin mutin ba ko kadan ai tun farko isma'il yai nauyin baki.
Rana ba ta
qarya yau aka daura auren Binto da angonta tsalha biki sosai aka sha na gani na
fade dan kunsan in abu ya hadu tsayawa bada labarinsa qauyanci ne kawai.
Ranar lahadi
da yamma aka dauki amarya se garin garu da yamma liqis aka kai amarya dakinta
bayan ankaita ban gare ban gare aka dawo da ita barinta yayinda yan kai amarya
kowa yaqi zama kowa nafadin ina ai su bazasu iya ko rabin awa aqauyeba.
Haka suka tafi
suka bar Binto amarya zaune ita kadai saman gadonta adakinta da yasha gyara
wanda inkana ciki bazaka taba cewa kana kauye bane.
Rubutawa
Faɗima Fayau
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.