Citation: Maikwari, H.U. & Sani, A. (2020). Tahamisin Waƙaƙƙen Ƙa’idojin Rubutun Hausa. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.
638. In aka sake nunka z can gun ƙarshe,
Z kan rikiɗe a daddage ta a ko cashe,
Nan aka sanya j ta zo a gaɓar ƙarshe,
To ita z idan tana ƙarshe tarshe,
Rikiɗewa takai ta zan mai sauyawa.
639. Cizo,
cije-cije zai zama nunkawa,
Dabba in tana da
haurun cizawa,
Ni ban sanya
hannuwa ko farawa,
An cije ka ba ka ma iya ramawa,
Cizajje dukan su z na juyewa.
640. Murza,
murje-murje shi ne nunkinsa,
Murza ki wuce, ki bar shi nan yai
aikinsa,
Mummurje idonki, Binta ɗauko muna fansa,
Masu ginar gyaɗa suna neman kwasa,
Murzajje cikin gyaɗa sai tamnewa.
641. Darza, darje-darje nan za shi fitowa,
Wanda ya taka
dakkali sai darjewa,
Daddagi z ta sauya j ga rubutawa,
Kalmar nan guda ta
darzan darjewa,
Darzajje da an gama sai bushewa.
642. In ka gane ƙa’idojin ga misalai,
Ƙirƙiro naka sa su dace
tuballai,
Sai ka gina ka
tsara kalma ta wakilai,
Doka ta yi nata
tsari na misalai,
To ka kiyaye
wanda za ka rubutawa.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.