Citation: Maikwari, H.U. & Sani, A. (2020). Tahamisin Waƙaƙƙen Ƙa’idojin Rubutun Hausa. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.
674. Yau harshenmu ya zamo gagara badau,
Ya gagara ya wuce
su shi gagara badau,
Bai da sa’a duk ga
harsuna malam dau-
Re kai nazari ka
san da ta yo fintinkau,
Furce Afirka har ƙasashen Turawa.
675. Bi-bi-si, Amerika ta kama su,
Hausa ake ta yi
matsa kama tasharsu,
Safe da rana har
maraice a tasharsu,
Hausa shirinta ko
da yaushe burinsu,
Jamus sun daɗe da harshen Hausawa.
676. Misra da Makka, har ƙasar Sin sun yarda,
Ta mamayi harsunan
batun har ga jarida,
Kuma ga shi a
zahiri, abin ya kore sheda,
Ba tamka gare ta harsuna tun-tun can da,
Farisa sui riƙo ga harshen Hausawa.
677. Libya tuni Gaddafi ya ce ya yarda,
Al’ummar ya sani
kuma ya shaida,
Sun bunƙasa ga yawa ba su
saranda,
Sun riƙi gaskiya akwai su da
al’ada,
Bai jayayya ya
aminta da Hausawa.
678. Ba harshe guda a Afirka da yak kutsu,
Yas shiga yankunan
ƙasashe yar ratsu,
Al’ummarsa duniya
sun warwatsu,
Harshen Hausa
ko’ina ya warwatsu,
A gidan rediyon
gabas da na Turawa.
679. Rediyo Ghana ba Asante suka yi ba,
Ba wani yare da ya
fi Hausa ake yi ba,
Bayan Ingilishi ba
harshe babba,
Tamkar Hausa ko ba
ka gane ba?
Nijar ba a Zarma
sai dai Hausawa.
680. Senegal Gambiyanmu Mali duka sa su,
Sun yarda da Hausa
ta ci yaƙi na dukansu,
Ta mamayi
harsunansu duk ta kama su,
Sun yi
mubayi’a gareta sun yarda da kansu,
Hausa a Cana ga
Wolof bai motsawa.
681. Birnin Makka can wurin jifan shaiɗan,
An yi muhalli a keɓe don jifar shaiɗan,
Al’ummar duniya ka
taruwa sai ka ga ɗan,
Mutum bisa ɗan mutum suna jifar shaiɗan,
Ga shi ɓato-ɓato rubutun Hausawa.
682. Rasha harsunansu wane a ƙidaya?
Sun yi yawa malam
ka je ka ga aya,
Ga ƙiyasin yawansu sai dai
a yi ƙarya,
Kai na wasusnsu
masu sa manyan kaya,
Duk da hakan ga sun biɗayo na Hausawa.
683. Nan a cikin gida Fulani sun yarda,
Sun lamunta ga
abin nan ga takarda,
Ba su da ja da
Hausa kowa ya shaida,
Sun yi aro gare ta, sun ɗau al’ada,
Sun zama kaɗo tun da nan aka lelewa.
684. Dubi Kanuri ba alanguburo
yanzu,
Can a ƙasarsu Borno komi ya
canzu,
Al’adunsu sun ɓace, du sun cazu,
Harshen Hausa ya
yi ƙarfi can yanzu,
Birnin Yerwa
Hausa ɗai ke haskawa.
685. Yarbawa suna gani an ka wuce su,
An zaka har ƙasar su an zarta su,
Sun saki nasu sun
aje ɗan harshen su,
Al’adunsu Hausa
yanzu du ta canye su,
Badun, Oyo, ga
sarautun Hausawa.
686. Su Igbo sun aminta mun zan zozozo,
Kun san su suna riƙo ga su da ƙwazo,
Sun riƙe nasu, kafin Hausa tac
ci Uzo,
Duba abinci
lokacin da Hausawa suka zo,
Sun bar eba yau
tuwo suka tuƙawa.
687. Inda
gafara nan kar a kiɗe ka,
Hausa gabanka to
gayamin ra’ayinka?
Ka ba da gari? Ko
ko sai an ta da ka?
Ku ka maƙwabtaka da suwa ku ag
ga iyaka,
Yau Neja ina
kwatancin Hausawa?
688. Zarma da Borgu Hausa yau ta taushe su,
An kakkaɓe harsunansu du an kwashe su,
Borgu da Hausa
Zarma ko an zarta su,
Al’adunsu yanzu du
sun ya da su,
Gun suturar jikinsu sun zan Hausawa.
689. Sai shukura mu ƙara gode Ilahinmu,
Ya ɗaukaka Hausa ta zamo tsaninmu,
Ya tattara harsuna
ƙasanta abin sonmu,
Ga mu da godiya ga
Allahu Karimun,
Nasara wadda yaz zubo gun Hausawa.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.