𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalama
Alaikum Malam dan Allah Ina Neman Shawara ni budurwace shakaru 22 amma Allah
bai ba ni mjin aure ba gashi Ina bukatar aure domin Allah ya jarrabeni da
sha'awa ba ni da Burin da ya ce nayi aure dan magance wannan matsalar dan Allah
abani sharawa mai yaka mata nayi koma a yanzuma ko saurayi ba ni da shi asakama
kon matsala ta aljan data hanani samin koda saurayi Gashi Ina fama da sha'awa.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Na tausayamiki
Allah yakawo miki mafita. Shawari shi ne kifara jin tsoron Allah kar halinda
kike ciki ya sa kibiye ma rudin zuciya ki saɓama
ubangijinki. kizama mai yawan ibada da yawan istigfari. Kiyawaita yin azumin
nafila, sannan kidaina karanta novels da zasuke tada miki hankali ko films.
kidaina zama ke ɗaya
acikin ɗaki kina
tunane-tunane, ki dinga fitowa cikin jama'a ana hidima dake musamman lokacin da
kikaga sha'awa na neman damunki, karki yadda rana tafito ta faɗi baki karanta qur'ani ba
domin shi warakane kuma maganine agaremu, kidaina gulmace-gulmace, inzaki kwanta
ki kwanta da alwala ki yi azkar. Kitashi sallah na cikin dare kiroki Allah akan
bukatunki.
Shikuma aure
lokacine ki daure kici jarrabawa in Allah ya kawoshi acikin lokaci qarami
za'ayishi.
Dangane da
matsala na jinnu kuma Kisami ganyen magarya guda bakwai ki dan dakasu ki zuba
ruwa akai sai ki tofa Ayatul ruqya aciki sai ki sha kuma kishafa a jikinki, ki
dinga mai-maita haka lokaci zuwa lokaci.
Kisami man
habbatussauda sai ki haɗasu
daman zaitun da jan miski ki gaurayasu sai ki tofa Ayatul ruqya acikinsu sai ki
dinga shafawa a kowacce gaɓa
a jikinki kaman so biyu arana musamman inzaki kwanta.
Kidinga yi
Alwala idan zaki kwanta Kuma karki dinga zama da najasa a jikinki.
Allah ta'ala
ya sa mudace.
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.