Ticker

6/recent/ticker-posts

Ban Samu Mijin Aure ba Saboda Ina Fama Da Matsalar Aljanu

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalama Alaikum Malam dan Allah Ina Neman Shawara ni budurwace shakaru 22 amma Allah bai ba ni mjin aure ba gashi Ina bukatar aure domin Allah ya jarrabeni da sha'awa ba ni da Burin da ya ce nayi aure dan magance wannan matsalar dan Allah abani sharawa mai yaka mata nayi koma a yanzuma ko saurayi ba ni da shi asakama kon matsala ta aljan data hanani samin koda saurayi Gashi Ina fama da sha'awa.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Na tausayamiki Allah yakawo miki mafita. Shawari shi ne kifara jin tsoron Allah kar halinda kike ciki ya sa kibiye ma rudin zuciya ki saɓama ubangijinki. kizama mai yawan ibada da yawan istigfari. Kiyawaita yin azumin nafila, sannan kidaina karanta novels da zasuke tada miki hankali ko films. kidaina zama ke ɗaya acikin ɗaki kina tunane-tunane, ki dinga fitowa cikin jama'a ana hidima dake musamman lokacin da kikaga sha'awa na neman damunki, karki yadda rana tafito ta faɗi baki karanta qur'ani ba domin shi warakane kuma maganine agaremu, kidaina gulmace-gulmace, inzaki kwanta ki kwanta da alwala ki yi azkar. Kitashi sallah na cikin dare kiroki Allah akan bukatunki.

Shikuma aure lokacine ki daure kici jarrabawa in Allah ya kawoshi acikin lokaci qarami za'ayishi.

Dangane da matsala na jinnu kuma Kisami ganyen magarya guda bakwai ki dan dakasu ki zuba ruwa akai sai ki tofa Ayatul ruqya aciki sai ki sha kuma kishafa a jikinki, ki dinga mai-maita haka lokaci zuwa lokaci.

Kisami man habbatussauda sai ki haɗasu daman zaitun da jan miski ki gaurayasu sai ki tofa Ayatul ruqya acikinsu sai ki dinga shafawa a kowacce gaɓa a jikinki kaman so biyu arana musamman inzaki kwanta.

Kidinga yi Alwala idan zaki kwanta Kuma karki dinga zama da najasa a jikinki.

Allah ta'ala ya sa mudace.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments