Ticker

6/recent/ticker-posts

Karɓar Kuɗin Miji Ta Hanyar Dabara

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum. Malam, barka da safiya. Tambayata ita ce: Mace ce mijinta ya kauce hanya (ta kama shi da mace). To, shi ne take bin hanyar da ta san za a iya bi don ta katange shi daga wancan mummunan aikin. Shi ne take yi masa dabaru domin karɓar kuɗi a wajensa, wani lokaci ma takan ɗaukar masa kuɗi kamar N500, ta cika ta sai turaruka masu tsada. Malam to, wannan abin da take aikatawa, shin ko tana da laifi?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salam warahmatullahi Wabarkatuh

Wajibinta ne da ma tun farko ta ɗauki dukkan matakan da suka halatta domin kare mijinta, da hana shi aikata irin wannan ɓarnar. Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

مَنْ رَآى مِنْكُمْ مُنْكَراً فَلْيُغَيِّرْهُ بِيَدِهِ ، فَإِنْ لَمْ يَسْتَطِعْ فَبِلِسَانِهِ ، وَإِنْ لَمْ يَسْتَطِعْ فَبِقَلْبِهِ ، وَذَلِكَ أَضْعَفُ الْإِيمَانِ

Daga cikinku duk wanda ya ga wani abin ƙyama to ya gyara shi da hannunsa, idan kuma ba zai iya ba to da bakinsa, idan kuwa ba zai iya ba to da zuciyarsa, kuma wannan ne mafi raunin imani.

Amma yin dabara, wadda ta haɗa da yin ƙarya, ko yaudara, ko sata, ko barazana, ko dai wata dabara, domin samu ko karɓar kuɗi daga gare shi, wannan kam bai halatta ba. Kuma ba shakka, wannan matar tana da laifi a kan haka, har sai ta tuba, kuma ta nemo amincewarsa da yafewarsa. Wannan ya zama haka ne, matuƙar dai yana ɗaukar nauyin biya mata  haƙƙoƙinta da suka hau kansa gwargwadon hali da ikonsa.

Idan kuma ba ya sauke haƙƙinsa ne saboda mummunar ɗabi’ar rowa ko makamanciyarta, to a nan ne Malamai suka yarda cewa za ta iya ɗaukar abin da zai yi daidai da buƙatarta da na ya’yanta, saboda Hadisin Hindu matar Abu-Sufyaan (Radiyal Laahu Anhumaa).

 WALLAHU A'ALAM

Sheikh Muhammad Abdullah Assalafiy

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/JoWs3feDfdyGE9yBsa1RSC

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments