Babi Na Ɗaya
Gabatarwa
1. Har kullum da nai nufin faro furci,
To Allah ke a
fari Sarki Majiɓinci,
Na kiri Alimun Azizun
Makaɗaici,
Ƙara min hikkima da
ilmi Mawadaci
Mai hikima buwaye Sarkin ƙagawa.
2. Na yi salati gun Nabiyi HabibinSa,
Da iyalai har da
dukka Sahabunsa,
Sa mana masu dauwama a tafarkinsa,
Tashe mu da su a lahira daf gefensa,
Manzon nan da an ka
aiko shiryarwa.
3. Sai mu yi godiya
ga Allah da daɗawa,
Salati ga nabiyu babu ranar ƙarewa,
Kan bautar Ubangiji ba mu ɗagawa,
Dukka haninsa mui
na’am sai amsawa,
Don baiwarSa
gun mu ta wuce ƙyargawa.
4. Ya ƙage mu kan halitta
kyawawa,
A halittunSa ba
ya ɗan Adam
gun burgewa,
Don Shi ya faɗa da kansa, mu ba mu musawa,
Yai muna ɗaukaka da harshen
sadarwa,
Tarin laffuza da zancen
furtawa.
5. In bayan Ka Rabbu da
mun dabirce,
Duk lamurranmu da
tuni sun lalace,
Ji da ganinmu Rabbu
sai da ka lamunce,
In ba taimakonka da
mun susuce,
Mun rikice mu dambale sai ruɗewa.
6. Kai kai harsuna ka shiryar da mutane,
Da su muka zantuka a ƙauye da birane,
Hikimar Jalla ce muke
rubutunmu na zane,
Ya bambanta harsunan nan ga mutane,
Ga su wuri guda abin na saɓawa.
7. Duk hikimar mutum ga harshe ka saka ta,
Wajen magana da nazzari sai mun sa ta,
Ko da bincike na ilmu dolenmu a sa ta,
Masu fasaha da sha’irai ke mulkinta,
Nan aka gane haziƙi mai burgewa.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.