TAMBAYA (05)❓
Assalam malam DANALLAH ataimaka min da addu’ar
karya sihiri. Please it’s urgent Allah yasaka da alkhair
AMSA
Waalaikumussalam. Warahmatullahi. Wabarakatuhum.
Ya tabbata a cikin Sahihul Bukhari (5819) an
rawaito cewar Labid Bin al'asam Alyahudi yayi amfanida gashin kan Annabi SAW
yayi masa sihiri wanda har Ma'aiki SAW yakanyi kokwanto a cikin gudanar da
al'amuransa na yau da kullum. Hakama Muslim ya fitardashi, hadisi mai lambata
2325
Sai Allah SWT ya nunawa Annabi SAW rijiyar da aka
binne sihirin a cikin mafarkinsa. Akaje aka tararda ruwan rijiyar ya sauya kala
kamar lalle saboda tasiri da dafin sihirin
Silar hakanne Allah SWT ya saukar da
"Mu'awwidathayn" wato Surorin neman kariya daga sharrin mutum da
aljan (Falaqi Surah ta 113 da Nasi Surah ta 114)
Annabi SAW ya warke sannan kuma ya koyarda
sahabbai cewar su dinga karanta wadannan surori domin neman tsari daga sihiri.
Wanda ana son mutum ya dinga karantasu da safe, yammaci da kuma lokacin
kwanciya bacci
Anfi son a karanta kowacce Surah sau uku-uku a
lokacin kwanciya bacci da karin Suratul Ikhlas itama sau 3 sai a tofe ko'ina a
jiki (inda ya sawwaqa)
Idan aka karantawa wanda akayiwa sihirin da
kyakkyawar niyya ko kuma shi da kansa ya karanta to in sha Allahu za a samu
waraka
Wallahu ta'ala a'alam
Subhanakallahumma, wabi hamdika, ash-hadu
anla'ilaha illa anta, astaghfiruka, wa'atubi ilayk
Amsawa:
✍Usman
Danliti Mato, Usmannoor_Assalafy
https://chat.whatsapp.com/DSdbBS8RZVoIKYG5exOuZE
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.