Ticker

6/recent/ticker-posts

Wakar Noma Ta Makada Idi Loga

 Citation: Bungudu, H. U. (2023). Zaɓaɓɓun waƙoƙin mawaƙan baka na noma. Ahmadu Bello University Press Ltd.

Domin samun cikakken littafi, a tuntuɓi:

Dr. Haruna Umar Bungudu
(Sarkin Gobir Na Bunguɗu)
Email: harunaumarbungudu@gmail.com
Phone: 08065429369

Waƙoƙin Noma

Waƙar Noma Ta Makaɗa Idi Loga 

Waƙar Noma Ta Makaɗa Idi Loga

 

Tarihin Makaɗa Idi Loga

An haifi Idirisu kimanin shekaru sittin da biyar (65) da suka wuce, wato wajajern shekarar dubu ɗaya da ɗari tara da hamsin da bakwai (1957) a wani gari da ake kira Dodon sahu  daga baya suka tashi suka koma garin malamai a can ne ya girma daga nan sai suka  koma garin Kwakwara da ke cikin yankin Gangara ta gundumar Sabonbirni a ƙarƙashin ƙaramar hukumar mulkin Sabon Birnin jihar Sakkwato, nisan kilomita uku daga Gangara, kuma har yanzu a nan yake zaune. Garin Kwakwara ya yi iyaka da garin Tulu-Rudu daga Kudu, yayin da kuma garin ya yi iyaka da Satiru daga Gabas.

Idirisu ya gadi kiɗi daga kakansu Amadu Maiwasa har zuwa ga babanshi wanda makaɗin noma ne, Idi Loga ya gadi kiɗin noma daga babansa kafin daga bisani ya faɗaɗa sana’arsa ta kiɗin noma zuwa ga na  Sarakuna da masu hannu da shuni. Idi yana da kimanin waƙoƙi fiye da ɗari biyu da hamsin (250) waɗanda ya yi a ciki da wajen Nijeriya. Ya sami laƙabinsa ne na Loga saboda irin rawarsa wadda yake yi a lokacin waƙarsa. Idi loga yana da matan aure ukku (3) su ne; Sahiya da Sa’a da kuma Talatu, yana  da ‘ya’ya goma sha tara a halin yanzu, tara maza ne, sauran kuma mata ne. mazan kuma sun haɗa da Ibrahim, da Basiru, da Isiya, da  Yakubu, da Muhmmadu Yazid, da Ashiru, sai tagwayensa Hassan da Hussaini suna nan ƙanana.

Yaransa da suke yawon kiɗi da su kusan duk danginsa ne na jini waziri Hamza ƙanensa ne wanda ke bi masa, akwai yayansa wanda yake bi ma uwa ɗaya uba ɗaya mai suna Isihu, sai Sale shi ma yayansa ne, amma ɗan wa da ɗan ƙane suke da shi, akwai kuma wani ƙanensa Sule, da wani ƙanen nasa da ake ce ma Buzu Ɗanƙargi, amma sunansa zananne shi ne Isiya. Sai wani abubakar ɗan Kaura wanda abokin Hamza ne. maroƙinsa wato Maba sunansa Sada, wanda ake kira Ɗanmaliki shi ma mutumen Kwakwara ne. kayan kiɗinsa shi ne kuru wanda ake kiɗin noma da shi. 

Post a Comment

0 Comments