Ticker

6/recent/ticker-posts

Mata A Yau (Gajerun Labarai)

Ƙilu ta Ja Bau - Uku

Kukurukuuuu! Zakaran gidan ɗaya tilo ya yi cara da asubahin fari babu wanda ya motsa. Can ya sake yi iya karfinsa ya ji shiru. Ba da daɗewa ba ya daddage ya kuma tsallara ihu amma a banza. Sai ya koma cikin akurkinsa ya kwanta ya ce "Ni dai na fita wAllahi."

Jim kaɗan Maigidan ya fito daga ɗakinsa ashe ya tashi. Ya ɗauki butarsa ya ji fayau babu ruwa. Har ya juya ya kalli ɗakin da ya fito zai kama faɗa sai ya lura har yanzu gari bai waye ba ya ja bakinsa ya yi shiru. Kar ya manta Baaba tana ɗaki kar ya tashe ta.

Ya je jikin randa ya sa kofi don debo ruwa sai nan ma ya karci ƙasar randar babu ko ɗigo. Ya mike a fusace ya yi tsaki ya wurga kofin cikin randar yana huci. Ya juya zai je ya tashi matarsa je nan sai ya ga mahaifiyarsa ta fito daga ɗakinta ita ma da buta a hannu.

Kafin ta yi magana ya yi sauri ya rusuna ya gaisheta cikin murya tattausa ta amsa masa ba gaba ɗaya ba don ba su yi sallah ba. Ta wuce shi ta shiga banɗakin gidan da kowa ke amfani da shi. Kafin ta fito ya ɗauki guga ya jawo ruwa a rijiya ya zuba a butarsa.

Da babarsa ta fito ya kar6i butarta ya cika mata shi da ruwa cikin girmamawa ta kar6a a zaune kan wata kujera a bakin makwarara ta kama alwala. Shi kuma ya shiga ban ɗakin yana takatsantsan kar ya saki tusa uwar ta ji. Ya yi ɗahara ya fito.

Da ya fito ya ga Baaba ta gama alwala har ta  koma ɗaki shi ma sai y zauna inda ta tashi ya ɗaura tasa alwalar. Yana cikin haka Ladanin masallacinsu ya kama kiran sallah da shaƙaƙƙiyar muryarsa. AlhamdulilLaah ya dai fi dubu da suke ƙudundune a cikin bargonsu.

Bacin ya kammala alwalar ya shiga ɗaki ya lalubo hula ya sa ya ce "Na tafi masallaci. Tashi ki zo zaure ki rufo kofar saboda tsaro" Matarsa ta yi wani juyi ta gyara kwànciya ta ce "Na ji." Amma shi gurnani kawai ya ji kafin ya fita ya ce "Kar fa in dawo ba ki tashi ba."

Wajen ƙarfe 6:30 na safe gari ya gama washewa Maigidan ya dawo zai ƙwanƙwasa kofar ke nan a zo a buɗe masa sai ya samu kofar yadda ya barta wato ba a rufe ba. Nan take ya fusata ya banki kofar cikin gaggawa ya kutsa ta zauren ya shiga gidan.

Nan ma zai soma faɗa a tsakar gida ke nan ya tuna cewa Baabarsa fa na nan. Ya yi sauri ya yiwa fushinsa linzami ya wuce ɗakin tsohuwar ya tsaya baƙin kofa ya yi sallama "Assalam alaikum Baaba in shigo?" cikin ladabi da sassauta murya. Ta ce masa "Wa alaik assalam e shigo."

Ya shiga a durƙushe ya zube a gabanta kansa a duƙe "Baaba ina kwana?" Ba ta amsa masa kai tsaye ba sai da ta ida addu'o'inta ta shafa ta ajiye carbinta sannan ta ce da shi "Nabaaba lafiya lau." ya bi ta da "Ina gajiya? Ya jiki jikinki naki?" Ta ce da shi "AlhamdulilLaahi."

Suka dai gaisa har suka shiga hira yana me take so ya sayo mata na magunguna tunda ta ce bayanta na yi mata ciwo. Ko dai ya kaita asibiti ne ko ya kira mata Dakta Halliru ɗan wansa da ya karanci aikin likita yana aiki a Asibitin Aminu Kano? Ta ce da shi a'a ya bar shi.

Bacin ya gama gaida babarsa ya tashi ya fito daga wajenta tana shi masa albarka sai ya shiga ɗakinsa nan ma da sallamarsa "Assalam alaikum." Ya ji kamar an amsa masa amma fa a cikiciki. Ya nemi waje ya zauna ya ajiye hularsa a gefensa matarsa na kwance akan gado.

Bayanta na juye ko ta juyo ta kalle shi. Ya ce da ita "Wai ba ki tashi kin yi sallah ba ne? Ba na ce kar in dawo in same ki a kwance ba?" Ya saurari ya ji amsa ba ta ce da shi ufan ba. Sai ya ɗora zance a kai "Sannan na ce ki bi ni ki rufo mana kofar gidan nan, nan ma haka na dawo na samu ba ki rufo ta ba. Ko me yasa?"

Ta ce "Na rufo ta mana sake komawa na yi na buɗe ta da na gama sàllah." Ya yi shiru bayan ta gama magana. Bai san sanda ya ɗaga muryarsa cikin bacin rai ya ce "Kin ga kar ki kawo mun rainin wayo kin ji ko wannan kofar ba ki rufe ta ba malama!" Ta ce "Na rufo ta."

"To shike nan kin rufo. Kin ce kin yi sallah ko? Wai me yasa na tashi butata babu ruwa ko na ɗahara ba ma na alwala ba? Ban ce ki daina bar mun ita haka ba?" Su ka yi shiru na ‘yan daƙiƙoƙi ta buɗa baki za ta yi magana ya ce "Ga shi ko gaishe ni ma ba ki yi ba!"

Ta yi masa wani irin kallon reni kai ka ce wani ne wanda bai isheta kallon biyu ahu ba. "Yau wajen kwana biyar ke nan kullum na shigo ni ne zan ce miki ina kwana? Wato kin fi ƙarfin ki fara gaishe ni ke nan ko me kike nufi?" "To menene don ka fara gaishe ni? Ni ba matarka ba ce?" Ta kada baki ta tambaye shi.

Ya ɗauke wuta na wani ɗan lokaci don tsananin mamaki! "Me kika ce?! Sake faɗa in ji ki da kyau tukunna! Ni kike cewa menene don na fara gaishe ki? Wato don ƙarfin hali har tambayata kike ke ba matata ba ce? Ikon Allaah." Ya faɗa cikin kogin tunani ya yi shiru.

Shin anya kin san ko ni waye kuwa? Kin San matsayinsu a rayuwarki kuwa? Ni fa ni ne mijinki wanda Allaah SWT Ya yi ki don ni! Ashe wata sa6uwar fitsara kika tsinto ban sani ba? Wato ni mijinki nine zan dinga gaishe ki duk wayewar garin Allaah? Yau zan ga rashin kunya! Kai!" ya tashi tsaye yana kallonta.

"Ai Sunnah ce! Sunnar Annabi ce miji ya fara gaida matarsa kuma ya gaishe ta safe da rana da yamma. Kai ka fi Annabi ne?" Ya ji wani irin surrr daga wuyansa ya yi ƙasa. Can ya buɗe bakinsa ya ce da ita "Da kyau. Lallai ban fi Annabi SAWS. Ke ko ubana bai kai darajar takalminsa ba wAllahi."

"Kuma kin yi gaskiya kam Manzo SAWS shi ne yake bibiyar ɗakunan matansa tara (9) kowacce ya je su gaisa ya tambayi lafiyarsu damuwarsu buƙatunsu da dai sauransu. Ni kuwa don Allaah in tambaye ki mana; Matana nawa ne?" Ya jira ta ba shi amsa amma ya ji shiru. "Ba ki da amsa ne?  Na ce ku nawa ne?!"

Nan ma said ya sake ɗora mata amsa ya ce "To alhamdulilLaah. Tunda abinda kike so in dinga yi ke nan wato shiga ɗakunan matana ina gaishe su to in sha Allahu abindaa zai fara faruwa ke nan kwanakwanan nan. Zan tabbatar miki da kasancewar hakan! Buri ki zai cika taf"

Ai kan ka ce kwabo matar nan ta dirgo daga kan gado ta durƙusa a gaban mijin ta kama ba shi haƙuri tana ta tuba tana neman gafararsa. Hawaye shar6e-shar6e tana ce da shi "Malam don Allaah don Annabi na tuba! wAllaahi ba abinda nake nufi ba ke nan." Ya yi gum yana kallonta da wani murmushin ƙeta a fuskarsa.

Ta ba shi haƙurin duniyar nan amma ina! Dama ya daɗe yana son ya ƙara aure amma saboda zaman lafiya, so da ƙauna da suke ga iyayenta mutanen kirki ya rasa ta inda zai 6ullo mata sai ga shi bagatatan ya tsinci dami a kala. Ai kuwa bai 6ata lokaci ba yanzu matansa hudu (4)

Da yake yana Allaah Ya yi masa arziƙi Dan kasuwa ne Yana samu akai akai nan da Nan ya same aka gina masa mai bangare hudu ya auri wasu Mata uku a gufi a gufi. Kuma kowacce ya kama zuwa gidanta don ya dinga gaisheta. Ma sha Allaah.

Daga baya ma aka ce ita matarsa ta fari ta yi yaji akan ko mene ne ma... Yauwa wai in ya je bangarenta ba ya tsayawa ya daɗe yana hira kamar yadda ta samu labarin yana yi a wajen sauran mata. Ya ji tsoron Allaah ya dinga kwatanta aldalci fa. Yanzu dai ko ta dawo shi ne ba a sani ba. 

www.amsoshi.com

Daga Taskar

Malam Muhammad Tajajjini Tijjani
Imel: mmtijjani@gmail.com
Lambar Waya: +234 806 706 2960

A Kiyayi Haƙƙin Mallaka

Post a Comment

0 Comments