𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaika malam don Allah ya halasta inyi Kitso da wiwi? Ma'ana in sa shi a cikin man kitso.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salamu. Ya
tabbata a hadisi cewa Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce: Duk abu
mai sa maye giya ce, duk abu mai sa maye haramun ne. Kamar yadda Albukhariy ya
ruwaito a hadisi mai lamba ta (2003).
Wiwi kuma yana daga cikin
abubuwan da ake hukunta su a matsayin kayan maye, don haka ita ma giya ce,
hukuncinsu ɗaya dai-dai-wa-daida. Sannan Allah
Ta'ala a cikin Alƙur'ani
ya bayyana giya a matsayin najasa ce a aya ta (90) da ke suratul Ma'ida:
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا إِنَّمَا الْخَمْرُ وَالْمَيْسِرُ وَالْأَنصَابُ وَالْأَزْلَامُ رِجْسٌ مِّنْ عَمَلِ الشَّيْطَانِ فَاجْتَنِبُوهُ لَعَلَّكُمْ تُفْلِحُونَ
Ya ku waɗanda
suka yi ĩmãni! Abin sani kawai, giya da cãca da refu da kiban ƙuri'a, ƙazanta
ne daga aikin shaiɗan, sai ku nĩsance shi, wa
la'alla ku ci nasara.
Malamai sun yi saɓani
a game da najasar da ake nufi a wannan aya, wasu malaman suna ganin siffanta
giya da Allah ya yi da najasar da ke wannan aya tana nufin najasa ce ta ma'ana
ba ta haƙiƙa
ba, don haka suke ganin ko da giya ta taɓa
jikin mutum ba dole ne sai ya wanke ba, saboda su a fahimtarsu ba najasa ce da
idan ta taɓa jikin mutum sai ya wanke ba.
Jumhur ɗin
malamai kuma suna da fahimtar duk wanda giya ta taɓa
jikinsa dole ne sai ya wanke hannunsa domin najasa ce ta taɓa
jikinsa, saboda a fahimtarsu ita giya najasa ce ta haƙiƙa ba
ta ma'ana ba. Kuma wannan fahimtar ita ce ke da rinjaye.
A bisa wannan dalili, sai ya
zama bai halasta a sanya wiwi a kai a yi kitso da shi ba, saboda wiwi giya ce,
giya kuma najasa ce, kuma ba ya halasta a shafa najasa da gangan a jiki.
Don ƙarin bayani a duba Fataawa Nurun Alad
Darb (7/2), na Ibn Uthaimeen.
Allah Ta'ala ne mafi sanin
daidai.
Jamilu Ibrahim, Zaria.
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.