Dattijo Alhaji Nuhu ke nan wanda mahaifansa daga Kano suka tafi wannan Kasar ta Burkina Faso fiye da shekaru 200 da suka wuce, a Ouagadougou aka haife shi. Attajiri ne daga harkar noman kayan marmari na lambu(Orchard) wanda ta hanyar ne ya mallaki ƙaddarori masu yawan gaske a ƙasar musamman gidaje da filaye. Ya baiwa al'ummar Hausawa da sauran Kabilu Musulmai da ba 'yan ƙasar ba wani makeken fili a Zango dake Birnin Ouagadougou kyauta suka gina Masallacin Juma'a. A lokacin da Marigayi Thomas Sankara ya yi juyin mulkin da ya zamo sanadiyar zaman shi Shugaban Ƙasar, ya soma gyara fasalin tsarin Birnin Ouagadougou sai wannan Masallacin ya faɗo cikin wuraren da za a rushe. Al'ummar da suka mallaki wannan Masallacin suka yi mashi ke ƙorafi akai sai ya naɗa kwamitin da zai gano silar samuwar wannan wuri idan ba ta haramtattar dukiya ne aka samar dashi ba ya yi masu alƙawalin ba zai rushe shi ba, za a zaud'a daga gefen shi. Sanin silar dukiyar Alhaji Nuhu ne sanadiyar tsirar Masallacin(2017 ne na ziyarci ƙasar)
Lambar Waya: 08149388452, 08027484815
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.